Sashe 65
Tantiriya A Gidan Yari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Suna fita suka dinga labari wlh kirki ne da shi Ashe suna ta bawa Umma labari ai har Hira suka yi dama Yana da magana,har wasa ya dinga yi mana wlh akwai kirki, a farko mun zaci bashi da mutunci mun ga Yana gadara da takama Ashe shima Tantiri ne a nutse yake magana baza kice shi ya fada ba,Spark fitowa yayi zai tafi Naila tazo zata raka shi ya Dan matsa nesa da ita kadan yace kar ace bani da kunya a gidan surukai,suna zuwa kofar gida yace koma gida,karki min make up lokacin dinner kuma na tsani wannan kwalliyar da mata keyi,duk kyanta Bata birgeni Sam,kiyi da kanki kawai ni bana son make up duk ta canjawa mutum kamanni,Naila tace to na huta nima.
Ana ta Shirin Dinner da yamma Chikar gayu itace babbar kawar Beauty an dauki wanka kamar me,Amarya kuwa tana wajen make Up tare da wasu kawayen ta Sha farin bride material me tsadar gaske an mata wata gown me kyan gaske ta zaratan amare,an nada mata dauri da silver gogoro, takalmi Silver jaka ma haka,make up din tayi kyau an dora mata mayafin amare a Kanta sharashara sai walwali take ta ko Ina,Ango Yasa Shadda Yar ubansu Silver kalar takalmi da jakarta da gogoro.
Su Chika duk anci ankon Leshi me kyan gaske Blue and white,kawaye an Sha wanka sunyi gayya kamar me, Yan mata tamfatsa tamfatsa sunzo duk kawayensu ne yawanci daga gidan yari suka fito,Kamal ne zaizo shima sabo da abokinsa Spark ai kuwa Rafeeq yace akwai dinner? akace ae yace ko banza na Kalli mata mu tafi Kamaluddeen,Kamal yace Allah ya shiryeka Kai ba Dan iska ba sai son kallon mata? Rafeeq yace ko banza ai na kashe kwarkwatar idona muje,Da yamma suka dira,Rafeeq lokaci nayi yafi uban kowa saurin shiryawa yace Kano sai da shadda ya fito cikin shadda me kyau wata ita ba milk ba ita Kuma ba ruwan kasa ba,suna dakin Spark shi da Kamal,Kamal yace gaskiya kayi kyau Rafeeq Allah kawo babban rabo,yayi shuru kamar Salihi,Mayen mata Misam ne Allah yayi ya kira wayar Rafeeq,kana Ina? Rafeeq yace dinner Yan mata ne iya kallonka,Misam yace amma baku da mutunci shine ko ku fada min ni shugaban mata guda,Ba komai ai gobe ma matan zasu taru ko? Rafeeq yace ai ance akwai walima mata da Maza za ayi wa'azin zama da iyali lafiya,Misam yace tab zanzo naji Ina jin wa'azi Ina zabar nawa ya nawa.
Ana ta tafiya wurin dinner dangin ango dana Amarya,Abba ya shugo gidan Yana tarkata kan Yan mata danginsu ku fita ku tafi aje ayi rayuwa Allah ya sanya Alkhairi,Wata babbar mace me suna Tani tace zanje nima nayi kallo, Abba yace Tani gidan uban wa zaki? ki batawa yara show sunyi gayu aga irinki kamar wata Tsohuwar mota hayis ba Inda zaki ai zubar da girma ne,Kubra ta cakare taci wani material an mata make up,kyan da tayi ya Isa,Dake Kubra ce sai Abba yace Yar Inna an fito? Ko ranar bikinmu baki kyau haka ba,idan an girma asan an girma,Kuma wallahi sai kika yi kyau kamar kiyi ta zama a haka,ai da bazan sake fita wajen sana'a ba gwara kullum na dinga kallonki.
Umma tace wai baza kaje bane? Abba yace a'a haka kawai naje na zubarwa da yarana mutunci wlh tsab naji kida zan taka, Kinga ai girma ya Fadi kuje ku dai kawo Basma nayi miki rainonta,tace madararta tana dakina Jikin bed,yace to ya karbi Basma Umma ta fita ta tafi tare dasu Hajiya Tagwadas ansha gayu.
