Sashe 37
Tantiriya A Gidan Yari Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Chikar Gayu sai da aka dan yawata da ita taga gari,tace to kaini tasha aka kaita tashar mota,motar Kaduna ta shiga har ta shiga ciki tace na fasa katsina zanje yes Katsina zani na fara zuwa wajen Uwata tukun na dawo naje Kaduna din gwara na fara cin uban me unguwar layinmu sannan naje gidan Ubana,fitowa tayi ta canja tasha ta hau motar Katsina suka ware birnin katsina, bayan awanni ta sauka a motar ta biya me napep yayi parking a kofar gidan me unguwar Layin,taci sa'a a waje ta ganshi,a gabansa ta tsaya,ya zaci fatalwa ce ya ja da baya Yana salati harda faduwa a kasa Yana Nuna Chikar Gayu da hannu, Chikar gayu tace nice ba Aljana bace Dan gyatumin ubanka,ai dama nace zan fito sharrin daka kulla min to na fito,Mikewa tsaye yayi yace karya kike gudowa kika yi Kuma sai na sake kiran police sun Maida ke,shegiya Yar iska haihuwar kwararo.
Ubanka aka Haifa a kwaroro cewar chika,me unguwa ya jawo sandarsa wai zai kwalawa Chikar gayu ya zaci a baya ne sanda tana karama, Chikar gayu taci kwalarsa dama gashi wani Dan figigi ta yanka Masa Mari,Mutane suka taru a wajen ana labari Chikar gayu ta dawo, Me unguwa ya dafe kumatunsa yace ni kika mara? tana rike da kwalar me unguwan ta lakace Masa hanci tace an mareka,baka ga na girma ba to na balaga dattijon banza, ta zaro Masa idanu tare da furta balaga ce ta jawo, na rika na tatira na tumbatsa, tayi fatali da rawaninsa ta shake shi sosai,mutane suka taho suna cewa dan Allah Chikar gayu sake shi kina mace a unguwar Nan kowa yasan ke saliha ce,Chikar gayu tace duk Wanda ya rabamu Allah ya isa,kar Wanda ya sake ya rabamu wlh duk Wanda ya rabamu iyalansa ma sun shiga uku,mutane suna ta mamaki, wani a ciki yace Chikar gayu da a baya ko yatsa aka sa mata baza ta iya cizawa ba ita dai barta da gayu.
Chikar Gayu tace to yanzu gartsa yatsan zanyi,mutum ya sa min yatsan a baki ya Gani idan ban gartsa Masa cizo ba kafira nake, koma na fille yatsan,Kuma wallahi fada bai mutu ba bari naje na huta zanzo har gida sai na hanaka Shan ruwa a layin Nan,bari naje naga dangi zan dawo a Yar dabata zanzo,Me Unguwa yace sai na daure ki,ta hankada shi tana haki tayi cikin gidan Me unguwa mata suna girkinsu a murhu sai kawai Ganin Chikar gayu suka yi ta daki tukunyar tayi foli foli da ita abincin Dake ciki ya juye a kasa,Mata da yara sai kowacce ta nufi dakinta ta rufe,Chikar gayu ta duba kajin gidan gonar me Unguwa da yawa a katon cage Yana kiwo ta bude su tare da Koro su waje tace duk ku fice Dan ubanku,sai Kaji suka yo waje tatatata suka yo waje suna kuka kuyat... kuyat...kut..kutt..kut,ta kwance akuyoyin me unguwa ta Koro su waje kofar gida suma,fitowa tayi ta ce zan dawo ne sai ka fada min abinda na Maka kayi min sharri zan dawo ne,gashi Nan kullum tsiya tsiya da kai kana cikin birni kana kiwon akuyoyi gidanka kamar na kauye, daga yanzu gaba ni da ku har yarana da jikokina da iyali na,Me unguwa Yana dafe da kumatu Inda yasha Mari yace sai naga bayanki,idan har Ina sallah to ni Kuma sai na nuna Maka banje gidan yari a banza ba,gidan yarin da kayi sanadin shigata to Kai na shigarwa,idan ba Kai asararre bane muna alaka da Kai ta jini amma Kaine munafuki ko,zaka ga tantirin iskanci me maiko.
gidansu ta nufa ana ta cewa ga Chikar Gayu ta fito ga Chikar gayu.
