← Book details Tushen Mu Daya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 8 OF 78

Sashe 8

Tushen Mu Daya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ranar gaba daya akwance na wuni kamar yadda hajjo tayi alkawari bata bani abinci ba kuma koda ahmad ya kira nadai fada masa banjin dadine bance masa ta hanani ba saboda duk son da miji ke miki kome mahaifiyar sa tayi miki bafa zaiji dadiba in kina yawan fada mishi aibunta kuma son da yake miki bai kai wanda yake mata ba saboda haka babu amfanin duk abin da uwar miji ta miki danta na dawowa ki kwashe ki fada masa koda yana goyon bayanki mahaifiya tafi karfin wasa wataran zai fara ganin bakinki

************"***"**"**"""

Bayan kwana biyar wanda tun washe garin da akai abin dana samu sauki na koma bakin aiki sai daifa inashan bakaken maganganu sai na ke toshe kunnuwana inyi kamar badani take ba

Misalin karfe Shadaya na dare lokacin dakina cike yake da yan kallo kama daga kan kannan sa zuwa yaran gida da abokanan su da suke gayyatowa duk sun fara yagamin ledar tsakar daki

Can naji kauri kauri natashi cikin barci saboda yau wani irin barci nakeji da wuri naso kwantawa saiga Nepa dan haka saina sa hijabina har kasa na kudundune nufina insun gama natashi na rufe kofar kamar yadda muka saba

Na tashi a firgice nace ina nake jin kauri sai lokacin shamsu ke cewa

Nima ina dan jin kauri kauri fa tun dazu cikin rashin bawa maganar muhimmanci

Na tashi da sauri na isa wajen socket din ikon allah sainaga Ashe dutsen guga ne aka jona ajiki aka dire shi a kan ledar tsakar dakin da sauri na zare shi yacinye gurin yayi jajawur

Nace waye ya jona min dutsen guga aka rasa wanda yayi ni mamakin abin da,ya kawo dutsen wajen ma nake dan acan bayan Tibi na aje amma aka samu yaron da ya janyo shi

Aka rasa wanda yayi kowa yace bashi bane haushin hakan yasa na kashe kallon nace to kowa ya tafi yaje ya kwanta babu wanda zaimin wani kallo tunda banna kuke min

Suka tashi daya bayan daya suna fita shamsu cikin jin haushi ya kalleni yayi tsaki ya fita

Na dauki buta nayi bandaki dan inyi fitsari

Ina dawowa kiran ahmad na shigowa wayata garin saurin indauki wayar ya hana in tuna da rufe kofa saboda yau tun safe rabona da inji shi

Inda muka shiga fira mundau dogon lokaci bayan mungama sam na manta ban rufe kofa ba na hau shirin barci nayi addua na kwanta

Can cikin barci naji kamar numfashin mutum a setin fuskata ana jan hijabina na tashi a firgice zan fasa ihu akayi saurin sa hannu aka
Rufe min baki.......

*_😍MAMAN DAN ALBARKACE_😍*✍️

*Wannan littafin na kudine idan kinason cigaba da karantawa zaki same shi akan farashin normal group 300 VIP 400 masu so ta private 1000 ki turo kudin ta wannan account number 2375144550 ki turo evidence ta wannan number 09138320449 katin MTN ta wannan number 09138320449*

*Idan kuma littafin mu guda biyu kikeso TUSHEN MU DAYA da FANSAH 2022 Zaki turo normal group 500 VIP 800 ta private 1000*

'm selling data to all Nigerian network Thank you for contacting Sdeendtm!
BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE
I'm
selling MTN data with this cheap price
MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500
Dial *131*4# or *460*260# to check Data balance Validity 1 month
Airtel,9mobile and Glo also available.
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills*
Whatsapp OR
Call *08066268951*
09/11/2022, 2:16 pm - Maman Dan Albarka Ce: https://chat.whatsapp.com/KqWJTlOAIPm8AY24jxV9YB