Naila ta Sha anko itama ta cakare ta zuba kyau kamar a saceta kawai Spark take jira,ba a dade ba yazo a mota ana tuka shi ya hakimce a baya sai kace shine angon,shadda sky ya saka shigen color din ankon da Naila ta saka,baya ta bude ta shiga gefensa,Yana ta kallonta yace kinyi kyau sosai,Amarya da ango sun karasa wajen Event suna waje ana ta musu ruwan pics sannan aka Bada sanarwa Amarya da Ango zasu shugo,salon kida aka canja.
Amarya da Ango ana rakosu ana wata musu buzzer suka shiga tar da zauna,Rafeeq tuni suna ciki shi da Kamal,Spark ne ya karaso tare da Naila rike da hannunta suka nemi wuri tare da zama,ko wanne table da abinci da kayan Sha gasu Nan.
Babbar Kawa aka Kira Suhailat Chikar gayu,Chikar gayu ta fito wannan fili ana nemanta,tun daga Jin sunan kowa ya baza Ido yaga wace Chikar gayu,Chikar gayu mikewa tayi akayi harrrrr ana kallonta,ta isa gaban Mc ta karbi Speaker tace Alhmdllh sabo da farin ciki a bani kidan Chika,aka saki sauti Chika tayi rawa iya rawa kamar me ita kadai kwal ta iya chashewa,Naila ce taje da Dan takunta kadan tana mata liki,Su Hanan ne suka shugo da kawayenta suna cin magani.
Naila ce ta radawa Chika maganganu sannan Chika tace a tsaya da kida zata Dan Bada tarihin Amarya a takaice,Sai dariya Chika take bawa mutane domin rawar tata ma ta iya shege ce,Speaker ta karba tace na tabbata kowa yana Jin Hausa a Nan sabo da haka ba ruwan mu da turanci America ma uwata,aka yi dariya.
Tarihin Amarya ta bayar a takaice a nutse Kuma, aka tafa mata,sannan tace Alhmdllh Alhmdllh nasan Amarya baki gaji siyar da dankunne da tozalin tsofaffi ba,Baki gaji siyar da mazari da Alli ba wannan sai Dan koli,Naila tace gaskiya ne wannan, sannan uwarta Bata kulla omo dan awo cewar Naila,bata da kanne ma bare ayi mata fitsarin kwance a mayafi ko Ango ya taba Jin zarnin a Jikin Amarya sanda Yana zuwa zance? Idan ya taba ji ya fada,Naila tace sai dai kamshi wlh,yeeeeee yan mata suka saki shewa.
Hanan ranta ya baci ita da kawayenta masu zugata,tun a wajen ta fara kwalla,tace ba Wanda yasan sirrina sai Naila,wallahi wallahi sai sun San sun min habaici,sai na lakadawa Amarya duka bari a kawota a ranar a gaban mijin nata shege munafuki ai shine ya Fadi sirrina.
Naila tace sabuwar Miya sabon tuwo,me za ayi da tsohon tuwo sai dai almajiri wlh ko a jefa a bola,Chikar gayu tace Kainuwa dashen Allah Amarya Beauty an gaji arziki gaba da baya, fara me farar aniya babu Mai ba sabulu natural daga Allah ce,hakora reras ango ka dace,Naila tace da gani ba yunwa a jikinta Kai da Ganinta kasan ta Sha Madara ta koshi tayi brush da Naman kaza,yayana yayi dace,yanzu nasan yayana ya auri mace, na tabbata ango kayi dace domin ka samu mace ta gari wacce zaka samu nutsuwa a cikin gidanka,wacce zata kula da Kai da danginka da duk wani Wanda ya shafeka.
Duk kawayen su Chikar yawanci daga gidan yari suka fito babu na gari sai dai dai kowa shegiyar kanta ce shi yasa basa Jin kunya ana fada zasu saki shewa,Chika tace jama'a a gurguje bamu iya tashin hankali ba duk da cewa Kawata Nawwara wato Beauty tana da abokiyar zama
Sabo da haka zan danyi nasiha ga Amarya,Beauty idan kika shiga ciki kika tashi hankalin ango to kinci amanata ni babbar Kawa,ko da abokiyar zamanki ta tsokaneki ki to ki nuna mata zaren ba kalar yadin bane, ki mata fatan shiriya idan Kuma anyi rashin sa'a tana da motsi a kanta to karki sa kishi a ranki ki tsaya iyakar iyawarki na ganin cewa an sadata da asibitin masu rangwamen hankali,Bamu ce idan an tabaki ki kyale ba,a'a bamu gaji haka ba,ba ruwanki da tsokana amma ana cewa kule kice chass amma a wajen me gida,yeeeeee ayiririri sai Chika lallai a nuna mata gidan kaso ba karya ba cewar Yan matan,Chika cikin nutsuwa taci gaba yanzu kishin fada da hauka jahilci ne da rashin sanin darajar Kai,a wajen me gida ake nuna kishi, Idan ta bashi Sadine ki bashi sukumbiya,aka kwashe da dariya a wajen,Rafeeq Yana dariya yace wannan yarinyar ban taba ganin Yar iska irinta ba,wai Sukumbiya,Kamal yana ta dariya yace ai dole suyi Yan gidan yari ne fa kaf kawayen maybe,waccen matar Spark din itace key na iskancin ita take musu rada.
