Sashe 75
Tantiriya A Gidan Yari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Karar motoci suka ji da Uban kida suna zuwa gidan suka saki sautinsu,Mima tace ai Spark ne yayi aure sai abinda kuka gani Kuma,kannen Spark gaba daya kasa hakuri suka yi suka fice Compound kallo,Spark yasan sa Ido suka fito yi,dariya yayi kawai yace wai Dan uwanka ma a zamanin nan bayanka yake so ya Gani,nafi karfin ku yara bazan fado kasa ba always Spark On top ne,Driver ne ya bude masa kofa ya fito ya zaga ya budewa Amarya,Su Badia suna ta kallo tace Uhmmm kofar ma sai ya bude mata sai kace Yar me kudi,Kansa ya zura cikin motar Yana yiwa Naila rada yace,behave well nasan ke Oga ce,Naila kafa daya ta zuro,Kannen Spark harda leke suka hango farar kafa ta Sha lalle me kyau,Anam tace to ai ba fara ce me kyau ba,bakake ma akwai kyawawa wlh sunfi ma fararen kyau wasu,mu a fada mana haske duk danginmu ba baki,Hannunta Spark ya riko ta fito,Kanta a lullube ,Arham yace ai dole dai a bude mana fuskar, Spark Goggo ya mikawa Naila yace Amana,zuwa yamma za a dauke ta,Make shi Goggo tayi tace to fitsararre mu Kuma ayi ya damu? Yana murmushi yace kwana zakuyi mana kuga Abuja gobe a maidaku a jirgi,Goggo tace Dan nan ni bana son na shiga jirgi matukar ba Makkah zanje ba,kawai Dan fitina da asarar kudi a iya Nigeria zamu hau jirgi aradu baza muyi asara ba baza muyi Maka asarar kudi ba,Rayya tace Goggo wlh sai dai ke a Maida ke a mota sai cutar mu kuke yi da tuni a jirgi zamu zo mu koma,Yaya Spark a biya mana zamu hau mu,Spark ya tsaya a cikinsu sai surutunsu suke suna dariya da nishadi.
Yan uwansa duk mamaki ya kamasu mutumin da baya dagawa kowa kafa wai shine tare da Yan kauye suna wani hira da dariya,Badia tace su Spark an fado,Arham yace ni wlh ya birgeni na koma fan din Amarya ma,irin wannan nake nema Ido rufe,Kuma ma ai a kauye akwai Yan birni a birni ma akwai Yan kauye,idan Kuma kunce talakawa ne duk ba da arziki aka haifi kowa ba sannan babu me mutuwa a binne shi da dukiya,Kuma yanzu ta tashi daga Yar gidan talaka ta zama matar me kudi.
Ai kai Arham Dabba ne wa yake ta Kai cewar Badia,su Googo Naila ta rike tace muje ciki,suka tafi ciki a hankali tare da Amarya suna ta guda har cikin palon,Mubarak ne yace sai ka bamu kyautar mu da ka mana alkawari, Spark yace ai dai Kwa bari na shiga dakin Amarya gobe na baku cikin nishadi,Suka ce ba damuwa barshi sai goben maybe ma zaka fi bamu da yawa,yace wai nawa kuka ce ne? 50k muka ce,yace gobe Kuma ai sai 100k sabo da Ina Ango na sak,suka ce a barshi sai goben,suka juya da mota suka tafi har Spark din,Rafeeq kuwa Misam yake wa magana yace
Shi yasa na tsani Yan gidanmu wlh Sam basu da hankali,ji wannan sa Ido haka,Misam yace Kai kake saurarar su ma,wannan Badiar tafi kowa Munafunci sai kace ba yan uwa ba,Kai Ana dabbancin a gidan Nan wlh yanzu zasu saka baiwar Allah a gaba.
Rafeeq ya furta ai wannan daidai take dasu bana jinta Allah yasa idan suka fada musu bakar magana su rama.
Suna shiga tafkeken palon sai kamshi da Sanyi kawai ke tashi,kullum gidan da kida kamar yaran Arna,Palon ma kida suke ji a manyan Speakers sai da suka shiga sannan aka rage kidan sosai amma yana tashi kasa kasa,Goggo tace bayin Allah a kashe mana kida addua zamu yi,sai lokacin Anam ta kashe suka zauna da Amarya a Saman Carpet.