Bayan kwana uku Beauty ma Allah yayi tayi sallama da kowa itama,ranar da Beauty zata fita aka kawo wata budurwar,Beauty tace yanzu duk ba kuka kike ba sai nan gaba zaki fada,ki saki ranki ki tsula tsiyarki Yar nan duk Nan mu da kika ganmu tantirai ne,mu da kanmu mun san ta wani bangaren ba kyau bama ji gidan masu laifi ai gidan tatirarrun Yan iska ne,budurwar ta Kalli Beauty kawai tana Jin wani kunya,Beauty ta Dora hannu a Kai tare da furta Laaaaaaaa Kunga kunya take ji cewar Beauty,su Azima suka ce da sauranta lallai,ke a Nan ba kunya Dan ubanki wallahi ki warware ko kici duka a gidan nan ba a mana kunya yanzu kyaji jiki cewar Azima da wata dattijuwa Yar duniya.
A ranar da yamma Beauty ta fita taje Wajen signing,ma'aikatan suna tayata murna,Beauty baki yaki rufuwa kowa ta gani sai gaisuwa Ina Kwana,idan ya amsa ma sai tace Dan Allah mu sake gaisawa Kuma gaisuwar da wani Shoky take kwasota ta duka ta kwaso tace Ina Kwana ta watsawa mutum shokynta,dariya ta dinga basu, Daddynta da kansa yazo daukanta suna ta murna ta shiga hadaddiyar mota suka tafi gida.
Naila bata San Spark shima Yana Shirin fita ba sunyi muguwar shakuwa kullum suna tare, tare suke yin komai Kuma Bai nuna yasan ba mace bace, Ranar da za a tafi dashi kotu ranar ya samu Naila a part dinsa tana zaune tana Shan lemo da cake,ya fito cikin shirinsa ,a gefe ya zauna a kusa da ita yace Jamilu zanje kotu,gaskiya ta bayyana akan sharrin da aka min
Naila zumbur ta mike tsaya tayi rau rau zata yi kuka,shima tsayen ya mike tare da rike hannayenta biyu ya bata labarin me Mama tayi, ya fada mata halin da ake ciki a nutse,ai Jamilu sai kuka sai kurruwa da burburwa,kasa ta sulale tayi zaman Yan bori tana tumami a kasa wayyo Allah na shiga uku kowa sai ficewa yake Yana barina,Ina zan sa kaina Beauty ta fita itama gashi kaima, hawaye rabe rabe a fuskarta sharkaf tana kuka harda shidewa tana furta way way way way ihihihihi wayyo zuciyata ta dafe kirjinta tana uban kuka,tausayi ta bawa Spark yace bance fa zan tafi na barka ba ka daina kuka,ya tasheta tsaye ta mike da kyar tana tangadi kamar Yar giya,rungumeta yayi a hankali a kirjinsa tana ta kuka Yana bubbuga bayanta a hankali,a nutse yasa hannayensa masu taushi tare da tallafo fuskarta ya shiga goge mata hawayenta amma wasu bulbulowa suke kawai, hannu biyu ta sa ta riko rigarsa gaban kirjinsa tayi baya da kanta tana rasgas uban kuka, yace amma da nasan haza zaka min bazan fada Maka ba,kayi shuru Jamilu,Naila tace sunana Naila ni ba namiji bane wlh, Spark ya kalleta sosai yayi dariya yace ai na sani tuntuni, kawai kallonki nake,tana shesheka ta furta yaushe ka sani a Ina? murmushi ya saki yace nasan kai mace ne ba tun yanzu ba sunanki ne kawai ban sani ba,Ashe sunanki Naila nice name,Naila duk a rude take tace na cire abinda nake daure kirjinta da shi taba kaji ni Macece,Spark yace ni da na kalla wai with my two Kworo Kworo eye,kallo fa nayi ni Kinga gani ya kori ji,ki bari na dawo zamuyi zancen,kici gaba da zama a jamilunki please kafin na fitar Dake,ai kace baza ka tafi ba,idan ban tafi ba taya zan fitar dake to? Naila ta sake fashewa da kuka,yace na fasa bazan tafi ba zan zauna,da kyar ya lallabata tayi shuru,idonta yayi jajir har ya fita tana hawaye.
