Sashe 12
Tushen Mu Daya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ah lallai masha allah allah yasanya alkhairi ta fada cikin zallar bakin ciki da nata kudirin daban
Bayan tafiyarsu ta shiga daki tarasa inda zata sa kanta tayi nan tayi nan can ta bushe da mahaukaciyar da riya cike da mugunta tace
Wallahi wallahi Talatuwa ke wawiyace amma zan koya miki hankali Badai dan dukiyar musa kika aura masa kanwarkiba wato babu gado bari a koma aci a inda yake samu
Hhhh ta kara fashewa da dariya indai ni asabe ina raye ko arzikin musa bazanbari suyi ba bare har a fantama da dukiya kuma su da garinnan sai bayan raina muddin ina raye kanwarkima ta tafi kenan mu zuba mugani shege ka fasa
Sukwa ana can su malam musa ana shirye shirye daurin aure inda bayan daurin auren Mero da malam musa suka rankayo nigeria
***********"*************
Kwatsam saiga malam musa daga zuwa ganin gida ya dawo da mata Inda ya tunkari hasana yamata bayanin baikara aure ba don ya wulakantata ba
Da dai sauran kalaman kwantar da hankali
Allah sarki hasana mace me hakuri da takwakkali tace babu komai ina zata zauna malam ?
Yace dayan dakin da kike aje kwanika zaki dawo dasu nan sai ita ta zauna a nan
Tace babu komai ya hadasu ya musu nasihar zaman lafiya
Hasana ta kwashe kayanta yasaka Mero wadda Dawowarta Kano sunanta ya rikida ya koma hajjo sakamakon sunan mahaifiyar hasanar ne saboda haka suke cewa mahaifiyarsu shiyasa ta saya sunan ya koma hajjo
Tun daga nan sunan ya bita
Da ta kwantar da hankalinta ana zaman lafiya amma daga baya ta tsiro da salon munafurci da Kisisina yau ta hada malam musa da,hasana husuma gobe ta hadashi da abdullahi kaninsa
Hakadai tazamemusu masifa a gida hasana nasane da ita ke duk wannan munafurcin
Amma don azauna lafiya bata biyemata ba saidai tana taka tsan tsan da abinda zai hadasu
**********""""*""*********
Ana nan abdullahi ya hadu da wata bakatsiniya tana kawo tallar abinci shagonsu me suna zainabu Zainabu irin yan matannan ne masu budadden ido sannan ga rashin kamun kai gata girma batayi aure ba
Amma a haka abdullahi yace yaji yagani ita yakeso
Inda yayanshi yashigemai gaba akai auran ta tare a dakin da abdullahi ke kwana yazama gidan su uku kenan
Tunda zainabu ta shigo sai hajjo tasa mu abokiyar cin mushe suka hadewa hasana kai
Inda zainabu ma na shige shigen malamai ta silar hakanne nema ta auri abdullahi tuni suka dinke takara dora hajjo akan hanya
Rana daya aka wayi gari hasana ta tubure ita bazata kara kwana garin ba tagaji da zama da malam musa gida zataje
Malam musa yayi yayi taki hakura hakadai ya shiryata ya kaita gida da kansa ko in hankalinta,ya kwanta kwana biyu zata yarda su dawo
Ya tsaya jiranta har wasu kwanaki amma bata canja zani ba
Liman yace yayi hakuri ya koma in hankalinta ya kwanta ya dawo ya dauketa
Haka malam musa ya dawo gida jikinshi a sanyaye saboda gaskiya shi yanason matarshi amma dole tasa ya hakura zuwa lokacin da zata yarda ta dawo
Ai hasana na barin gida hajjo ta baje kolinta ta samu yadda takeso
Sun kara curewa ita da zainabu sai abin da suka cewa mazajensu za ayi takai ta kawo malam musa na mugun tsoron Hajjo baya taba
Mata musu akan abin
Datace komene ne