Naila Amarya anci gaba da kukan karya kasa kasa ta wani langabar da Kai anyi kasa da shi tana wasa da zoben hannunta me tsada da Spark ya saka mata a mota,Mima ma Jin Amarya tana kuka tace a ranta amma yarinyar nan muguwar criminal ce,Addua aka yi sosai sannan Maman Rafeeq da tafi dama dama a ciki itace ta yiwa Amarya nasiha,harda cewa Kinga dai shi dan dangi ne ato ki girmama masa yan uwa sannan kema su girmama ki,ayi hakuri da juna, tunda kika ce kinji kin gani kina so dole sai ayi hakuri,Mima tace ya zama dole kuwa,Goggo tace shine dai yaji ya gani yace Yana so Kuma,yo mace ke auren namiji ko namiji ne ke auren mace? Sadaki ya biya wuri na gugan wuri million guda sadaki sannan aka bashi,Yar masu shanu ce fa Wanda suka gaji arzikin dabbobi,Mima kirji ta dafe tace what? Serious fa? Million Daya? Goggo tace ai harda mota sabuwa gal tana can wajen Ubanta yayanta yana boris da ita a cikin gari, yo a dauki wannan zizar a sadaka ne,kallon wannan kawai yayi ai sai ya samu nutsuwa.
Kalleta fa baki ga kalarta bane?ai ba matar yara bace,ku godewa Allah ma da muka baku da wuri ba sai da muka bari ya kwanta a gadon asibiti ba kawo ruwa kawo ciyawa ana so ya farfado.
Dukkansu kallon kallo suka fara Goggo daga magana daya sai fadar magana take musu iri iri,Tani tace Kunga mu ku bamu waje sallah zamu yi,Mima tace Anam nuna musu yanda ake amfani da toilet din basu sani ba na sani,Goggo tace Kalli hakoran mu dukkan mu hakoran Makkah ne a bakunan mu har Yan matan nan su Rayya duk munje Makkah kasa me tsarki,har akwai wata toolet da bamu gani ba,ki tambaya kiji ko da kike zuwa Makkah bakya haduwa da Yan Fulani duk mune ko Ina,wlh babu wani abinda zaku yi bamu iya siya ba,a Daji kawai muke ne, ba rayuwa muka sa a gaba ba.
Mima tace da Haram ba,Goggo tace wlh yarinya ki kiyayeni ba a wasa da Fulani ba a kawo mana raini sai na sa a batar dake duk kudinki,mukus suka yi ba wacce ta sake ko tari sunji tsoro ko su Goggo suna daga cikin criminal basu sani ba,basu San Goggo barazana tayi musu ba kawai.
Tani tace a kawo muku kayan arziki irin wannan iyayenta su yarda da danku suna son Yar su amma suka dauka suka bashi ita Amana,mutum me daraja,yaro ya samu yarinya duniya guda zai samu ya moreta, yayi mata ciki, ta haifa Masa yara amma ku zauna Kuna fada mana magana,Baku da tsari Kai dan Allah ku canja tsarinku, ku canja hali, Sam halin ku baiyi ba,baku yi ba,Kun sire min wlh,nononta kadai aka bashi ya isheshi rayuwa bare a Kai ga lu'u lu'un,duk Yan dakin kunya suka ji Yan matan da samari suka shiga boye dariyarsu,Maman Rafeeq tace Dan Allah kuyi hakuri haka,Tani tace Allah to a dinga zaginmu a fakaice, yarinyar nan fa ba nonon jaka gareta ba bana saniya bane na mutum ne,yau na tabbata bazai bari ta sake ba,Kuma kawai an baku ita kwasha kwasha shine ake zagin mu,jarababben Dan naku ma da naci, in banda kwarzaba me zaiyi yarinya Kun jawo mana asarar kudi sai mun dinga kawo mata magani kar ya lalata ta,Lateefa tace to kuyi hakuri ku taso muje kuyi Alwala.
Maman Rafeeq Hannun Amarya ta rike taji Laushi tace a ranta ba abin kayi magana ba ayi Maka cari,bari na fada a raina laushin nan kamar bata aikin wahala.
Toilet Lateefa ta kaisu cikin wani bedroom hadadde ta shimfida musu Sallaya manya da yawa sannan ta fito suka bar musu dakin suka koma Palo suka fara gulmar rashin mutuncin dangin Amarya,Mima tace Kinga Goggo nan kamar zata dake ni.
