← Book details Tushen Mu Daya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 62 OF 78

Sashe 62

Tushen Mu Daya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Allah hajjo na yarda dan baki ganta bane ni sai lokacin ma da tace tana da aljanun na yi tunani allah hajjo idanunta kwala kwala ne fa abin tsoro gata wata yar gajera kamar a kifeta da kwaryar ga k`afa a gwame ni bnga abinda yaya yagani jikinta ba wallahi duk yammatan garinnan yarasa wazaiso sai ita fisabilillah wallahi yafita kyau ko zai girmeta k`adanne dan wannan uwar mata ce

Dan ubanki nace tashi kibani waje ta fada tana mai kai mata dundun a baya tashi tayi tana diddira k`afa tayi uwar d`aka

************************

Nayi mamakin uban barcin dana sha nida na kwanta tun k`arfe goman safe na kalli agogon dak`in yanzu har k`arfe biyu tayi duk nauyin barcina ana kiran sallah nake farkawa amma yau wanne irin barci nayi haka na kai kallona inda na kwantar da kalim ya farka abunshi yana gefe yana wasanshi daya ke yarone shi mara kwaramniya da barna har yasaba inbarshi d`aki shi kad`ai walid ma tashi na shi ya farkar dashi

Yunk`urin tashi nayi naji jikina kamar anmin shegen duka ko,ina ciwo yake

Yunk`urawa nayi na tashi zuro kafafuna na sauko daga gadon na kalli kalim nace kalim kana ji yunwa ko daya ke yana jin abin da nake cewa d`aga min kai yayi nikaina nasan yana jin yunwar tunda bansa ba kaiwa haka banyi abinciba sannan gashi tun indomen safe dana dafa masa bai k`ara cin komai ba ma tashi na bud`e flarsk d`in shayi nan na juye mai sauran na zuba mai madara da milo na bashi sauran birdin da babanshi ya ci ya rage danni sam shayi bai dameni ba nafi ganewa dumamen abinci

Aikwa nan danan ya shiga ci cikin nutsuwa

Na d`auki buta nafita na d`auro alwala nazo zan tada sallah haka kawai nake jin zuciyata cikn k`unci

*_MAMAN DAN ALBARKA CE😍✍️_*
09/11/2022, 2:23 pm - Maman Dan Albarka Ce: *_WANNAN LITTAFIN NA KUDINE KI SIYA KIKARANTA CIKIN AMINCI AKAN FARASHI MAI SAUKI 300 KACAL TA WANNAN ACCOUNT NUMBER 2375144550 LAWALI AHMAD ZENITH BANK KITURO EVIDENCE TA WANNAN NUMBER 09138320449 INKUMA KATIN MTN NE SHIMA TA WANNAN NUMBER 09138320449_*

*_INKUMA DUKA LITTATTAFAN BIYU KIKE SO FANSAH 2022 DA KUMA TUSHEN MU DAYA ZAKI TURO 500_*

*🪴TUSHEN MU DAYA🪴*

_*😍MAMAN DAN ALBARKA CE*_

_*PAID PAGE 36*_

Da k`yar na daure nayi sallar ina jin wani `bacin rai na taso min
Wuni nayi ranar ina cikin k`unci koda ahmad ya dawo haka na tsinci kaina da tsanar shi kwata kwata sai nadinga jin haushin sa ko magana banason inji yamin nafi ganewa inzauna ni ni kad`ai in kad`aita kullum maganata ni dai gida zani ya d`aukoni ya kawoni ya hanani zuwa ganin iyayena

Ahaka rayuwar taci gaba da tafiya shi kanshi ahmad yana mamakin yadda aminatu ta koma mafad`aciya ko magana yyi saita taso mai dai dai da kalim wannan abu kad`an zaiyi saita doke shi sam ta canza halayenta yana mata uzuri saboda bata taba irin rashin kunyar ba sai ya d`auka hanata zuwa gidan dayayi ne ya kawo haka tuni ya fara mata shirin zuwa kano amma yace sai yaronshi yad`anyi k`wari tukun

