Sashe 14
Tushen Mu Daya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Haka kwa zaije cikin yarinta in ya kawo mata ta cire naira goma ko ashirin a cikin kudin ta bashi tana samai albarka sata takeso ta koya masa ta karfi da yaji
Ko makaranta wani lokacin inya shirya zaije takan kwabe masa uniform tace kaje kayi wasanka ba kullum ake karatuba haka zai fice abinshi yana murna yana ganin mamanshi tafi kowa sonsa
Malam ma ya farga ana mai sata amma baitaba kawowa ahmad bane sabo da ganinshi ai bai isa daukar kayan wani ba kuma duk wata bukata yana kokarin saukewa iyalansa yadai yi shiru ya kudiri niyar zaisa ido akan duk mai mai hakan yadai san babu
Mai shigarmai daki inya dawo daga
Ahmad sai hajjo
Ana haka rannan ya kwabe kayansa zai shiga wanka har yakai ruwan sai ya fasa ya leko ta bandaki yaga ahmad ya fito daga dakin hajjo ya doshi dakinsa cikin sanda
Sai ya fito ahankali yabi bayanshi bayan yagama shigewa da yake rigar daya cire nacan sakale sai yaga yadauki wata yar kujera yasaka da kyar ya janyo rigar yasa hannu a aljihun yana lalubawa ya ciro kudin ya bar rigar nan dan bashida wayon wani
Mayarwa
Ya juyo kenan suka ido hudu da malam musa wanda ke kallon shi hawaye na zuba a idonshi
take jikinshi ya fara rawa yafara kuka saboda shima yafa ji ajikinshi cewa babu kyau abin da yakeyi kawai dan hajjo ta fison hakanne kuma sannan ta mai kashedi karya sake
Yace ita ta ke aikenshi
Inba hakaba zata yankashi
Malam ya karaso ya durkusa a gabanshi ya kama hannayensa yana kallon kudin sannan ya dago kanshi
Da kyar yace ahmadina meyasa kake daukar abin daba naka ba me zakai da kudade harhaka um me kake son siya da bazaka iya tambayata ba naba ka ?
Ahmad ya girgiza kai babu komai baba Ba abin dazan siya
Yace tom kuma kake taba kayan daba nakaba bakasan babu kyau taba kayan wani ba koda kuwa na mahaifane allah yana kona duk me daukar kayan wani
Kasan barawo?
Ahmad ya daga kai yace eh baba irin wanda aka wuce dashi rannan ta bayan layi anata dukanshi yara na masa ihu
Malam musa yace shima daukar kayan mutane yayi kuma daga gida ake farawa ahmadina banason watarana akamamin kai kana aikata hakan kaji kadaina karka kara kaji
Ahmad yana kuka yace nibanaso a konani kuma,banason adakeni ana yawo dani baba
Ya janyoshi jikinshi ya rungume yana shafa bayanshi yawwa ahmadina allah yamaka albarka yakare ka daga sharrin masu sharri
Yaron yace amen baba
Hajjo dataji ahmad shiru baidawo ba ta biyo bayanshi harzata daga labule saitaji abin da suke cewa gabanta na faduwar
Karfa ahmad yace ita ke aikoshi ya zubda mata mutumci gurin malam
Sai kuma.