Spark bayan an kaishi kotu da matakan tsaro a motar gidan yarin,Mima ya fara gani ya dauke kansa,Mummy ya gani wajenta ya tsaya ya gaisheta ta rungume shi tace Dana I miss you,ya furta me too,Rafeeq ya mikawa Hannu suka tafa da Kamal shima suka gaisa,bayan duk wani bincike kotu ta wanke Spark tas bashi da hannu a kisan Asmau sannan Mama Kuma an yanke mata hukuncin daurin rai da rai,tana ta kuka,yaranta suma sai kuka suke na bakin ciki,ana fitowa daga kotu wai Spark ya bisu su tafi,Spark yayiwa Wanda suka zo dashi Yana da abubuwan yi a ciki akwai kwangilar gyaran kofofi da zai musu shi lallai a Maida shi ciki sai ya gama zai fito,Har kudi ya basu tun a mota,Su Mummy suna kallo Spark yabi motar gidan yari suka koma ciki da shi, to da uwar kudinsa.
Naila tana palonsa ta zuba tagumi tana ta wani sabon hawayen Spark ya shugo yace au kukan kike yi dama? Naila tana kuka tace nidai ka zauna karka tafi,Spark yace Tantiriyata ke da na sanki da juriya,jajirtacciyar ce ke fa,kici gaba da fitowarki a Jamilunki karki sake a gano har na samu ki fita please,Naila tace to kawai yace ko ke fa,Baki murmushi ba? Harararsa tayi tana goge hawaye,da kafadarsa ya Dan biki tata kafadar kadan,kansa ya dora a kafadarta yana karewa fuskarta kallo,janye jikinta tayi da sauri ya koma zai kwanta a cinyarta ta mike ta canja kujera,dariya yayi yace ki dakko hijab dinki ki daina boye boyen sallah,kamar an dinke bakin Tantiriya,tunda Spark zai bar gidan shike nan Kuma ta rasa sukuni,Bata kazar kazar da surutu ko wani Abu,Su kansu a gidan yarin ana mamakin Jamilu ya daina walwala Sam,Yar dariyar da yake bawa mutane ya daina an rasa dalili,su Malam Sharu har tambayar Jamilu suka yi wai meke damunka ne Jamilu? Yace ba komai kawai,Su Dan Indo,Goje sunyi sunyi suji meke damun Terror Jamilu amma basu gano komai ba.
Ubanka aka Haifa a kwaroro cewar chika,me unguwa ya jawo sandarsa wai zai kwalawa Chikar gayu ya zaci a baya ne sanda tana karama, Chikar gayu taci kwalarsa dama gashi wani Dan figigi ta yanka Masa Mari,Mutane suka taru a wajen ana labari Chikar gayu ta dawo, Me unguwa ya dafe kumatunsa yace ni kika mara? tana rike da kwalar me unguwan ta lakace Masa hanci tace an mareka,baka ga na girma ba to na balaga dattijon banza, ta zaro Masa idanu tare da furta balaga ce ta jawo, na rika na tatira na tumbatsa, tayi fatali da rawaninsa ta shake shi sosai,mutane suka taho suna cewa dan Allah Chikar gayu sake shi kina mace a unguwar Nan kowa yasan ke saliha ce,Chikar gayu tace duk Wanda ya rabamu Allah ya isa,kar Wanda ya sake ya rabamu wlh duk Wanda ya rabamu iyalansa ma sun shiga uku,mutane suna ta mamaki, wani a ciki yace Chikar gayu da a baya ko yatsa aka sa mata baza ta iya cizawa ba ita dai barta da gayu.