*************************
Bayan Tafiyar malam musa hasana ta warware tana harkar ta kamar ba itaba sai dai ko maganar komawa gidan malam musa bataso sam
Kuma sannan ne tafara kananun ciwo yau da lafiya gobe babu inda mahaifiyar ta ta gano cewa lallai tana da juna biyu
Tasamu malam da maganar cikin tsananin farin ciki tana fadamai shikenan ga hanyar komawar hasana dakinta
Malam ya maza ya kwabeta da karta sake yaji maganar su binne maganar cikin hasana danshi yasan tana da makiya su bar maganar a tsakaninsu zai cigaba
Da mata addu a dan yasan cewa tabbas wannan rashin zaman nata wajen mijinta ba banza ba
Haka kuwa akayi hasana tacigaba da rainon cikinta batare da sanin kowa ba ko su asabe basuda labari saboda bawani damuwa sukai da ita ba
Sannan itanma tunda tadawo bata wani fitowa ko tsakar gida bare suji labarin cikin wajen yan gulma
***********************
Malam musa tunda yakoma baikara tunanin komawa gida wajen hasana ba saboda anciremai tunanin hakan kwata kwata
Hajjo kuma duniyata tasamu yadda takeso sai dai ko batan wata bata taba yiba kusan shekara guda kenan da auransu amma shiru tayi
Buge bugen tayi neme nemen maganin abanza shiru kake ji
Inda ta addabi malam musa ita haihuwa take so kodai shine baya haihuwar da dai sauran maganganu
Yakan cemata komai lokacine
Ahaka har zainabu tasamu nata cikin zo kuga iyayi da kisisina saita fara yiwa hajjo gorin ciki abin na kona zuciyar hajjo amma takan danne saboda
Tana amfanuwa da zainabun ba kadanba
Zainabu taciga ba da renon cikinta cikin cin burin haihuwar da namiji dan ita dukiyar su abdullahi takeson handamewa itama nata burin daban
Har addu a take allah karya bawa hajjon
Kai allah yarabamu da Mugun mutum abin da allah ne ke kyautarshi ga wanda yaso saboda tsaurin ido irin na dan adam sai ya iya daga hannu ya roki allah karya ba wani wa,iyazubillah
************************
Haka hasana ta cigaba da rainon cikinta watarana ta shi da nakuda inda mahaifiyarta ta ita karbi haihuwar ta haifi danta santalele inda bayan haihu aka gyareta tsaf
Sai bayan komai ya lafa tukun aka je gidan su asabe aka fadi haihuwar
Lokacin da sukaji bakaramin firgita suka yi ba sun shiga rudu shin wacce hasanar ce ?
Aka hasana dai matar malam musa
Suka kwashi mayafai sukaje donsu tabbatar duk da suna cikin rudu yaya akai ta haihu bayan duk irin kudaden da suka kashe
Sun tarar da mai jego cikin koshin lafiya ita da kyakykyawan jaririnta
Inda aka tarbesu cikin mutumci duk kokarinsu na kar su tona halin da suke ciki na bakin ciki da hassada kiri kiri hakan ya kasa boyuwa
Dan talatuwa ma da aka miko mata yaron kin amsa tayi tana allah ya raya dai barshi basaina dauka ba ainaganshi ma barcinsa yake
Haka suka dawo kowacce ta kasa zaune ta kasa tsaye gashi yanzu sundaina sakin jiki da junansu bare su kulla wadda zasu kulla
************************
Bayan tafiyar su mahaifiyar hasana tashiga shakku akan irin yadda suka zo da kuma yanayin su
Da liman yadawo tafada masa komai dan ita gaskiya bata yarda da suba sam dagani akwai wata akasa
Liman yajamata gargadi me tsauri karta yarda insun kara zuwa tabasu jinjirin sannan ita kanta hasanar indai basun zo sunganta a tsakar gidaba
Karta barsu suganta tce tayi barci shi yanzu burinshi malam musa ya waiwayo gida yazo yaga gudan jininshi