`Ban garen hajjo kam ta zuba ido tana jiran taji wata matsala ta taso tsakanin aminatu da ahmad amma abin mamaki shiru ta kasa kunnen ta zuba idon shiru kuma ta tabbatar aminatun taci abincin
Koda ta koma wajen boka ya tabbatar mata maganin yana kan aiki ta kwantar da hankalinta ta basu lokaci tukun abinda yasa bata ga sunkai ga fitowa filiba sunyi dambe ba ko anji kansu ba aminatun bata wasa da addu,a shiyasa amma duk da haka ya tabbatar basa zaman lafiya sam

Nikaina ina mamakin kaina yadda nazama mafad`aciyar gaske abu kad`an saina hau fushi musamman in ahmad na kusa sai yazama na ni kaina na tsangwami kaina nafi ganewa zaman kad`aici

Dan ko kalim ya gane ni tsorona yake ji madadin kusa dani daya ke kwanci koya zauna kan cinyata yanzu duk ya yadaina sai dai ya ra`be jikin kujera wani lokacin barci ya kwashe shi bashi da walwala shi kanshi in kaga walwalar shi abbanshi ya dawo

Shi kanshi ahmad yanzu hak`uri kawai yake wajen watanni biyu kenan suna cikin wannan halin zata dafa abinci zata yi komai amma bata da walwala sam dai dai da hakk`inshi na aure in yana nema tana bashi sai dai sam babu wani armashi wani lokacin in abun ya tashi har ture shi take batason jinsa kusanta sam

Yau ma kamar kullum haka na tashi sai dai `bacin ran yau yafi na kullum haka kawai tun safe da ahmad ya fita nasamu na tattara d`akin na gyara na yi abincin karyawa ko wanka banwa yaran ba bare ni nayi na yi kwanciyata ko girkin rana ban d`ora ba
Bare na dare har gashi yanzu karfe biyar na yamma harda minti uku

Kalim dai na deba mai sauran abin karin da nayi yaci doya ce da kwai dana soya mana sai ruwan shayi ni kam komai ban iya,sawa a bakina ba saboda tsabar bak`in cikin dake nukurkusata hankalina gaba d`aya yayi kano kamar akan k`aya nake
Daya ke ba sallah nake ba iya kacina in tashi inyi fitsari indawo in kwanta

Walid yayi kashi intashi in wanke mishi ma ina har ya fara fitowa a pampers d`in

Sallamar ahmad naji
Amma in amsa haka kawai nake ga aikine na k`ara maida kaina na gyara kwanciyata

Shi kwa jin yayi sallama ba a amsa ba sannan ga wani tsami tsami da yake jin yana tashi a d`akin ya shiga bin d`akin da kallo nan yaganta kwance ga walid yayi kashin har ya taba zanin da suka yi shimfid`a dashi dan kan tabarma take sai zanin data shimfid`a

Kalim da tun shigowar abban nashi ya zabura da sauri yayi wajen shi ya k`ank`ame shi shima kama yaron yayi ya dauke shi nan ya shiga binsa da kallo ganin tun kayan da ya fita ya barshi da shine a jikin sa ita,kanta aminatun hakane alamar dai babu wanda yayi wanka a cikinsu

Jiyayi ranshi ya fara `baci dan halin aminatu ya fara isar sa baisan meke damunta ba sam ya ya zata bar yara babu wanka inma dashi take fushinta bai kamata ya shafi yara ba sai kuma wani tunani ya d`arsu a ransa sai ya ajiye kalim ya k`arasa wajen ta

Tsugunnawa yayi kusa dani ina jinsa ya lek`a fuskata nan yaga idona biyu hannun sa ya kai wuyana ya taba qaunah lafiya kuwa meke damun ki ne ko baki da lafiya ne naga tun safe bakiwa yarannan wanka ba