Chikar Gayu tace to yanzu gartsa yatsan zanyi,mutum ya sa min yatsan a baki ya Gani idan ban gartsa Masa cizo ba kafira nake, koma na fille yatsan,Kuma wallahi fada bai mutu ba bari naje na huta zanzo har gida sai na hanaka Shan ruwa a layin Nan,bari naje naga dangi zan dawo a Yar dabata zanzo,Me Unguwa yace sai na daure ki,ta hankada shi tana haki tayi cikin gidan Me unguwa mata suna girkinsu a murhu sai kawai Ganin Chikar gayu suka yi ta daki tukunyar tayi foli foli da ita abincin Dake ciki ya juye a kasa,Mata da yara sai kowacce ta nufi dakinta ta rufe,Chikar gayu ta duba kajin gidan gonar me Unguwa da yawa a katon cage Yana kiwo ta bude su tare da Koro su waje tace duk ku fice Dan ubanku,sai Kaji suka yo waje tatatata suka yo waje suna kuka kuyat... kuyat...kut..kutt..kut,ta kwance akuyoyin me unguwa ta Koro su waje kofar gida suma,fitowa tayi ta ce zan dawo ne sai ka fada min abinda na Maka kayi min sharri zan dawo ne,gashi Nan kullum tsiya tsiya da kai kana cikin birni kana kiwon akuyoyi gidanka kamar na kauye, daga yanzu gaba ni da ku har yarana da jikokina da iyali na,Me unguwa Yana dafe da kumatu Inda yasha Mari yace sai naga bayanki,idan har Ina sallah to ni Kuma sai na nuna Maka banje gidan yari a banza ba,gidan yarin da kayi sanadin shigata to Kai na shigarwa,idan ba Kai asararre bane muna alaka da Kai ta jini amma Kaine munafuki ko,zaka ga tantirin iskanci me maiko.
gidansu ta nufa ana ta cewa ga Chikar Gayu ta fito ga Chikar gayu.
Bayan kwana uku Beauty ma Allah yayi tayi sallama da kowa itama,ranar da Beauty zata fita aka kawo wata budurwar,Beauty tace yanzu duk ba kuka kike ba sai nan gaba zaki fada,ki saki ranki ki tsula tsiyarki Yar nan duk Nan mu da kika ganmu tantirai ne,mu da kanmu mun san ta wani bangaren ba kyau bama ji gidan masu laifi ai gidan tatirarrun Yan iska ne,budurwar ta Kalli Beauty kawai tana Jin wani kunya,Beauty ta Dora hannu a Kai tare da furta Laaaaaaaa Kunga kunya take ji cewar Beauty,su Azima suka ce da sauranta lallai,ke a Nan ba kunya Dan ubanki wallahi ki warware ko kici duka a gidan nan ba a mana kunya yanzu kyaji jiki cewar Azima da wata dattijuwa Yar duniya.
A ranar da yamma Beauty ta fita taje Wajen signing,ma'aikatan suna tayata murna,Beauty baki yaki rufuwa kowa ta gani sai gaisuwa Ina Kwana,idan ya amsa ma sai tace Dan Allah mu sake gaisawa Kuma gaisuwar da wani Shoky take kwasota ta duka ta kwaso tace Ina Kwana ta watsawa mutum shokynta,dariya ta dinga basu, Daddynta da kansa yazo daukanta suna ta murna ta shiga hadaddiyar mota suka tafi gida.