Taji sabanin hakan
Bai tambayeshi wake aiko shi ba
Sai kokarin hanashi dabi,ar da taji yanayi
Tayi kwafa ta juya ai wallahi malam ka makaro indai ina raye sai ahmad ya lalace koda kwa zanyi yawo tsirarane
Nadai san ta bangaren fadamasa bani ce mahaifiyarsa ba nagama da kowa ta wannan fanni saboda har ita zainabun dake takamar zata tona na rufe bakin shegiya bare wani sakaran mijinta
Takarasa maganar tana mai shigewa daki
Haka dai malam musa yayi kokarin canzawa ahmad makaranta can kusa da shagonsu dan yana zargin yaran makarantar da yake zuwane ke dorashi a hanyar inda ahmad na dawowa ta makarantar boko zai wuce shagonsu in yadawo nan yake zama
Kafin lokacin islamiyya yayi inda nan tsallaken shagonne malam musa da kanshi ke mikashi in antaso sai ya kara zama zuwa lokacin tashin malam musa sai su dawo gida tare
Hajjo bataji dadin wannan hukuncin da malam ya yanke ba amma ganin
Kartayi magana malam yace tanada wata manufa saitayi shiru
Saboda ita yanzu ta kanta take laulayi yasakota gaba
Amma fa taci burin duk tsaron da malam zaibawa ahmad,saita rushe shi kota tsiya kota arziki indai tana raye kuma bokaye suna wanzuwa a bayan kasa
************************
Dare ya raba inda kowanne me rai ya na makwancinsa sai dai wadan da fitar ta zamewa dole da kuma wadanda ke fitar dan radin kansu
Buga kofar gidan ake iya karfi abdullahi da dakinsu shine farkon shigowa shi yafara ji ya fito lokacinne kuma malam musa yafito a lokacin karfe biyu da rabi na dare
Ya kalli yayanshi yace yaya buga kofa akefa
Malam musa yace eh muje muga waye da tsohon darennan allah yasa lafiya
Nan suka karasa sai malam musa yaji muryar daya daga cikin .masu gadin kasuwar da suke ne
Suka bude suka ganshi a firgice yana haki
Malam musa kuzo muje babu lokaci shagonku yakama da wuta kuma abin mamaki shi kadaine babu inda wutar ta taba sai shi anyi anyi a kashe wutar taki mutuwa
Innanillahi wa,inna ilaihirraji,un shine kawai abin da suke maimaitawa
Sukayi saurin juyawa gida abdullahi da babu riga jikin sa yasako
Malam musa da yatarda hajjo ido biyu yace maza kizo ki rufe gidan fita ta kamamu
Malam lafiya meyafaru?
Ta tareshi da tambayoyi
Yace inmundawo kwaji ki tabbatar kin rufe gidan cikin hanzariya fita
****************"********
Tashin hankali wanda ba asa masa rana sunje sun tarda shagon gaba daya wuta ta mamayeshi babu wani guri da ya rage
Anyi anyi wutar ta mutu amma kamar karata ake
Kuma abin mamaki iya shagonsu ne haka akaita fama amma wutar tayi biris
Saida ta cinye kayan shagon kakaf babu abinda tabari sannan cikin wani ikon allah kuma saita fara raguwa da kanta harta mace sai hayaki
Shagon yakoma kamar bashiba tuni Abdullahi ya sume aka kwashe shi ranga ranga sai asibiti
Malam musa kwa yadai zauna ne a dandagaryar kasa ba um ba um um
Zuwa lokacin asuba tayi sai zuwa jaje ake musu ana allah yakiyaye gaba cikin tausayawa
Haka malam musa ya lallaba da taimakon abokin kasuwancinsa da shima ya taso
Samakon labarin dayasamu shaguna naci da wuta shagonshi na jikin nasu malam musa shine yataimakawa malam musa sukaje masallaci sukayi sallah
Daga nan suka wuce asibiti inda suka tarda Abdullahi ya farfado
Likitan yace razana ce tasashi suma andubashi babu wata matsala aka basu sallama
Suka dawo gida jiki a sanyaye
Hajjo da zainabu da sunkasa tabuka komai suna cikin fargaba suka tare su harsuna hada baki gurin tambayar lafiya
Yanayin yadda suka shigo malam na rike da hannu abdullahi shima kanshi kokari yake da zaisamu mai rike shi so yake
Haka suka zauna a tsakar gidan jigum jigum dan duk babu wanda ya iya magana a cikinsu
Can dai malam musa yayi karfin halin dagowa da kyar yace kuyi hakuri mu rungumi kaddarar data rinkemu
Shagonmu na kasuwa ne ya kone kurmus babu abin da aka samu aka fitar duk wuta ta cinyesu
Hajjo ta zabura da karfi tana mai kama kirjinta
Kana nufin shagon ku dai ya kone
Wayyoh mun shiga ukunmu mun lalace shikenan shikenan wayyoh allah na
Haka take ta sambatu
Wanda zainabu ita batasan ma lokacin data karaso kusa da abdullahi ba ta kama kafadunsa tana girgiza shi
Wai baban Ummi sunan diyarta ta fara
Kana nufin kace min Shagon da muke samun abinci ta hanyarshi ya kone?