Anam tace Kuma da sai kuyi shuru, baku kyauta ba wlh ai ko ba komai suci darajar Spark yanzu sai sunyi ta gulmar a can,Mima tace who cares? suna ta gulma,Arham su mazan jira kawai suke a bude musu Amarya su ganta,Mima tace wannan naci da yawa yake wai gidan Spark din ne Baku sani ba,ba sai kuje ku ganta ba a can,wannan fa taron mata ne,Kun samu a gaba,amma sabo da basa Jin maganar iyayensu kin tashi suka yi,funfurus suka yi a wajen sun zauna a kujeru wasu kuma a kasa.
Su Goggo Sallah suka kasaru ta azahar,Naila ma tayi harda wanke fuska da sabulu tana idar da Sallah ta fara shafa powder tana gyarawa,tayi Yar make up dinta sama sama tayi kyau sosai ta sake shafa turaruka har Jikin kayanta da mayafin sannan Goggo tace ni wai ya naga idon ba alamar anyi kuka ne? Naila tace na rantse kuka na dinga yi na gaske fa,Abbana na tuna ta sake kebe baki,Goggo tace to ya isa kinyi kukanki,tace yanzu karki sake rufe fuska kyale shegu su ganki ai ba mummuna bace,kawar Umma tace yawwa ta Dora mayafin a kanta ta bar fuskar a waje, suna zaune sai ga Anam ta shugo musu da abinci ta ajiye,ta fice da sauri tace na ganta wallahi ta hadu,Badia tace tayi dariya Kinga hakoranta? Anam tace a'a,to rufe mana baki yanzu haka karyayyen hakori gareta,Badia ma ta dauki wani abincin ta shigar musu da shi Dan ta ga Amarya,taci sa'a Naila na magana ta ganta taga hakora masu kyau reras,sai ta fito tace na tabbatar ba karya.
Mima tace ahh Dan fa kyakyawa fa kyakyawa ce gaskiya, magana ta Allah tana da kyau wlh ko ita zata yi kanta baza ta yi haka ba amma fa ba kyan hali bata da kunya,Anam tace bari na sake Kai ruwan nan na ganta again,ta dauka kenan Arham ya kwace wai shi zai Kai,Mima tace je kice su fito Palo zasu fi sakewa,amma ni kar su bata mana dakin yara su fito ato.
Amma kin San masifarsu kice su fito zasu fi sake wa.
Anam ta shiga tace Amaryar mu ku fito Palo wai zaku fi sakewa,suka mike,kawar Umma a ciki tace wlh su Goggo Kun kwato mana yanci sosai,gashi sai lallaba mu akeyi ana Jin tsoron mu,Goggo tace ai ba a bari yanzu Kai ya kulle, ke kyaleni nan zuwa na Makkah sau takwas, a waye nake karrr ba me daga min Kai,wacce shinkafa ce banci a Makkah ba,wanne tayal (tiles)ne ban gani ba,su Tani wlh duk sun je yafi sau uku,haka su Rayya duk an biya musu sun je,shi kanshi Hashimu Baban Naila tun Yana saurayi mahaifinsa ya biya Masa yaje har sau biyu,Umman Naila kanta zuwanta biyu Makkah.
Yan uwansa duk mamaki ya kamasu mutumin da baya dagawa kowa kafa wai shine tare da Yan kauye suna wani hira da dariya,Badia tace su Spark an fado,Arham yace ni wlh ya birgeni na koma fan din Amarya ma,irin wannan nake nema Ido rufe,Kuma ma ai a kauye akwai Yan birni a birni ma akwai Yan kauye,idan Kuma kunce talakawa ne duk ba da arziki aka haifi kowa ba sannan babu me mutuwa a binne shi da dukiya,Kuma yanzu ta tashi daga Yar gidan talaka ta zama matar me kudi.
