← Book details Tushen Mu Daya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 23 OF 78

Sashe 23

Tushen Mu Daya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Tace to aminatu wannan ahmad ne dan gidan babanmu dake Niger state nasan baba ya taba miki maganarshi to gashinan lokacin zuwanshi yayi sauran ya rage naku kudai daita kanku ni zan wuce ahmad ga aminatun da ake fada maka nan allah tabbatar da alkhairi

Ta kare tana mai tashi ta fita

Bayan fitarta munfi minti biyu sai dai ina jin ajikina kallona yake sai can dayaga bani da alamar

Tukun yace fatan mun sameku lafiya?

Kaina asunkuye nace lafiya lau

Yashiga yimin yan tambayoyi duk idonshi akaina

Nikuma nakasa ko dago idanuna na kalleshi ina dai amsamai

Yace duk nasan su baba sun miki bayanina kamar yadda sukamin kafin tahowata

Alhmadulillah nidai kinmin kuma naji araina cewa zan iya aurenki

Bawai saboda hadin da aka mana ba ko daya a rayuwata inason mace mai tarbiyayya da nutsuwa inda duba daya na miki na gane lallai nasamu irin matar danakeso

Saidai bansaniba kona miki kutse akwai wani aranki inhar akwai wanda kikeso kifito kifadamin dan bazanso in rabaki da wanda kikeso ba ni nawa mai saukine zan iya danne nawa son danake miki inhar hakan zaisaki farin ciki amma zanso mucikawa su baba burinsu kodan musasu farin ciki

Kamar yadda kikasani ina niger state ne garin lapai da zama sannan ina aiki a _Company Fine coat Paint_ muna tafiye tafiye zuwa gari gari a takaice dai ni dan gwangila ne in ankirani ina zuwa kuma nima in nasamu kwangilar nakan kai mutane
Nanemi aikin gwamnati allah baisa nasamu ba duk da takarduna sunyi kyau amma har yanzu ina nema bancire raiba

Ya ya kike gani um nayi miki ko kuma ya

Nidai kunya kamar na nutse agurin nasa hijabina na rufe fuskata

Ya kalleni yace bude fuskar ki dago ki kalleni kigani ko bana cikin tsarinki kona miki tsufa duk kifada dago mana

Wayyo allah na wannan mutumin baisan yadda yake bani kunyaba wlh

Yayi dariya yace cab kunyata ce har haka gwara ki dago ki morewa kallona tun wuri karkice kinyi zaben tumun dare

Nidai nakasa dagowa araina ina tunanin lallai wannan zama dashi akwai aiki ashe yana magana haka

Can yace ai gashi ni inata more kallonki yarinya ni kinga nayi dace da yar black beauty na ya karasa cikin raha

Da sauri na karasa rufe fuskata ina murmushi

Yace kiyi magana mana

Na dan dago sainaga gaba daya ya tsareni da idanunshi
Na ce ni ba abin da zance allah ya tabbatar mana da alkhairin sa

Ya kalleni yace cab aibaki isa ba amsa zaki bani kina sona?
.
Ya karasa maganar yana mai dan sakkowa daga kan katifar zuwa gefen tabarmar danake kai

Saina karajina a takure

Na yi murmushi kawai na sunkuyar da kaina

Yakara tausasa murya yace kinada waya?

Na girgiza kai dan ni bantaba rike waya ba baba baibarnibama dan yace sai dai in mijin da zai aureni ya bukaci hakan amma haka kawai bazan rike waya ba

Nima kuma sai hakan bai dameniba duk da duk yan ajinmu suna da ita wasu babba wasu keypad amma bata dadani da kasaba har tsokanata suke wai ban shigo gariba har yanzu bani da waya

Nakanyi murmushi kawai ina kallonsu musamman wadanda zasu makaratar har acikin class suna daga wayar samari wasu kuma su kunna kallo da dai sauran shirmen da baikamata ba

Yace to inna siyomiki zaki amsa ?