Ya dago ya kuramata ido can ya daga mata kai kamar karamin yaro
Ita nan tabi layin hajjo sunata karadin ihu da koke koke kamar ance uwarsu ta mutu
Makotane suka fara shigowa duk wanda yashigo sai su fara bashi labari haka akadinga yiwa su malam musa jaje
Cikin tausayawa inda ana ganin basu hajjo bane yakamata suyi kuka ba amma su sunyi tawakkali sai dai na zuci
*************************
Bayan kwana biyu hukumar kasuwa ta harhada musu tallafin datake bawa duk wanda wani ifti,la,i yasama
Amma ina kudaden bawasu masu yawa bane ko iya gyaran shagon zai cinye bare ayi maganar
Zuba kaya
Gashi dama daran ranar da aka kawo musu kaya adaran shagon yakama da wuta dai dai da cinikin ranar basu irgaba yana shagon
Gashi a lokacin bankuna basu wani yawaita ba bakowa ne yayarda da ajiyar banki ba
Basu ajiyar kudi gida kuma ga shi har bashi suka ci dan rabin kayan da aka kawo musu duk bashine saboda suna shirin raba shagon
Biyune
Kowa ya kula da nashi saboda halin rayuwa kowa ya fara tara iyali
Saiga wannan kaddarar
Haka suka hakura da gyara shagon suka dawo gida suka zauna kudin da ke hannunsu dashi suke hidimar gida
Haka dai har aka shafe wata guda babu wata hanya da suka gani da har zasu san yadda zasuyi
Lokacinne kuma mai kaya yasakosu gaba inda babu sani babu sabo ya uzzura musu
Ganin basu da wata hanyar da zasu biyashi
Yasa suka yanke shawarar saida gidan inyaso su kama haya sai su biyashi sai yabasu wasu kayan inyaso sai suyi kokarin gyara shagon da sauran kudin
Ai zainabu najin labarin za asaida gida ta tashi hankalinta masifar yau da ban ta gobe da ban ita saidai abdullahi yasaketa baza a saida gidaba
Tun yana lallabata har karshe ta kaisu ga sakin ta tattara yaranta ta yi gaba inda yabar mata sune kafin hankalinsa ya kwanta ya amso yaransa dama yagaji da halinta
Gwara rabuwarta su matar da bazata so rufin asirinka ba meye amfanin zama da ita
Ita hajjo ta bangarenta tafi nono fari alhininta kawai akan dukiyar da suka rasa ne amma ita burinta yanzu su bar garin suyi nesa da kano inyaso ta
Cika burinta cikin ruwan sanyi babu wanda
Yasanta tafiyar zainabu ma
Tafi komai yimata dadi dama fargabarta kenan kuma ta tafi
Saita kwantar da hankalinta
Inda,daga karshe aka yi cinikin gidan aka saida
Suka kama haya suka biya mai kaya kudinsa sai dai
Wata sabuwa yace shi sam bazai kara musu kayaba yama gode da kudinsa ya fito haka suna ji suna gani suka yi hakuri
Inda suka shiga buga bugar hanyar da zasubi don samun rufin asirinsu da kuma na su hajjo
Inda allah ya hada malam musa da wani abokin sa amma shi ba mazaunin kano bane