Tunda ba zamanin waya bane bare asanar mai
Hasana taciga ba da shayar da yaronta wanda ranar suna na zagayowa yaci sunan sa Ahmad wanda liman ne ya rada masa yayi komai da yakamata uba yayiwa yaro kama daga suturarshi zuwa ragon suna da dai sauran hidindimu
Wanda daga bangaren su asabe babu ko allura data fito daga wajensu sunan sunyi jika
sunsha zuwa gidan liman da sunan ganin jariri amma ba abasu kamar yadda liman yabada umarni hakan na musu ciwo dan suna da nasu
Kudurin nazuwan kowacce burinta ta hallakar da yaron
Haka dai har ahmad yacika shekara Daya yana tafiyarsa ko ina
Asanne ne kuma hasana ta fara wani irin ciwo tun tana yi a tsaitsaye har ta kaita ga kwanci inda kullum cikin nemar mata magani ake
Amma fa shiru akace wai malam yaci shirwa
Tafi tafi har yazama ko magana bata iyawa
Lokacin dole tasa aka cire ahmad a nono tunda yana cin abincinsa
Gashi kuma har zuwa lokacin Malam musa bai waiwayo gida ba
Bayan doguwar jinya allah yayiwa hasana rasuwa inda malam yaji mutuwarta yarinya mai masa biyayyah duk cikin ya,yansa itace mafi soyuwa agare shi
Haka dai har bayan arba,in a lokacin ne kuma su asabe suka zo wai suna bukatar abasu ahmad su rike jikansu ya taso a gidan ubanshi
Inda malam liman yayi tsalle ya dire akan bazai taba badashi ba
Sunyi sunyi da sukaga babu riba sai suka hakura bawai dan sunbar maganar ba
Inda malam liman yadage da nemawa ahmad magungunan tsari da addu,o,i ingantattu
wanda koda mutum yaso cutar dashi da asiri to bazai taba tasiri akan shiba
Ahmad yataso yaro me hazaka da kokari ga wayo duk inda malam liman yasa kafa to fa zai aje tashi baya taba yarda yafita batare dashi ba
Zuwa lokacin yana da shekaru biyu
*************************
Hajjo har yanzu shiru babu labari wanda zuwa lokacin Zainabu ta haihu amma
Mace ta haifa duk da bataso hakan ba tanada Shekara daya takuma samun wani cikin
Hankalin Hajjo fa inyayi dubu ya tashi
Malam musa baida muba dan yasan haihuwa lokacice inyayi allah bai manta dashi ba zaibashi
Kwana biyu inya kwanta yana yawan mafarkin hasana da wani abu ahannunta tana mikomai amma kafin ya mika hannu ya amsa sai yaga ta bace beganta ba
Haka dai hankalinsa duk yayi gida
Yasamu abdullahi da maganar inda suka yanke shawarar zasuje gidan daga nan sa duba gonaki tunda ba noman suke yiba aliyune me kula da gonaki wanda shi ba noman yakeba haya duk ya bada gonakin
Yake amsar
Kudaden yana murkushewa
Bayan yanke shawarar malam musa ta tuntubi hajjo da batun tafiyar inda fa nan hankalinta ya tashi tana tsoron karfa yaje
Ya dawo da hasana shiyasa tasa boka ya ciremai tunanin hasanar sam amma data sani tsanar garin tasamai gaba daya
Gashi yace mata da asuba zasu tafi babu damar tayi komai tana ji tana gani suka tafi
*************************
Bayan zuwan sune suka samu labarin haihuwar hasana da kuma rasuwarta malam musa yayi kukan rashin mace irin hasana mace tagari
Inda ya nemi afuwar malam liman akan rashin waiwayarsu da baiyi ba
Malam liman yamai uzuri
Inda Ahmad tunda malam musa ya dauke shi ya makalkaleshi yaki bari ko sauke shine yayi
Malam musa ga abun farin ciki kuma ga akasinsa babu hasana amma hasana ta haifa masa yaro inda babu inda ya baro kamannin mahaifinsa sak