Sannan baki ga kashin da yaronnan yayi ba gashi har ya fara fitowa alamar tun safe baki cire masa pampers d`in ba bare batun wanka

Tashi nayi cikin fushi ina gyara d`aurin zanina kaga lafiyata k`alau ni kadaina lak`amin ciwo malam wanka banyi niyar yi musu b kashi kuma nagani sai me eh wankewar ne bazanyi ba
Ehhe na k`arasa fadar cikin murgud`a baki na galla masa harara naja tsaki na maida kaina na kwanta

Dan har ga allah ni kad`ai nasan irin tsanar shi dana keji a raina ga zafin ran danake ji

Kalim da tun da tafara masifa ya koma bayan abbanshi ya rabe dan shi kanshi tsoronta yake ji bare daya ji tanawa abbanshi fad`a

Ahmad kam mamakine ya kamashi ganin yau abin nata har da tsaki inda tunda take abunta iyakaci tace tagaji ya maida ta gida ko kuma ta k`i kulasa inyana magana ko dukan kalim in yayi laifi kad`an amma yau harda su tsaki

Ga kuma yara data barmai babu wanka sannan tace batayi niya ba mekenan me aminatu keson maida kanta girgiza kai kawai yayi

Ya tashi yaje ya jona ruwan zafi ya dawo bayan ruwan yayi ya sirka da kanshi ya fara yiwa kalim wanka tukun ya tsugunna kusa da ni yasa hannu y d`auke walid dani kaina warin kashin ya dameni amma k`unci dake nukurkusata ya hana in ji a raina ya damenin ko na wanke mai

Ina kallon shi shima ya masa wanka ya dawo ya nade shi a zani ya kwantar kan gado ya kwashe shimfidar ya fita alamar wanke zanin yayi

Ya shirya yaran walid daya ji dad`in ruwan zafi tuni yayi barci nan ya dawo ya rik`o hannun kalim suka zauna kan kujera

,ya kalleni ina abinci ?

Banyi ba shine amsar dana bashi kawai

Bakiyi ba fa kika ce wai meke damunki ne um ?

Mena miki ne kike k`ok`arin ganin kin walahar dani qaunah
Me kike so ne?

Kinfi son ko yaushe kiga raina ya `baci kin tada min hankali ina kike son nasa raina kwata kwata kin canza halayen ki na da kin aro halayen da bana ki ba harfa ni kikaiwa tsaki ni qaunah

Ya fad`a yana mai nuna kanshi da yatsa alamar abin na cimai rai duk maganar daya ke cikin sanyin murya yake yinta

Ai kwanciyar hankalin
Ka kawai ka maida ni mahaifata kawani d`aukoni ka kawo ni wannan mugun garin haka kawai kaini bansan k`addara data sa na aure kaba ma wallahi
Ni ka maida ni gida kawai kasakeni na gaji da auren

Nagaji nagaji ni kasakeni nace ina mai fad`in hakan cikin hargagi
Na fashe da kuka ni kad`ai nasan me nake ji a jikina

Da ruhina jina nake kamar akan k`aya fatana kawai in bar garinnan in rabu da ahmad dan ni kadai nasan irin tsanar dana masa dauriyata ta k`are sam

Subhanallah qaunah saki kuma kiyi hakuri pls nan ya shiga rarrashina duk ya rikice dan banta `ba cewa ya sake niba duk inda ya taroni saina botse ganin kalim yana kallon mu yasa shi tashi ya kama hannun kalim ya fita can jimawa sai gashi ya dawo

Zama yayi ya kamoni ya mik`ar ya rungumeni ya shiga lallashi na yana bani bakin inyi hak`uri har bikin yaya yusuf yazo tunda duka duka wata uku ya rage

Lokacin daya ce hakanne na k`ara rikicemasa akan gobe gobe ma nake son komawa gida

ganin dai bashi da yadda zai dani ya lallabani akan in shirya goben mu wuce amma da sharad`in babu batun sai in ankwana biyu zai barmu can inna huta na dawo
Chapter 62 · 0% Book details