Nace baba bai barina rike waya saidai in katambayeshi

Yace to shikenan zan tambayashe dan kinga inna tafi inason nadinga jin muryarki kuma dole sai inkinada waya hakan zata faru

Nace to shikenan

Nan yashiga jana da hira nakan amsa jefi jefi dan na fahimci shi mutum ne da babu ruwanshi da boye boye yanada saukin kai ga raha haka dai har wajen karfe tara tukun lokacin su aunty nafeesa suka fito da shirin tafiya

Sai lokacin na tuna ko abincinma banzuba mishiba nace bakaci abinciba gashi har aunty nafeesa ta fito

Yace ni anan zan kwana gidan sabon babana tare da yusuf sune dai zasu wuce yanzu

Sainace to nima zani in kwanta ina da jarabawa gobe

Yace allah yabada sa a to saida safen na amsa da allah ya kaimu ina mai fita

Mukayi sallama da aunty nafeesa wadda ita kadai zata wuce su su salim sai sunci abinci tukun zasu tafi tunda su bamu da nisa

Harta juya ta kirani
Na karasa
Tace yaya kukai kun dai dai daita baki masa shirmen nakiba

Na kalleta cikin jin haushi waini zata cewa mashirmanciya bayan ga kannenta can suna shirman sunki fito da mijinma kullum sai tara samari suka iya duk sun gansame

Nace mundai daita
.ta gallamin harara babu kunya zaki wani ce kun dai dai ta adaibi a hankali karki nuna masa rawar kai

Nidai na wuce ta ina cewa ta gaida yaran cikin jin haushinta

***********************

Satin ahmad daya a gidanmu inda zuwa lokacin nikaina zan iya cewa na kamu da soyayyarsa duk da bantaba yinta ba wata irin shakuwace tashiga tsakaninmu mai wahalar fasaltawa in gari ya waye yakan bi su yusuf kasuwa wani lokacin kuma yakan je gidan baba abdullahi yadau su salim su zagaya dashi gari

Sai da yamma muke fira adakin yaya yusuf inda yana kan katifa ni ina kasa kan tabarma

Yawa baba maganar wayata inda baba ya amince ya siyomin yabani

Inda ana ya gobe zai tafi salim ya rakashi suka siyomin wayata yar madaidaiciya tecno ce inda yamin alkawarin indai yakara zuwa zai canzamin da babba

Washe gari ya wuce cikin kewa nikaina nasan zanyi kewarshi saidai inna tuna zamuna waya sainaji dan sanyi

***********************"*

Watanmu shida da ahmad inda cikin watannin nan ya maida kano tamkar gida baya wata sai yazo wani lokacinma yakance min daga wajen aikine ya karaso kafin ya koma gida dan kar hajjo tace yacika zirga zirga

Lokacin watanmu biyar da yin Candy inda su baba suka dauko maganar aurenmu duk da babu jituwa tsakaninsa da baba abdullahi har lokacin amma da maganar auren tazo dole baba abdullahin shi ya nemi babanmu saboda baba musa abdullahin ya wakilta akan komai

An tsaida ranar aurenmu watanni uku masu zuwa

*_😍MAMAN DAN ALBARKACE😍_*✍️

*Wannan littafin na kudine idan kinason cigaba da karantawa zaki same shi akan farashin normal group 300 VIP 400 masu so ta private 1000 ki turo kudi ta wannan account number 2375144550Lawali ahmad zenith Bank ki turo evidence ta wannan number 09138320449 katin MTN ta wannan number 09138320449*

*Idan kuma littafin mu guda biyu kikeso TUSHEN MU DAYA da FANSAH 2022 Zaki turo normal group 500 VIP 800 ta private 1000*

'm selling data to all Nigerian network Thank you for contacting Sdeendtm!
BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE
I'm
selling MTN data with this cheap price
MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500
Dial *131*4# or *460*260# to check Data balance Validity 1 month
Airtel,9mobile and Glo also available.
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills*
Whatsapp OR
Call *08066268951*
09/11/2022, 2:16 pm - Maman Dan Albarka Ce: *🪴TUSHEN MU DAYA🪴*