Ahmad ya kasance fari irin mai sirkin ja ja dinnan Yana da kyan shi gwargwado masha allah
Bayan tafiyarsu ta shiga daki tarasa inda zata sa kanta tayi nan tayi nan can ta bushe da mahaukaciyar da riya cike da mugunta tace
Wallahi wallahi Talatuwa ke wawiyace amma zan koya miki hankali Badai dan dukiyar musa kika aura masa kanwarkiba wato babu gado bari a koma aci a inda yake samu
Hhhh ta kara fashewa da dariya indai ni asabe ina raye ko arzikin musa bazanbari suyi ba bare har a fantama da dukiya kuma su da garinnan sai bayan raina muddin ina raye kanwarkima ta tafi kenan mu zuba mugani shege ka fasa
Sukwa ana can su malam musa ana shirye shirye daurin aure inda bayan daurin auren Mero da malam musa suka rankayo nigeria
***********"*************
Kwatsam saiga malam musa daga zuwa ganin gida ya dawo da mata Inda ya tunkari hasana yamata bayanin baikara aure ba don ya wulakantata ba
Da dai sauran kalaman kwantar da hankali
Allah sarki hasana mace me hakuri da takwakkali tace babu komai ina zata zauna malam ?
Yace dayan dakin da kike aje kwanika zaki dawo dasu nan sai ita ta zauna a nan
Tace babu komai ya hadasu ya musu nasihar zaman lafiya
Hasana ta kwashe kayanta yasaka Mero wadda Dawowarta Kano sunanta ya rikida ya koma hajjo sakamakon sunan mahaifiyar hasanar ne saboda haka suke cewa mahaifiyarsu shiyasa ta saya sunan ya koma hajjo
Tun daga nan sunan ya bita
Da ta kwantar da hankalinta ana zaman lafiya amma daga baya ta tsiro da salon munafurci da Kisisina yau ta hada malam musa da,hasana husuma gobe ta hadashi da abdullahi kaninsa
Hakadai tazamemusu masifa a gida hasana nasane da ita ke duk wannan munafurcin
Amma don azauna lafiya bata biyemata ba saidai tana taka tsan tsan da abinda zai hadasu
**********""""*""*********
Ana nan abdullahi ya hadu da wata bakatsiniya tana kawo tallar abinci shagonsu me suna zainabu Zainabu irin yan matannan ne masu budadden ido sannan ga rashin kamun kai gata girma batayi aure ba
Amma a haka abdullahi yace yaji yagani ita yakeso
Inda yayanshi yashigemai gaba akai auran ta tare a dakin da abdullahi ke kwana yazama gidan su uku kenan
Tunda zainabu ta shigo sai hajjo tasa mu abokiyar cin mushe suka hadewa hasana kai
Inda zainabu ma na shige shigen malamai ta silar hakanne nema ta auri abdullahi tuni suka dinke takara dora hajjo akan hanya
Rana daya aka wayi gari hasana ta tubure ita bazata kara kwana garin ba tagaji da zama da malam musa gida zataje
Malam musa yayi yayi taki hakura hakadai ya shiryata ya kaita gida da kansa ko in hankalinta,ya kwanta kwana biyu zata yarda su dawo
Ya tsaya jiranta har wasu kwanaki amma bata canja zani ba
Liman yace yayi hakuri ya koma in hankalinta ya kwanta ya dawo ya dauketa
Haka malam musa ya dawo gida jikinshi a sanyaye saboda gaskiya shi yanason matarshi amma dole tasa ya hakura zuwa lokacin da zata yarda ta dawo
Ai hasana na barin gida hajjo ta baje kolinta ta samu yadda takeso
Sun kara curewa ita da zainabu sai abin da suka cewa mazajensu za ayi takai ta kawo malam musa na mugun tsoron Hajjo baya taba
Mata musu akan abin
Datace komene ne
*************************
Bayan Tafiyar malam musa hasana ta warware tana harkar ta kamar ba itaba sai dai ko maganar komawa gidan malam musa bataso sam