*🪴TUSHEN MU DAYA🪴*

*_😍MAMAN DAN ALBARKA CE_*😍

*_Littafin tushen mu daya labarine daya danganci Wata zuria wadda babu abin daya yiwa zuriar nan lullubi face Cin amana zalunci rashin tausayi rashin tsoron allah sannan ga sassanyar soyayya labarin Aminatu da surukarta labarine da zaka zubda mata hawaye ka kannen miji suma sun sako ta gaba shin dama haka yakamata surukai su zauna da matan ya,yansu? Duk sai kun tsunduma cikin wannan labari mai suna TUSHEN MU DAYA_*

```Bismillahirranirrahim```

*Free Page6️⃣*

*Masu son a tallata musu hajarsu ko link na group dinsu suyi magana ta wannan number 09138320449*

Kokawa muka fara da wanda ya rufemin bakin Duk kokarina in lalubi Fitila inkunna inga wane

yaki bari kokarinshi kawai shine ya rabani da sutura ta

Dana ga ba sarki sai allah sai nashiga kokawar kwatar kaina

Shikuma sai kara tusa kansa yake yana kokarin kai bakinsa fuskata

Na daddage iya karfina na kartsamai wani azababben cizo wanda zafin cizon yasa yayi saurin cire hannun sa guda da yasa ya rufe min baki

Anan nasamu nasarar kurma uban ihu har sau uku wanda nasan duk nisan dakin hajjo zata ji

Aikwa yana ganin haka yayi sauri gurin kokarin guduwa na rike shi

burina insan wane da karfin halin nan har haka da ya shigomin daki so nake koda mutane sun zo suganshi

Amma da yake karfin ba daya ba tuni ya fincike ya gudu

Na tashi da sauri na rarumi hijabina nasa dan duk ya barkamin doguwar rigar barcin dana kwanta da ita

Nayi hanyar bakin kofa zuciyata ma bugawa cikin tsoron ko bai tafi ba ina mamakin rashin zuwan kowa bayan baza a
rasa wanda yaji ihuna ba wato koma mene da yasamu nasarar cimma burin shi haka zai keta min haddi babu mai ceto na

Nayi saurin sawa dakin mukulli na koma nakwanta cikin zulumi da fargaba da kuma tsoro

Ina mamakin abin har mutumcina ake hari nidai nasan kofar gidannan ana rufeta sai dai in ta bayan dakina wajen karamar katangar nan ya biyo ikon allah haka naketa sake sake har barci yayi gaba dani cikeda da mafarkai marasa dadi

*****"******************

A kwana atashi aka ce ba wuya a wajen allah yau satin ahmad biyu kenan da tafiya

Ina zaune ina tsintar shinkafa wadda tun bayan tafiyar ahmad sau daya hajjo tayi tuwo shima acewar ta babane yace shinkafa da miya ta isheshi sukuma yaranta sunfi son shinkafa kullum shiyasa takeyi

Sallamar fadime naji kawar hajjo .
.
Salamu alaikum .

Gabanane naji ya wani yanke ya fadi bansan meyasa ba inhar zanganta sainaji faduwar gaba bata kwana uku batazo gurin hajjo ba kuma duk zuwan da zatai tare suke fita allah yasan ina suke zuwa

Nadago na amsa suka shiga gaisawa da maman Aisha dake kofar dakin ta

Nayi sauri gurin gaisheta

Ina wuni maman zainab daya ke tana da ya, zainab haka wasu ke cemata

Ta wani kalleni a kaikaice madadin ta amsa sai ta jefo min tambaya

Hajjo na nan?

Nace eh tana daki

Ta wuceni ta shige

Nacigaba da aikina

Maman Aisha da ke kofar dakinta tayi saurin ta sowa ta karaso kusa dani

Cikin rada tashiga magana aminatu kinsan wani abu ?

ganin ta fara magana kuma nasan bawani abu bane sai tsabar gulmarta saina yi saurin tashi dama farantin karshe ne a hannuna nayi hanyar wajen girki dan nasan bazata biyoni ba sai anwuce dakin hajjo za atarda wajen