Yabashi shawarar. Ya bishi suje can inda yake aikin biredi yakeyi a Niger state Lapai insunje ko allah zaisa adace
Malam musa yayi na.am da shawarar sa yace amma sai dai inje nikadai nadinga dawowa ? Saboda iyalina bansan ina zan ajesuba
Ko makaranta wani lokacin inya shirya zaije takan kwabe masa uniform tace kaje kayi wasanka ba kullum ake karatuba haka zai fice abinshi yana murna yana ganin mamanshi tafi kowa sonsa
Malam ma ya farga ana mai sata amma baitaba kawowa ahmad bane sabo da ganinshi ai bai isa daukar kayan wani ba kuma duk wata bukata yana kokarin saukewa iyalansa yadai yi shiru ya kudiri niyar zaisa ido akan duk mai mai hakan yadai san babu
Mai shigarmai daki inya dawo daga
Ahmad sai hajjo
Ana haka rannan ya kwabe kayansa zai shiga wanka har yakai ruwan sai ya fasa ya leko ta bandaki yaga ahmad ya fito daga dakin hajjo ya doshi dakinsa cikin sanda
Sai ya fito ahankali yabi bayanshi bayan yagama shigewa da yake rigar daya cire nacan sakale sai yaga yadauki wata yar kujera yasaka da kyar ya janyo rigar yasa hannu a aljihun yana lalubawa ya ciro kudin ya bar rigar nan dan bashida wayon wani
Mayarwa
Ya juyo kenan suka ido hudu da malam musa wanda ke kallon shi hawaye na zuba a idonshi
take jikinshi ya fara rawa yafara kuka saboda shima yafa ji ajikinshi cewa babu kyau abin da yakeyi kawai dan hajjo ta fison hakanne kuma sannan ta mai kashedi karya sake
Yace ita ta ke aikenshi
Inba hakaba zata yankashi
Malam ya karaso ya durkusa a gabanshi ya kama hannayensa yana kallon kudin sannan ya dago kanshi
Da kyar yace ahmadina meyasa kake daukar abin daba naka ba me zakai da kudade harhaka um me kake son siya da bazaka iya tambayata ba naba ka ?
Ahmad ya girgiza kai babu komai baba Ba abin dazan siya
Yace tom kuma kake taba kayan daba nakaba bakasan babu kyau taba kayan wani ba koda kuwa na mahaifane allah yana kona duk me daukar kayan wani
Kasan barawo?
Ahmad ya daga kai yace eh baba irin wanda aka wuce dashi rannan ta bayan layi anata dukanshi yara na masa ihu
Malam musa yace shima daukar kayan mutane yayi kuma daga gida ake farawa ahmadina banason watarana akamamin kai kana aikata hakan kaji kadaina karka kara kaji
Ahmad yana kuka yace nibanaso a konani kuma,banason adakeni ana yawo dani baba
Ya janyoshi jikinshi ya rungume yana shafa bayanshi yawwa ahmadina allah yamaka albarka yakare ka daga sharrin masu sharri
Yaron yace amen baba
Hajjo dataji ahmad shiru baidawo ba ta biyo bayanshi harzata daga labule saitaji abin da suke cewa gabanta na faduwar
Karfa ahmad yace ita ke aikoshi ya zubda mata mutumci gurin malam
Sai kuma.