Sabo da haka Amarya a zauna lafiya da miji,mudai Munji dadi da iyayenmu basu gaji siyar da tozalin mata da Alli ba,Mun gode Jama'a Allah ya Maida kowa gidansa lafiya ta mikawa MC waya,Hanan ta kumbura iya kumbura ta fusata,Mohsin ango Yana jinsu ba yanda ya iya da su yaso dai ya hanasu amma sun shammace shi,Bai zaci haka zasu yi ba,yace maganin Hanan kenan da ta taba Naila ita zata dinga sasu suna mata rashin mutunci,bata San Naila ba,da ace bata kula Naila ba da lafiya za ayi bikin a gama,Naila ta koma ta zauna kusa da Rafeeq tace baka gaishe ni ba Ina Auntynka,Rafeeq yace ni kawar Nan taki badan Yar duniya bace da na sota ma,Chika? Yace ae ita amma duk danginmu mu kare a Yan gidan yari fisabilillahi,Naila tace gobe za a dakko malamar mu me yin wa'azi a gidan yari ta bangaren Mata,Matashiya ce irinmu amma akwai ilimin addini da hankali wlh ga wa'azi da koya zamantakewar aure,yanzu ku Dan masifa ma malamar me wa'azi yan gidan yari takewa wa'azi duk malaman duniya,Naila tace gwara irin tamu,shekarata ashirin a gidan yari a can aka haifeta yanzu an fitar da ita shekaru biyu da suka wuce Bata fi 22yrs ba wlh sai baiwar wa'azi,Rafeeq yace Allah ya kaimu ai harda Maza maji wa'azin,su Chikar ne suka gayyato mana malama Ikram,wlh indai kana son Chika zan Maka hanyarta,sai nayi shawara cewar Rafeeq,Kamal yace Amarya ango Yana harararmu ki koma wajensa kishin masifa ne da shi,Naila ta mike ta koma wajen Spark.
Ana ta Shirin Dinner da yamma Chikar gayu itace babbar kawar Beauty an dauki wanka kamar me,Amarya kuwa tana wajen make Up tare da wasu kawayen ta Sha farin bride material me tsadar gaske an mata wata gown me kyan gaske ta zaratan amare,an nada mata dauri da silver gogoro, takalmi Silver jaka ma haka,make up din tayi kyau an dora mata mayafin amare a Kanta sharashara sai walwali take ta ko Ina,Ango Yasa Shadda Yar ubansu Silver kalar takalmi da jakarta da gogoro.
Su Chika duk anci ankon Leshi me kyan gaske Blue and white,kawaye an Sha wanka sunyi gayya kamar me, Yan mata tamfatsa tamfatsa sunzo duk kawayensu ne yawanci daga gidan yari suka fito,Kamal ne zaizo shima sabo da abokinsa Spark ai kuwa Rafeeq yace akwai dinner? akace ae yace ko banza na Kalli mata mu tafi Kamaluddeen,Kamal yace Allah ya shiryeka Kai ba Dan iska ba sai son kallon mata? Rafeeq yace ko banza ai na kashe kwarkwatar idona muje,Da yamma suka dira,Rafeeq lokaci nayi yafi uban kowa saurin shiryawa yace Kano sai da shadda ya fito cikin shadda me kyau wata ita ba milk ba ita Kuma ba ruwan kasa ba,suna dakin Spark shi da Kamal,Kamal yace gaskiya kayi kyau Rafeeq Allah kawo babban rabo,yayi shuru kamar Salihi,Mayen mata Misam ne Allah yayi ya kira wayar Rafeeq,kana Ina? Rafeeq yace dinner Yan mata ne iya kallonka,Misam yace amma baku da mutunci shine ko ku fada min ni shugaban mata guda,Ba komai ai gobe ma matan zasu taru ko? Rafeeq yace ai ance akwai walima mata da Maza za ayi wa'azin zama da iyali lafiya,Misam yace tab zanzo naji Ina jin wa'azi Ina zabar nawa ya nawa.