*_😍MAMAN DAN ALBARKACE 😍_*

*_Littafin tushen mu daya labarine daya danganci Wata zuria wadda babu abin daya yiwa zuriar nan lullubi face Cin amana zalunci rashin tausayi rashin tsoron allah sannan ga sassanyar soyayya labarin Aminatu da surukarta labarine da zaka zubda mata hawaye sannan ga kannen miji suma sun sako ta gaba shin dama haka yakamata surukai su zauna da matan ya,yansu? Duk sai kun tsunduma cikin wannan labari mai suna TUSHEN MU DAYA_*

*Masu son atallata musu hajarsu ko link din goup dinsu zasu yi magana ta wannan number 9138320449*

```Bismillahirrahamanirrahim```

*LAST FREE PAGE*

Kwanaki sun mika kamar wasa sai gashi bikin mu ya rage wata daya inda lokacinne kuma ahmad ya zo akan maganar shirye shiryen bikin

Dan yace nan gaba bazai samu lokacin zuwan ba dalilin wani aiki da yasako shi gaba

Inda azuwannan ne ya sallameni da duk abin da yasan zan bukata duk da ya tambayeni mene ne al,adarmu ta yammata me dame zanyi nasanar masa walima kawai aka shiryamin a islamiyya inda ya bani kudade isassu sannan ya bani wasu daban ko zan bukaci wani abun shi bazai kara zuwaba sai daurin aure

Anan yake fadamin ya tambayi aunty nafesa al,adar mu tace shi zai hada lefe wanda ya fadamin acan ma haka suke ashe al,adarmu daya yace yabata kudin komai da komai zata zo ta tambayeni size dina na takalmi da sauransu yasan ba fadamai zanyi ba

Kwanan sa uku ya juya a gaggauce

Inda kamar yadda yace washe gari saiga shi aunty nafeesa tazo gidanmu inda ta tambayeni na fada mata

***********************

Bikin ya rage sati uku naje gidan inna muna zaune naga ta kureni da ido nace yayane inna wannan kallonfa

Tace ba dole in kallekiba naga bakimin kama da amaren ba sam

Nace kamar ya?

Tace shin anfaramin gyara kuwa? Dan naganki yadda nasaba ganinki babu wani dan canji

Anan nake tambayarta wanne irin gyara danni dai ban ma fahimceta ba

Ta kalleni ta girgiza kai ta ce ita matar babannaki bata fara miki dan gyare gyaren nan na amare ba ko kuwa ita,nafeesar tunda tasan komai na zamani

Sai lokacin fahimceta gyaran jikin amare take nufi sai kunya ta kamani

Tace ba tambayarki nake ba

Nace a a inna bata min komai ba

Tace cab da haka za a mika ki har can uwa duniya gayanki babu wani dan gyara haba basu kyautaba sam ita dai wannan rukayyar nakula bata da damuwa akan sha aninku sam amma ai da na kowa ne ina laifin koda bazata kashe kudinta ba inta tuntubeni ai zanbada amiki

Amma yanzuma lokaci bai kureba zanwa mahaifinki magana kidawo nan mu da kika zama dolenmu mayi miki zanwa gwagwgonki binta magana tunda ita aikinta kenan inta kama gidanta zaki koma ko kuma zata na zuwa nan dinne tana miki shikenan

Amma mace ai yar gyara ce ina za ai aure haka

Nan dai tashiga nan ta cigaba da banbaminta wanda ni awajena banga abin wani daga hankaliba har zuwa yamma na mata sallama na tafi

Bayankwana biyu tasa aka kiramata babanmu
Tamaj magana na koma gidanta inda gwagwgwo bintar ce tace inzauna gidan innar zaifi saboda ita gidanta hayaniyar mutane tayi yawa ta dinga zuwan ita
Chapter 23 · 0% Book details