Taji sabanin hakan
Bai tambayeshi wake aiko shi ba
Sai kokarin hanashi dabi,ar da taji yanayi
Tayi kwafa ta juya ai wallahi malam ka makaro indai ina raye sai ahmad ya lalace koda kwa zanyi yawo tsirarane
Nadai san ta bangaren fadamasa bani ce mahaifiyarsa ba nagama da kowa ta wannan fanni saboda har ita zainabun dake takamar zata tona na rufe bakin shegiya bare wani sakaran mijinta
Takarasa maganar tana mai shigewa daki
Haka dai malam musa yayi kokarin canzawa ahmad makaranta can kusa da shagonsu dan yana zargin yaran makarantar da yake zuwane ke dorashi a hanyar inda ahmad na dawowa ta makarantar boko zai wuce shagonsu in yadawo nan yake zama
Kafin lokacin islamiyya yayi inda nan tsallaken shagonne malam musa da kanshi ke mikashi in antaso sai ya kara zama zuwa lokacin tashin malam musa sai su dawo gida tare
Hajjo bataji dadin wannan hukuncin da malam ya yanke ba amma ganin
Kartayi magana malam yace tanada wata manufa saitayi shiru
Saboda ita yanzu ta kanta take laulayi yasakota gaba
Amma fa taci burin duk tsaron da malam zaibawa ahmad,saita rushe shi kota tsiya kota arziki indai tana raye kuma bokaye suna wanzuwa a bayan kasa
************************
Dare ya raba inda kowanne me rai ya na makwancinsa sai dai wadan da fitar ta zamewa dole da kuma wadanda ke fitar dan radin kansu
Buga kofar gidan ake iya karfi abdullahi da dakinsu shine farkon shigowa shi yafara ji ya fito lokacinne kuma malam musa yafito a lokacin karfe biyu da rabi na dare
Ya kalli yayanshi yace yaya buga kofa akefa
Malam musa yace eh muje muga waye da tsohon darennan allah yasa lafiya
Nan suka karasa sai malam musa yaji muryar daya daga cikin .masu gadin kasuwar da suke ne
Suka bude suka ganshi a firgice yana haki
Malam musa kuzo muje babu lokaci shagonku yakama da wuta kuma abin mamaki shi kadaine babu inda wutar ta taba sai shi anyi anyi a kashe wutar taki mutuwa
Innanillahi wa,inna ilaihirraji,un shine kawai abin da suke maimaitawa
Sukayi saurin juyawa gida abdullahi da babu riga jikin sa yasako
Malam musa da yatarda hajjo ido biyu yace maza kizo ki rufe gidan fita ta kamamu
Malam lafiya meyafaru?
Ta tareshi da tambayoyi
Yace inmundawo kwaji ki tabbatar kin rufe gidan cikin hanzariya fita
****************"********
Tashin hankali wanda ba asa masa rana sunje sun tarda shagon gaba daya wuta ta mamayeshi babu wani guri da ya rage
Anyi anyi wutar ta mutu amma kamar karata ake
Kuma abin mamaki iya shagonsu ne haka akaita fama amma wutar tayi biris
Saida ta cinye kayan shagon kakaf babu abinda tabari sannan cikin wani ikon allah kuma saita fara raguwa da kanta harta mace sai hayaki
Shagon yakoma kamar bashiba tuni Abdullahi ya sume aka kwashe shi ranga ranga sai asibiti
Malam musa kwa yadai zauna ne a dandagaryar kasa ba um ba um um
Zuwa lokacin asuba tayi sai zuwa jaje ake musu ana allah yakiyaye gaba cikin tausayawa
Haka malam musa ya lallaba da taimakon abokin kasuwancinsa da shima ya taso
Samakon labarin dayasamu shaguna naci da wuta shagonshi na jikin nasu malam musa shine yataimakawa malam musa sukaje masallaci sukayi sallah
Daga nan suka wuce asibiti inda suka tarda Abdullahi ya farfado
Likitan yace razana ce tasashi suma andubashi babu wata matsala aka basu sallama
Suka dawo gida jiki a sanyaye
Hajjo da zainabu da sunkasa tabuka komai suna cikin fargaba suka tare su harsuna hada baki gurin tambayar lafiya
Yanayin yadda suka shigo malam na rike da hannu abdullahi shima kanshi kokari yake da zaisamu mai rike shi so yake
Haka suka zauna a tsakar gidan jigum jigum dan duk babu wanda ya iya magana a cikinsu
Can dai malam musa yayi karfin halin dagowa da kyar yace kuyi hakuri mu rungumi kaddarar data rinkemu
Shagonmu na kasuwa ne ya kone kurmus babu abin da aka samu aka fitar duk wuta ta cinyesu
Hajjo ta zabura da karfi tana mai kama kirjinta
Kana nufin shagon ku dai ya kone
Wayyoh mun shiga ukunmu mun lalace shikenan shikenan wayyoh allah na
Haka take ta sambatu
Wanda zainabu ita batasan ma lokacin data karaso kusa da abdullahi ba ta kama kafadunsa tana girgiza shi
Wai baban Ummi sunan diyarta ta fara
Kana nufin kace min Shagon da muke samun abinci ta hanyarshi ya kone?