Kuma sannan ne tafara kananun ciwo yau da lafiya gobe babu inda mahaifiyar ta ta gano cewa lallai tana da juna biyu
Tasamu malam da maganar cikin tsananin farin ciki tana fadamai shikenan ga hanyar komawar hasana dakinta
Malam ya maza ya kwabeta da karta sake yaji maganar su binne maganar cikin hasana danshi yasan tana da makiya su bar maganar a tsakaninsu zai cigaba
Da mata addu a dan yasan cewa tabbas wannan rashin zaman nata wajen mijinta ba banza ba
Haka kuwa akayi hasana tacigaba da rainon cikinta batare da sanin kowa ba ko su asabe basuda labari saboda bawani damuwa sukai da ita ba
Sannan itanma tunda tadawo bata wani fitowa ko tsakar gida bare suji labarin cikin wajen yan gulma
***********************
Malam musa tunda yakoma baikara tunanin komawa gida wajen hasana ba saboda anciremai tunanin hakan kwata kwata
Hajjo kuma duniyata tasamu yadda takeso sai dai ko batan wata bata taba yiba kusan shekara guda kenan da auransu amma shiru tayi
Buge bugen tayi neme nemen maganin abanza shiru kake ji
Inda ta addabi malam musa ita haihuwa take so kodai shine baya haihuwar da dai sauran maganganu
Yakan cemata komai lokacine
Ahaka har zainabu tasamu nata cikin zo kuga iyayi da kisisina saita fara yiwa hajjo gorin ciki abin na kona zuciyar hajjo amma takan danne saboda
Tana amfanuwa da zainabun ba kadanba
Zainabu taciga ba da renon cikinta cikin cin burin haihuwar da namiji dan ita dukiyar su abdullahi takeson handamewa itama nata burin daban
Har addu a take allah karya bawa hajjon
Kai allah yarabamu da Mugun mutum abin da allah ne ke kyautarshi ga wanda yaso saboda tsaurin ido irin na dan adam sai ya iya daga hannu ya roki allah karya ba wani wa,iyazubillah
************************
Haka hasana ta cigaba da rainon cikinta watarana ta shi da nakuda inda mahaifiyarta ta ita karbi haihuwar ta haifi danta santalele inda bayan haihu aka gyareta tsaf
Sai bayan komai ya lafa tukun aka je gidan su asabe aka fadi haihuwar
Lokacin da sukaji bakaramin firgita suka yi ba sun shiga rudu shin wacce hasanar ce ?
Aka hasana dai matar malam musa
Suka kwashi mayafai sukaje donsu tabbatar duk da suna cikin rudu yaya akai ta haihu bayan duk irin kudaden da suka kashe
Sun tarar da mai jego cikin koshin lafiya ita da kyakykyawan jaririnta
Inda aka tarbesu cikin mutumci duk kokarinsu na kar su tona halin da suke ciki na bakin ciki da hassada kiri kiri hakan ya kasa boyuwa
Dan talatuwa ma da aka miko mata yaron kin amsa tayi tana allah ya raya dai barshi basaina dauka ba ainaganshi ma barcinsa yake
Haka suka dawo kowacce ta kasa zaune ta kasa tsaye gashi yanzu sundaina sakin jiki da junansu bare su kulla wadda zasu kulla
************************
Bayan tafiyar su mahaifiyar hasana tashiga shakku akan irin yadda suka zo da kuma yanayin su
Da liman yadawo tafada masa komai dan ita gaskiya bata yarda da suba sam dagani akwai wata akasa
Liman yajamata gargadi me tsauri karta yarda insun kara zuwa tabasu jinjirin sannan ita kanta hasanar indai basun zo sunganta a tsakar gidaba
Karta barsu suganta tce tayi barci shi yanzu burinshi malam musa ya waiwayo gida yazo yaga gudan jininshi
Tunda ba zamanin waya bane bare asanar mai
