← Book details Tantiriya A Gidan Yari Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 73 OF 98

Sashe 73

Tantiriya A Gidan Yari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Bayan an bayar da Rafeeq Mima tace ta gama Bada yara a duniya, sai ta haifo mace Kuma,a da matan taso ta raba sunfi dadin raino da tankwarawa,idan macece Bata da matsalar Maza sai yanzu Kuma ta haifi Bisma wacce itama tayi aure da yaranta biyu tana zaune a Uk,sai Badia itama tayi aure da yarta Daya a garin Bauchi,su ma basu da wata tarbiyyar kowa harkar gabansa yake babu me yiwa wani fada,Wanda kake shiri da shi to da shi kawai zaka yi zumunci.

Daga Nan Mima ta haifo Waleed,Atif,Arham duk makarantar sojoji sukeyi matasa dasu,sai Kuma ta haifi mata biyu Anam,Zainab suma duk sun zama Yan mata haka marasa tarbiyya ne,ga kudi ga sakaki na iyaye sai abinda suka ga dama,karatu Kuma da wuri ake saka su shi yasa zaka gansu yara amma sunyi Nisa a karatu,Ina kaje boko Ina zasu boko,Islamiyya a gidan ake musu sai sunga dama suke zuwa ma dake Islamiyya ce amma boko ko basa so sai sunje.

Mace komai kankantar ta matukar me kudi ya fito to dole aure zasu mata karatu tayi a gidan mijinta shi yasa su Badia ko secondary basu gama ba aka musu aure a hannun mazajensu suka yi karatu.
Idan talakane Kuma sai suce yarsu karatu zata yi sabo da baza su bashi ba.
Duk sun lalata family dinsu sun tarwatsa kansu.

Ci gaban labari

Ana Kai Invitation prison Azima me kwana ba wando ta cika Umarni ta raba na Beauty a gidan tace kowacce tayi addua da fatan Alkhairi tunda ba a samu zuwa ba, suna ta tayata murna,Zagawa tayi ta katangar bangaren Maza wata a ciki ta dagata sama ta watsa musu Iv ta ko wacce kusurwa ta bangaren mazan.
Dan Indo ya dawo daga cikin ball yaga IV da yawa ya dauka ya fara karantawa sabo da IV din gidan yarin daban suka bayar da kudi aka buga musu ba irin na normal mutane da aka raba bane,ya karanta yaga an saka
Iyalan General Ahmad Maleek
Na farin cikin gayyatar ku
Zuwa wajen daurin auren
Yayansu, Wanda an riga an daura shi tun 12Jul
Naila Hashim (Jamilu)
Da Angonta
Ashraf Ahmad Maleek(Spark)

Ku da baku samu damar halatta ba a tayamu da addua,yanzu haka an Kai Amarya dakin mijinta idan da rabo ma an samu tuni.

Sabo da takaici Dan Indo ta hannunsa ya yayyaga,ya kurma ihu tare da furta Kai Yan matan gidan yariiiiii.......kuzo nayi muku cikiiiii.....kun San yanda ake cikiiiii .....Kafin kace me gidan yari bangaren Maza ya dauka Jamilu yayi aure,kowa yazo Dan Indo yake nema.

Jamilu da yayi aure ba a kawo mana shi gidan yari ba mun more,Dan Indo yace ba labari gashi wannan Spark din ubansa ma Soja ne duk iskancina ai bazan kawo matar wani ba.
Scoler ne ya saki shewa ahayyeeee chass wa ya fada muku barno gabas take? Ai na fada muku Terror yayi gabas kunyi Yamma wlh na gaba yayi gaba na baya sai labari billahillazi,Jamilu tana can tana tsotsar madarar Nido,washer yace har milky me bukunboti ma yanzu ta zuki abarta da tsinken zuka straw .

Malam Sharu kuwa suna Gani suka fara Alhmdllh Alhmdllh wato aihin Allah ya karbi adduar mu ya shirya Jamilu da Spark,Allah ya Kara dankon kauna da soyayya har mutuwa,Malam Garzali yace Astagafrillah wato sai naji darshin hassada a raina, hassada ta darso a kirjina,naji Ina yiwa wannan yaro Spark Hassada da samun Jamilu Tantiriya naji wannan ni'ima dama kaina ta fada,Allah ya shiryeka Dan uwa cewar Malam Jilani.

Su Naila suna hanya Spark sai waya yake wa driver Wanda ya dakko Amarya da kawayenta kayi fa tuki a hankali karka cuceni Mubarak,Wlh ka kashe min Amarya sai ka mutu kaima, Mubarak Dan gidan yayan su Mima ne Uzairu,sauran biyu Kuma yayyen Wahida ne,dukkansu cousins din spark ne ba yanda suka iya haka ya tattaro su dakko Amarya.

Naila kuwa hirarsu kawai suke da su Rayya sai fulatanci suke,Chika kuwa Misam ta dinga nemowa a social media ta ganshi kuwa a Instagram tayi following dinsa,tana duba pics dinsa da videos dinsa gasu Nan latest,sai dai tana yawan ganinsa da Yan mata,ana shigowa garin Abuja Naila ta fara murmushi harda rawa da kafadu anzo.. anzo... Mubarak yace Spark ya samu daidai shi wlh,Naila tace ai dama nace bazan bacci ba idona kirrrrr sai anzo,Mubarak Yana dariya ya kira Spark a waya yace Ango munzo muna Abuja amma gidan Mummy zamu fara kaita sun ce,Spark yace to kuje Gani nan, Mubarak yace Kai Spark harka ta mata me zaka yi Kuma,Yace baka da hankali Mubarak ance ma Amarya wasa ce ya ja tsaki ya kashe wayar.