Ana ta tafiya wurin dinner dangin ango dana Amarya,Abba ya shugo gidan Yana tarkata kan Yan mata danginsu ku fita ku tafi aje ayi rayuwa Allah ya sanya Alkhairi,Wata babbar mace me suna Tani tace zanje nima nayi kallo, Abba yace Tani gidan uban wa zaki? ki batawa yara show sunyi gayu aga irinki kamar wata Tsohuwar mota hayis ba Inda zaki ai zubar da girma ne,Kubra ta cakare taci wani material an mata make up,kyan da tayi ya Isa,Dake Kubra ce sai Abba yace Yar Inna an fito? Ko ranar bikinmu baki kyau haka ba,idan an girma asan an girma,Kuma wallahi sai kika yi kyau kamar kiyi ta zama a haka,ai da bazan sake fita wajen sana'a ba gwara kullum na dinga kallonki.
Umma tace wai baza kaje bane? Abba yace a'a haka kawai naje na zubarwa da yarana mutunci wlh tsab naji kida zan taka, Kinga ai girma ya Fadi kuje ku dai kawo Basma nayi miki rainonta,tace madararta tana dakina Jikin bed,yace to ya karbi Basma Umma ta fita ta tafi tare dasu Hajiya Tagwadas ansha gayu.
Naila ta Sha anko itama ta cakare ta zuba kyau kamar a saceta kawai Spark take jira,ba a dade ba yazo a mota ana tuka shi ya hakimce a baya sai kace shine angon,shadda sky ya saka shigen color din ankon da Naila ta saka,baya ta bude ta shiga gefensa,Yana ta kallonta yace kinyi kyau sosai,Amarya da ango sun karasa wajen Event suna waje ana ta musu ruwan pics sannan aka Bada sanarwa Amarya da Ango zasu shugo,salon kida aka canja.
Amarya da Ango ana rakosu ana wata musu buzzer suka shiga tar da zauna,Rafeeq tuni suna ciki shi da Kamal,Spark ne ya karaso tare da Naila rike da hannunta suka nemi wuri tare da zama,ko wanne table da abinci da kayan Sha gasu Nan.
Babbar Kawa aka Kira Suhailat Chikar gayu,Chikar gayu ta fito wannan fili ana nemanta,tun daga Jin sunan kowa ya baza Ido yaga wace Chikar gayu,Chikar gayu mikewa tayi akayi harrrrr ana kallonta,ta isa gaban Mc ta karbi Speaker tace Alhmdllh sabo da farin ciki a bani kidan Chika,aka saki sauti Chika tayi rawa iya rawa kamar me ita kadai kwal ta iya chashewa,Naila ce taje da Dan takunta kadan tana mata liki,Su Hanan ne suka shugo da kawayenta suna cin magani.
Naila ce ta radawa Chika maganganu sannan Chika tace a tsaya da kida zata Dan Bada tarihin Amarya a takaice,Sai dariya Chika take bawa mutane domin rawar tata ma ta iya shege ce,Speaker ta karba tace na tabbata kowa yana Jin Hausa a Nan sabo da haka ba ruwan mu da turanci America ma uwata,aka yi dariya.
Tarihin Amarya ta bayar a takaice a nutse Kuma, aka tafa mata,sannan tace Alhmdllh Alhmdllh nasan Amarya baki gaji siyar da dankunne da tozalin tsofaffi ba,Baki gaji siyar da mazari da Alli ba wannan sai Dan koli,Naila tace gaskiya ne wannan, sannan uwarta Bata kulla omo dan awo cewar Naila,bata da kanne ma bare ayi mata fitsarin kwance a mayafi ko Ango ya taba Jin zarnin a Jikin Amarya sanda Yana zuwa zance? Idan ya taba ji ya fada,Naila tace sai dai kamshi wlh,yeeeeee yan mata suka saki shewa.
Hanan ranta ya baci ita da kawayenta masu zugata,tun a wajen ta fara kwalla,tace ba Wanda yasan sirrina sai Naila,wallahi wallahi sai sun San sun min habaici,sai na lakadawa Amarya duka bari a kawota a ranar a gaban mijin nata shege munafuki ai shine ya Fadi sirrina.