Hasana taciga ba da shayar da yaronta wanda ranar suna na zagayowa yaci sunan sa Ahmad wanda liman ne ya rada masa yayi komai da yakamata uba yayiwa yaro kama daga suturarshi zuwa ragon suna da dai sauran hidindimu
Wanda daga bangaren su asabe babu ko allura data fito daga wajensu sunan sunyi jika
sunsha zuwa gidan liman da sunan ganin jariri amma ba abasu kamar yadda liman yabada umarni hakan na musu ciwo dan suna da nasu
Kudurin nazuwan kowacce burinta ta hallakar da yaron
Haka dai har ahmad yacika shekara Daya yana tafiyarsa ko ina
Asanne ne kuma hasana ta fara wani irin ciwo tun tana yi a tsaitsaye har ta kaita ga kwanci inda kullum cikin nemar mata magani ake
Amma fa shiru akace wai malam yaci shirwa
Tafi tafi har yazama ko magana bata iyawa
Lokacin dole tasa aka cire ahmad a nono tunda yana cin abincinsa
Gashi kuma har zuwa lokacin Malam musa bai waiwayo gida ba
Bayan doguwar jinya allah yayiwa hasana rasuwa inda malam yaji mutuwarta yarinya mai masa biyayyah duk cikin ya,yansa itace mafi soyuwa agare shi
Haka dai har bayan arba,in a lokacin ne kuma su asabe suka zo wai suna bukatar abasu ahmad su rike jikansu ya taso a gidan ubanshi
Inda malam liman yayi tsalle ya dire akan bazai taba badashi ba
Sunyi sunyi da sukaga babu riba sai suka hakura bawai dan sunbar maganar ba
Inda malam liman yadage da nemawa ahmad magungunan tsari da addu,o,i ingantattu
wanda koda mutum yaso cutar dashi da asiri to bazai taba tasiri akan shiba
Ahmad yataso yaro me hazaka da kokari ga wayo duk inda malam liman yasa kafa to fa zai aje tashi baya taba yarda yafita batare dashi ba
Zuwa lokacin yana da shekaru biyu
*************************
Hajjo har yanzu shiru babu labari wanda zuwa lokacin Zainabu ta haihu amma
Mace ta haifa duk da bataso hakan ba tanada Shekara daya takuma samun wani cikin
Hankalin Hajjo fa inyayi dubu ya tashi
Malam musa baida muba dan yasan haihuwa lokacice inyayi allah bai manta dashi ba zaibashi
Kwana biyu inya kwanta yana yawan mafarkin hasana da wani abu ahannunta tana mikomai amma kafin ya mika hannu ya amsa sai yaga ta bace beganta ba
Haka dai hankalinsa duk yayi gida
Yasamu abdullahi da maganar inda suka yanke shawarar zasuje gidan daga nan sa duba gonaki tunda ba noman suke yiba aliyune me kula da gonaki wanda shi ba noman yakeba haya duk ya bada gonakin
Yake amsar
Kudaden yana murkushewa
Bayan yanke shawarar malam musa ta tuntubi hajjo da batun tafiyar inda fa nan hankalinta ya tashi tana tsoron karfa yaje
Ya dawo da hasana shiyasa tasa boka ya ciremai tunanin hasanar sam amma data sani tsanar garin tasamai gaba daya
Gashi yace mata da asuba zasu tafi babu damar tayi komai tana ji tana gani suka tafi
*************************
Bayan zuwan sune suka samu labarin haihuwar hasana da kuma rasuwarta malam musa yayi kukan rashin mace irin hasana mace tagari
Inda ya nemi afuwar malam liman akan rashin waiwayarsu da baiyi ba
Malam liman yamai uzuri
Inda Ahmad tunda malam musa ya dauke shi ya makalkaleshi yaki bari ko sauke shine yayi
Malam musa ga abun farin ciki kuma ga akasinsa babu hasana amma hasana ta haifa masa yaro inda babu inda ya baro kamannin mahaifinsa sak
Ahmad ya kasance fari irin mai sirkin ja ja dinnan Yana da kyan shi gwargwado masha allah