Ya dago ya kuramata ido can ya daga mata kai kamar karamin yaro
Ita nan tabi layin hajjo sunata karadin ihu da koke koke kamar ance uwarsu ta mutu
Makotane suka fara shigowa duk wanda yashigo sai su fara bashi labari haka akadinga yiwa su malam musa jaje
Cikin tausayawa inda ana ganin basu hajjo bane yakamata suyi kuka ba amma su sunyi tawakkali sai dai na zuci
*************************
Bayan kwana biyu hukumar kasuwa ta harhada musu tallafin datake bawa duk wanda wani ifti,la,i yasama
Amma ina kudaden bawasu masu yawa bane ko iya gyaran shagon zai cinye bare ayi maganar
Zuba kaya
Gashi dama daran ranar da aka kawo musu kaya adaran shagon yakama da wuta dai dai da cinikin ranar basu irgaba yana shagon
Gashi a lokacin bankuna basu wani yawaita ba bakowa ne yayarda da ajiyar banki ba
Basu ajiyar kudi gida kuma ga shi har bashi suka ci dan rabin kayan da aka kawo musu duk bashine saboda suna shirin raba shagon
Biyune
Kowa ya kula da nashi saboda halin rayuwa kowa ya fara tara iyali
Saiga wannan kaddarar
Haka suka hakura da gyara shagon suka dawo gida suka zauna kudin da ke hannunsu dashi suke hidimar gida
Haka dai har aka shafe wata guda babu wata hanya da suka gani da har zasu san yadda zasuyi
Lokacinne kuma mai kaya yasakosu gaba inda babu sani babu sabo ya uzzura musu
Ganin basu da wata hanyar da zasu biyashi
Yasa suka yanke shawarar saida gidan inyaso su kama haya sai su biyashi sai yabasu wasu kayan inyaso sai suyi kokarin gyara shagon da sauran kudin
Ai zainabu najin labarin za asaida gida ta tashi hankalinta masifar yau da ban ta gobe da ban ita saidai abdullahi yasaketa baza a saida gidaba
Tun yana lallabata har karshe ta kaisu ga sakin ta tattara yaranta ta yi gaba inda yabar mata sune kafin hankalinsa ya kwanta ya amso yaransa dama yagaji da halinta
Gwara rabuwarta su matar da bazata so rufin asirinka ba meye amfanin zama da ita
Ita hajjo ta bangarenta tafi nono fari alhininta kawai akan dukiyar da suka rasa ne amma ita burinta yanzu su bar garin suyi nesa da kano inyaso ta
Cika burinta cikin ruwan sanyi babu wanda
Yasanta tafiyar zainabu ma
Tafi komai yimata dadi dama fargabarta kenan kuma ta tafi
Saita kwantar da hankalinta
Inda,daga karshe aka yi cinikin gidan aka saida
Suka kama haya suka biya mai kaya kudinsa sai dai
Wata sabuwa yace shi sam bazai kara musu kayaba yama gode da kudinsa ya fito haka suna ji suna gani suka yi hakuri
Inda suka shiga buga bugar hanyar da zasubi don samun rufin asirinsu da kuma na su hajjo
Inda allah ya hada malam musa da wani abokin sa amma shi ba mazaunin kano bane
Yabashi shawarar. Ya bishi suje can inda yake aikin biredi yakeyi a Niger state Lapai insunje ko allah zaisa adace
Malam musa yayi na.am da shawarar sa yace amma sai dai inje nikadai nadinga dawowa ? Saboda iyalina bansan ina zan ajesuba