Naila tace sabuwar Miya sabon tuwo,me za ayi da tsohon tuwo sai dai almajiri wlh ko a jefa a bola,Chikar gayu tace Kainuwa dashen Allah Amarya Beauty an gaji arziki gaba da baya, fara me farar aniya babu Mai ba sabulu natural daga Allah ce,hakora reras ango ka dace,Naila tace da gani ba yunwa a jikinta Kai da Ganinta kasan ta Sha Madara ta koshi tayi brush da Naman kaza,yayana yayi dace,yanzu nasan yayana ya auri mace, na tabbata ango kayi dace domin ka samu mace ta gari wacce zaka samu nutsuwa a cikin gidanka,wacce zata kula da Kai da danginka da duk wani Wanda ya shafeka.
Duk kawayen su Chikar yawanci daga gidan yari suka fito babu na gari sai dai dai kowa shegiyar kanta ce shi yasa basa Jin kunya ana fada zasu saki shewa,Chika tace jama'a a gurguje bamu iya tashin hankali ba duk da cewa Kawata Nawwara wato Beauty tana da abokiyar zama
Sabo da haka zan danyi nasiha ga Amarya,Beauty idan kika shiga ciki kika tashi hankalin ango to kinci amanata ni babbar Kawa,ko da abokiyar zamanki ta tsokaneki ki to ki nuna mata zaren ba kalar yadin bane, ki mata fatan shiriya idan Kuma anyi rashin sa'a tana da motsi a kanta to karki sa kishi a ranki ki tsaya iyakar iyawarki na ganin cewa an sadata da asibitin masu rangwamen hankali,Bamu ce idan an tabaki ki kyale ba,a'a bamu gaji haka ba,ba ruwanki da tsokana amma ana cewa kule kice chass amma a wajen me gida,yeeeeee ayiririri sai Chika lallai a nuna mata gidan kaso ba karya ba cewar Yan matan,Chika cikin nutsuwa taci gaba yanzu kishin fada da hauka jahilci ne da rashin sanin darajar Kai,a wajen me gida ake nuna kishi, Idan ta bashi Sadine ki bashi sukumbiya,aka kwashe da dariya a wajen,Rafeeq Yana dariya yace wannan yarinyar ban taba ganin Yar iska irinta ba,wai Sukumbiya,Kamal yana ta dariya yace ai dole suyi Yan gidan yari ne fa kaf kawayen maybe,waccen matar Spark din itace key na iskancin ita take musu rada.
Sabo da haka Amarya a zauna lafiya da miji,mudai Munji dadi da iyayenmu basu gaji siyar da tozalin mata da Alli ba,Mun gode Jama'a Allah ya Maida kowa gidansa lafiya ta mikawa MC waya,Hanan ta kumbura iya kumbura ta fusata,Mohsin ango Yana jinsu ba yanda ya iya da su yaso dai ya hanasu amma sun shammace shi,Bai zaci haka zasu yi ba,yace maganin Hanan kenan da ta taba Naila ita zata dinga sasu suna mata rashin mutunci,bata San Naila ba,da ace bata kula Naila ba da lafiya za ayi bikin a gama,Naila ta koma ta zauna kusa da Rafeeq tace baka gaishe ni ba Ina Auntynka,Rafeeq yace ni kawar Nan taki badan Yar duniya bace da na sota ma,Chika? Yace ae ita amma duk danginmu mu kare a Yan gidan yari fisabilillahi,Naila tace gobe za a dakko malamar mu me yin wa'azi a gidan yari ta bangaren Mata,Matashiya ce irinmu amma akwai ilimin addini da hankali wlh ga wa'azi da koya zamantakewar aure,yanzu ku Dan masifa ma malamar me wa'azi yan gidan yari takewa wa'azi duk malaman duniya,Naila tace gwara irin tamu,shekarata ashirin a gidan yari a can aka haifeta yanzu an fitar da ita shekaru biyu da suka wuce Bata fi 22yrs ba wlh sai baiwar wa'azi,Rafeeq yace Allah ya kaimu ai harda Maza maji wa'azin,su Chikar ne suka gayyato mana malama Ikram,wlh indai kana son Chika zan Maka hanyarta,sai nayi shawara cewar Rafeeq,Kamal yace Amarya ango Yana harararmu ki koma wajensa kishin masifa ne da shi,Naila ta mike ta koma wajen Spark.