Data ga haka bata samu damar yimin gulmar ba sai ta koma tacigaba da aikinta amma lokaci lokaci tana dagowa kamar zatayi magana sai indauke kaina

Harna kammala girki su hajjo na daki

Dana gama nayi sallama nace hajjo nagama

Tace to ki hadamin kwanikan ganinan fitowa

Nace to

Can ta fito ta gama rabon ta ta koma ana dan jimawa sai gata ta fito da mayafi ita da fadime

Toni saina dawo haka kawai na bisu da kallo fita babu wani tsari da girman hajjo daga zuwan kawa sai binta unguwa ko ina suke zuwa oho na watsar da tunanin

Na tashi har zanyi hanyar lunguna saina dawo nayi wajen maman Aisha

Nace maman Aisha dan allah kinsan inda ake kitso da zan samu azo amin ?

Tayi caraf tace min ainima inayi bakisan na iya ba kizo inmiki me kyau irin naku na amare

hala Me gidan zai dawone ? Zakiyi kitso aikwa zanmiki kanana

Tambaya daya namata ta baibayeni da tata tambayar

Saina ce tom bari ayi la asar saina zo kikamamin

A a bari inkinyi sallar ni zanzo lungunki inmiki

Nadai ce mata to ne kawai bisa dole bekamata in gwasaleta ba sannan ma bayan haka kannan ya isheni inda na godewa allah gashina bashida wani karfi irin gashin fulanin nanne mara cika cukus yanada yawa gwargwado sai tsayi amma ni tazar danake kullum ta isheni gwara amin

Inba dan dolen ba bazan ba maman Aisha kaina ba fisabilillah danni allah ya gani kazantar ta na bani haushi
************************
Haka kuwa akayi bayan la,asar sai gata da kibiyar ta da matajinta harda man alayyadinta

Nace a a inada man kitso bari na dauko kibiyar ma dana shiga daki saina dauko tawa da matajina haka kawai kizo da mataji inyarda kisamin akai

Na dauko tabarma da kujera na shimfida tabarmar na aje mata kujerar na shiga taje kaina dan banason wani ya tajemin kai ciwo yake min

Ina cikin tazar kan naji tafara magana

Kai amarya kina da gashi gaskiya ji gashinki baki ta taso tasa hannu tana tabawa kai ga laushi me kike sama sa gaskiya dama nice....

Babu tubarkallah babu komai take tankani azuciyata nace tubarkallah masha allah

Nagama muka shiga kitso

Tana min kitso tafara bani labari

Amarya kinsan fadime ko?

Nace maman zainab nasanta mana

Tace ba irin sanin nan ba nake nufi

Ai abin dayasa kikaga in kika gaidata bata amsawa ba Diyarta fa hajjo taso ya aura hauwa,u to shikuma ahmad baya son yarinyar tunda bata tashi cewa ya nemi Hauwar ba fa

Saida Mijinta ya yi sha awar hada auran ku sannan ta tada fitinar wai ta riga data zaba mai mata ita bata yarda ya auro ki ba Tawa aminiyarta alkawarin zasu hada auran zumunci

Amma mijinta yadai nuna mata fin karfi ne a lokacin da kuma hadin kan kaninshi na can kano tunda shi yanada zafi dole akai amma ansha daru fa

Kuma hauwar fa tana son mijinki sosai shiyasa uwarta ta rikice da akace ahmad zai yi aure harfa sabani suka samu da ita fadimen daga bayane suka shirya

Nidai nayi shiru inajinta
Bandai cemata komai ba amma hakika biri yayi kama da mutum irin kiyayyar da hajjo ke nunamin ba banza ba bayanna nan in fadime tazo irin kallon datake aunamin na fadarmin da gaba saidai nayita addu a a zuciyata innaganta intazo ina takura
Chapter 8 · 0% Book details