Naila bata San Spark shima Yana Shirin fita ba sunyi muguwar shakuwa kullum suna tare, tare suke yin komai Kuma Bai nuna yasan ba mace bace, Ranar da za a tafi dashi kotu ranar ya samu Naila a part dinsa tana zaune tana Shan lemo da cake,ya fito cikin shirinsa ,a gefe ya zauna a kusa da ita yace Jamilu zanje kotu,gaskiya ta bayyana akan sharrin da aka min
Naila zumbur ta mike tsaya tayi rau rau zata yi kuka,shima tsayen ya mike tare da rike hannayenta biyu ya bata labarin me Mama tayi, ya fada mata halin da ake ciki a nutse,ai Jamilu sai kuka sai kurruwa da burburwa,kasa ta sulale tayi zaman Yan bori tana tumami a kasa wayyo Allah na shiga uku kowa sai ficewa yake Yana barina,Ina zan sa kaina Beauty ta fita itama gashi kaima, hawaye rabe rabe a fuskarta sharkaf tana kuka harda shidewa tana furta way way way way ihihihihi wayyo zuciyata ta dafe kirjinta tana uban kuka,tausayi ta bawa Spark yace bance fa zan tafi na barka ba ka daina kuka,ya tasheta tsaye ta mike da kyar tana tangadi kamar Yar giya,rungumeta yayi a hankali a kirjinsa tana ta kuka Yana bubbuga bayanta a hankali,a nutse yasa hannayensa masu taushi tare da tallafo fuskarta ya shiga goge mata hawayenta amma wasu bulbulowa suke kawai, hannu biyu ta sa ta riko rigarsa gaban kirjinsa tayi baya da kanta tana rasgas uban kuka, yace amma da nasan haza zaka min bazan fada Maka ba,kayi shuru Jamilu,Naila tace sunana Naila ni ba namiji bane wlh, Spark ya kalleta sosai yayi dariya yace ai na sani tuntuni, kawai kallonki nake,tana shesheka ta furta yaushe ka sani a Ina? murmushi ya saki yace nasan kai mace ne ba tun yanzu ba sunanki ne kawai ban sani ba,Ashe sunanki Naila nice name,Naila duk a rude take tace na cire abinda nake daure kirjinta da shi taba kaji ni Macece,Spark yace ni da na kalla wai with my two Kworo Kworo eye,kallo fa nayi ni Kinga gani ya kori ji,ki bari na dawo zamuyi zancen,kici gaba da zama a jamilunki please kafin na fitar Dake,ai kace baza ka tafi ba,idan ban tafi ba taya zan fitar dake to? Naila ta sake fashewa da kuka,yace na fasa bazan tafi ba zan zauna,da kyar ya lallabata tayi shuru,idonta yayi jajir har ya fita tana hawaye.
Spark bayan an kaishi kotu da matakan tsaro a motar gidan yarin,Mima ya fara gani ya dauke kansa,Mummy ya gani wajenta ya tsaya ya gaisheta ta rungume shi tace Dana I miss you,ya furta me too,Rafeeq ya mikawa Hannu suka tafa da Kamal shima suka gaisa,bayan duk wani bincike kotu ta wanke Spark tas bashi da hannu a kisan Asmau sannan Mama Kuma an yanke mata hukuncin daurin rai da rai,tana ta kuka,yaranta suma sai kuka suke na bakin ciki,ana fitowa daga kotu wai Spark ya bisu su tafi,Spark yayiwa Wanda suka zo dashi Yana da abubuwan yi a ciki akwai kwangilar gyaran kofofi da zai musu shi lallai a Maida shi ciki sai ya gama zai fito,Har kudi ya basu tun a mota,Su Mummy suna kallo Spark yabi motar gidan yari suka koma ciki da shi, to da uwar kudinsa.
Naila tana palonsa ta zuba tagumi tana ta wani sabon hawayen Spark ya shugo yace au kukan kike yi dama? Naila tana kuka tace nidai ka zauna karka tafi,Spark yace Tantiriyata ke da na sanki da juriya,jajirtacciyar ce ke fa,kici gaba da fitowarki a Jamilunki karki sake a gano har na samu ki fita please,Naila tace to kawai yace ko ke fa,Baki murmushi ba? Harararsa tayi tana goge hawaye,da kafadarsa ya Dan biki tata kafadar kadan,kansa ya dora a kafadarta yana karewa fuskarta kallo,janye jikinta tayi da sauri ya koma zai kwanta a cinyarta ta mike ta canja kujera,dariya yayi yace ki dakko hijab dinki ki daina boye boyen sallah,kamar an dinke bakin Tantiriya,tunda Spark zai bar gidan shike nan Kuma ta rasa sukuni,Bata kazar kazar da surutu ko wani Abu,Su kansu a gidan yarin ana mamakin Jamilu ya daina walwala Sam,Yar dariyar da yake bawa mutane ya daina an rasa dalili,su Malam Sharu har tambayar Jamilu suka yi wai meke damunka ne Jamilu? Yace ba komai kawai,Su Dan Indo,Goje sunyi sunyi suji meke damun Terror Jamilu amma basu gano komai ba.