Ai kai Arham Dabba ne wa yake ta Kai cewar Badia,su Googo Naila ta rike tace muje ciki,suka tafi ciki a hankali tare da Amarya suna ta guda har cikin palon,Mubarak ne yace sai ka bamu kyautar mu da ka mana alkawari, Spark yace ai dai Kwa bari na shiga dakin Amarya gobe na baku cikin nishadi,Suka ce ba damuwa barshi sai goben maybe ma zaka fi bamu da yawa,yace wai nawa kuka ce ne? 50k muka ce,yace gobe Kuma ai sai 100k sabo da Ina Ango na sak,suka ce a barshi sai goben,suka juya da mota suka tafi har Spark din,Rafeeq kuwa Misam yake wa magana yace
Shi yasa na tsani Yan gidanmu wlh Sam basu da hankali,ji wannan sa Ido haka,Misam yace Kai kake saurarar su ma,wannan Badiar tafi kowa Munafunci sai kace ba yan uwa ba,Kai Ana dabbancin a gidan Nan wlh yanzu zasu saka baiwar Allah a gaba.
Rafeeq ya furta ai wannan daidai take dasu bana jinta Allah yasa idan suka fada musu bakar magana su rama.
Suna shiga tafkeken palon sai kamshi da Sanyi kawai ke tashi,kullum gidan da kida kamar yaran Arna,Palon ma kida suke ji a manyan Speakers sai da suka shiga sannan aka rage kidan sosai amma yana tashi kasa kasa,Goggo tace bayin Allah a kashe mana kida addua zamu yi,sai lokacin Anam ta kashe suka zauna da Amarya a Saman Carpet.
Naila Amarya anci gaba da kukan karya kasa kasa ta wani langabar da Kai anyi kasa da shi tana wasa da zoben hannunta me tsada da Spark ya saka mata a mota,Mima ma Jin Amarya tana kuka tace a ranta amma yarinyar nan muguwar criminal ce,Addua aka yi sosai sannan Maman Rafeeq da tafi dama dama a ciki itace ta yiwa Amarya nasiha,harda cewa Kinga dai shi dan dangi ne ato ki girmama masa yan uwa sannan kema su girmama ki,ayi hakuri da juna, tunda kika ce kinji kin gani kina so dole sai ayi hakuri,Mima tace ya zama dole kuwa,Goggo tace shine dai yaji ya gani yace Yana so Kuma,yo mace ke auren namiji ko namiji ne ke auren mace? Sadaki ya biya wuri na gugan wuri million guda sadaki sannan aka bashi,Yar masu shanu ce fa Wanda suka gaji arzikin dabbobi,Mima kirji ta dafe tace what? Serious fa? Million Daya? Goggo tace ai harda mota sabuwa gal tana can wajen Ubanta yayanta yana boris da ita a cikin gari, yo a dauki wannan zizar a sadaka ne,kallon wannan kawai yayi ai sai ya samu nutsuwa.
Kalleta fa baki ga kalarta bane?ai ba matar yara bace,ku godewa Allah ma da muka baku da wuri ba sai da muka bari ya kwanta a gadon asibiti ba kawo ruwa kawo ciyawa ana so ya farfado.
Dukkansu kallon kallo suka fara Goggo daga magana daya sai fadar magana take musu iri iri,Tani tace Kunga mu ku bamu waje sallah zamu yi,Mima tace Anam nuna musu yanda ake amfani da toilet din basu sani ba na sani,Goggo tace Kalli hakoran mu dukkan mu hakoran Makkah ne a bakunan mu har Yan matan nan su Rayya duk munje Makkah kasa me tsarki,har akwai wata toolet da bamu gani ba,ki tambaya kiji ko da kike zuwa Makkah bakya haduwa da Yan Fulani duk mune ko Ina,wlh babu wani abinda zaku yi bamu iya siya ba,a Daji kawai muke ne, ba rayuwa muka sa a gaba ba.
Mima tace da Haram ba,Goggo tace wlh yarinya ki kiyayeni ba a wasa da Fulani ba a kawo mana raini sai na sa a batar dake duk kudinki,mukus suka yi ba wacce ta sake ko tari sunji tsoro ko su Goggo suna daga cikin criminal basu sani ba,basu San Goggo barazana tayi musu ba kawai.