Naila ya kira a waya yace Amaryata? Naila ta kama dariya tace nazo ai no more damuwa,yace yeah mun daina fada ai Kuma,wani wuri suka yi parking,Dattijai mutan kauye basu San haka ba a rayuwarsu sai yau,Motocin Spark ne guda hudu masu tsadar gaske sababbi gal suka karaso wajen da su Amarya suke,Mota Daya Kamal ne da Rafeeq sai wani Abokin Spark shima farook,Daya motar Kuma sojoji ne mutum uku Helux baka me rufaffen baya tana Shining,Ango Yana cikin farar mota Yar ubansu an mata wata uwar kwalliyar flowers kana gani kasan ta Amarya ce.

Gaba driver ne shima Soja ne ke tuka shi,kofa driver ya bude Masa ya fito,Ya Sha wata Gezna kalar adon leshin Naila milk,yau ya sa hula a Saman tarin sumarsa wacce ta Sha gyara,Sajensa da dan gemu yasha gyara sai sheki yake,Naila tace ga nawan nan,Chika tace uhmm muna kallon sabon salo yau duk akan Amarya Allah ya bamu itaku Naila,Rayya tace aradu dama ance duk Wanda yaje gidan yari Bada hakkinsa ba sai ya daukaka.

Chika tace nima nan na hango tawa Daukakar Rayya,dole sai na auri kanin mijin yarinyar nan Naila,baza ta sabu ba,ai ko Misam ya shirya ko Rafeeq cikinsu dole wani ya Kara rage mugun iri idan ba haka ba na tambade,Dije tace ni kuwa Ja'e ma da zai dawo to ni wlh da na gama tawa Daukakar aradu na Saba da Hallaren Ja'e,duk kudin mutum,duk kyawun Da namiji ke ko da Larabawa za a tara min a jefa Ja'e cikinsu to Ja'e zan zaba,Rayya tace yo me za ayi da mutum ba saniya sai motoci.

Spark ne ya tako cikin takunsa na Yan gayu ya bude bayan mota yaga Dije ce ya Maida ya rufe yace shi yasa naga motar ta min duhu,dayan side din ya zaga ya bude yace lantarki haba yanzu naga haske,dariya Naila tayi a hankali tace bari nayi kunya tunda Amarya ce,Mayafinta ta lulluba a kanta fuskarta duk ta rufe sai ta mayafin kawai take kallon mutum,Hand bag dinta ta dauka sannan ya riko hannunta ta fito a hankali, Spark Yana tsotsar alawa a bakinsa Naila tace San min abinda kake ci,ya ma manta shi Yana Shan abu,cirowa yayi da hannu ya sa mata a baki yace haba in kayi aure shike nan baza a barka kayi kiba ba, komai Kaci sai matar ta ci,mata ku dai zuciyar ku a mace take kullum a baku,Naila tace Dan Allah karka sa Amarya ta dinga dariya ana ganinta,Su Goggo ana mota suna ta salati.

Goggo tace yau ni Ramatu naga abinda ya isheni ni 'yasu,rashin kunya kiri kiri,wallahi Kin Gani Tani hannu ya rike mata,Tani tace yau ni Ina zan iya kallon wannan fitsara,dole Kakan Naila yaji zancen nan cewar Goggo,Tani ta rafka salati ganin Spark ya rungume Amarya suna dariya a Jikin mota,mayafinta ya daga ya shigar da kansa shima,Goggo tace haka duniya ta koma? Shike nan duniya tazo karshe an kusa tashin kiyama,ke Kinga Dan Allah mun bani Ramatu,ai muna kauye ta nan yajuju da majiju zasu fara bullowa,Goggo tace na fadawa Naila idan ta fara ganinsu ta bugo mana waya mu kimtsa,Me tuki dai yana ta dariyar su Goggo,bangaren su Dije ma sai salati suke suna Jin kunya,Chika kuwa ficewa tayi da su Kamal suna ta daukan Amarya da Ango pics da video iri iri,sai da suka gama sannan Spark ya sa Amarya a motarsa ya shiga gefenta suka tafi gidan Mummy.

Mummy ya ta iya Danta ne ya fada mata zasu zo haka ta kira kawaye da wasu Yan uwan suka je gidanta za a kawo musu Amarya,Mima kuwa duk dangin kusan suna gidanta itama suna jiran Amarya,suna cewa wannan bikin arna kawai aka yi Amarya ya gama kwashewa da ita sabo da iskanci yanzu ace za a kawo musu ita,Mima tace mu da muka gansu akan gado ai magana ta kare Kuma,ni wlh tunda ake haihuwa ban taba ganin yaro irin Spark ba, kace zaka Masa Baki yace zai afka Maka.

Maman Rafeeq tana ta dariya tace kar ki Masa baki wlh hukuncin Allah ne,Kuma Dan kin gansu akan gado sai kice yayi wani Abu ba fa lallai bane zafi ya rage maybe,Mima tace ai kune Yan zamani Kuma ba wasu manya bane Kun San ya matasan yanzu suke,Maman Rafeeq tace sai addua wlh yaran yanzu,Lateefa tace ai Ubansa ne ya daure Masa gindi shi yasa ko me yace sai ya hau ya zauna,duk yaran da basa gabansa yafi kaunar su,da wuri yake musu Abu,ko Rafeeq Dan yaki karba ne amma ya damu,baya son sana'ar Nan tasa wai Shawarma Joint kiji iskanci,wlh duk kudi ne yasa su yin haka,basu da matsala ne shi yasa suke wannan iskancin cewar Kawar Mima.
Mima tace yanzu haka Amaryar da dan cikinta a gaba irin dai ta Christian,gata tsagera idonta kar ni dai na shiga uku banyi dacen suruka ba cewar Mima tana zuba tagumi.
Chapter 73 · 0% Book details