Tani tace a kawo muku kayan arziki irin wannan iyayenta su yarda da danku suna son Yar su amma suka dauka suka bashi ita Amana,mutum me daraja,yaro ya samu yarinya duniya guda zai samu ya moreta, yayi mata ciki, ta haifa Masa yara amma ku zauna Kuna fada mana magana,Baku da tsari Kai dan Allah ku canja tsarinku, ku canja hali, Sam halin ku baiyi ba,baku yi ba,Kun sire min wlh,nononta kadai aka bashi ya isheshi rayuwa bare a Kai ga lu'u lu'un,duk Yan dakin kunya suka ji Yan matan da samari suka shiga boye dariyarsu,Maman Rafeeq tace Dan Allah kuyi hakuri haka,Tani tace Allah to a dinga zaginmu a fakaice, yarinyar nan fa ba nonon jaka gareta ba bana saniya bane na mutum ne,yau na tabbata bazai bari ta sake ba,Kuma kawai an baku ita kwasha kwasha shine ake zagin mu,jarababben Dan naku ma da naci, in banda kwarzaba me zaiyi yarinya Kun jawo mana asarar kudi sai mun dinga kawo mata magani kar ya lalata ta,Lateefa tace to kuyi hakuri ku taso muje kuyi Alwala.
Maman Rafeeq Hannun Amarya ta rike taji Laushi tace a ranta ba abin kayi magana ba ayi Maka cari,bari na fada a raina laushin nan kamar bata aikin wahala.
Toilet Lateefa ta kaisu cikin wani bedroom hadadde ta shimfida musu Sallaya manya da yawa sannan ta fito suka bar musu dakin suka koma Palo suka fara gulmar rashin mutuncin dangin Amarya,Mima tace Kinga Goggo nan kamar zata dake ni.
Anam tace Kuma da sai kuyi shuru, baku kyauta ba wlh ai ko ba komai suci darajar Spark yanzu sai sunyi ta gulmar a can,Mima tace who cares? suna ta gulma,Arham su mazan jira kawai suke a bude musu Amarya su ganta,Mima tace wannan naci da yawa yake wai gidan Spark din ne Baku sani ba,ba sai kuje ku ganta ba a can,wannan fa taron mata ne,Kun samu a gaba,amma sabo da basa Jin maganar iyayensu kin tashi suka yi,funfurus suka yi a wajen sun zauna a kujeru wasu kuma a kasa.
Su Goggo Sallah suka kasaru ta azahar,Naila ma tayi harda wanke fuska da sabulu tana idar da Sallah ta fara shafa powder tana gyarawa,tayi Yar make up dinta sama sama tayi kyau sosai ta sake shafa turaruka har Jikin kayanta da mayafin sannan Goggo tace ni wai ya naga idon ba alamar anyi kuka ne? Naila tace na rantse kuka na dinga yi na gaske fa,Abbana na tuna ta sake kebe baki,Goggo tace to ya isa kinyi kukanki,tace yanzu karki sake rufe fuska kyale shegu su ganki ai ba mummuna bace,kawar Umma tace yawwa ta Dora mayafin a kanta ta bar fuskar a waje, suna zaune sai ga Anam ta shugo musu da abinci ta ajiye,ta fice da sauri tace na ganta wallahi ta hadu,Badia tace tayi dariya Kinga hakoranta? Anam tace a'a,to rufe mana baki yanzu haka karyayyen hakori gareta,Badia ma ta dauki wani abincin ta shigar musu da shi Dan ta ga Amarya,taci sa'a Naila na magana ta ganta taga hakora masu kyau reras,sai ta fito tace na tabbatar ba karya.
Mima tace ahh Dan fa kyakyawa fa kyakyawa ce gaskiya, magana ta Allah tana da kyau wlh ko ita zata yi kanta baza ta yi haka ba amma fa ba kyan hali bata da kunya,Anam tace bari na sake Kai ruwan nan na ganta again,ta dauka kenan Arham ya kwace wai shi zai Kai,Mima tace je kice su fito Palo zasu fi sakewa,amma ni kar su bata mana dakin yara su fito ato.
Amma kin San masifarsu kice su fito zasu fi sake wa.
Anam ta shiga tace Amaryar mu ku fito Palo wai zaku fi sakewa,suka mike,kawar Umma a ciki tace wlh su Goggo Kun kwato mana yanci sosai,gashi sai lallaba mu akeyi ana Jin tsoron mu,Goggo tace ai ba a bari yanzu Kai ya kulle, ke kyaleni nan zuwa na Makkah sau takwas, a waye nake karrr ba me daga min Kai,wacce shinkafa ce banci a Makkah ba,wanne tayal (tiles)ne ban gani ba,su Tani wlh duk sun je yafi sau uku,haka su Rayya duk an biya musu sun je,shi kanshi Hashimu Baban Naila tun Yana saurayi mahaifinsa ya biya Masa yaje har sau biyu,Umman Naila kanta zuwanta biyu Makkah.