Sashe 48
Tantiriya A Gidan Yari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ashraf Kuma tunda ya fita yake tunanin wannan yarinyar yace anya kuwa wannan bata da hadi Jamiluna,bari Allah ya hadamu idan da rabon na sake kallon Jamilu timbir ai shike nan,zata gane kurenta duk gashin Nan sai na cire shi in na samu dama ai nasan kalar boobs din nata da can wajen Garejin, ai nafi tantancewa idan na sake gani,murmushi ya saki yace Allah ya sake hadamu wayo zan mata.
Yau kwana yayi da farin ciki da murna yaga me kama da Jamilunsa,Allah Allah yake su sake haduwa,Naila ma tafiya tayi taji dadin ganinsa Kuma ta fahimci bai ganeta ba,ga kudi zata samu nan take ta bugawa Chikar gayu waya tace ki bar gidan Mima kice za a miki aure ki dawo gidan Mummy ki dinga hada mata tuggu kina gana mata azaba,Chikar gayu ita kaunar Misam tuni ta kama ta ma, bata yin abinda akace tayi iskancinta kawai take a gida,duk abinda akace tayi ba shi zata yi ba ta buwayi kowa ta gallabe su,idan akace ta soya dankalin sai ta soya doya,in akace kosai sai tayi yamballs,kowa yanzu tsoron sata dafa Masa Abu yake sabo da an San ba shi zata kawo ba anyi anyi bata ji,Misam dinma bai san me take ba domin bai cika zuwa gidan ba.
Chikar gayu tace ni bazan koma gidan wata ba na Saba da Nan gaskiya ni nayi miji sabo da haka a gidan surukaina nake bazan zubar da damata ba,Na hadu da wani cool guy,kije kiji da aikinki nima nawa nake yi, Naila tace ba komai wlh sai nazo gidan na tona miki asiri,Chikar gayu tace ba komai nima Ina ji da nawa ai iya shegen sabo da haka na gani Kuma na yaba,Kuma tunda na kulla Masa sai na aure shi inshaallah,kin fasa basu tarbiyyar? ae na fasa idan na aure shi nafi bashi da kyau ,Misam ne ya shugo gidan sanye da yard me tsada fari yayi kyau,Chikar gayu wayar ta kashe ta kalle shi ya galla mata harara,tace an musulunta ashe yau anje masallaci,ashe kana sallah ai ban sani ba,Rafeeq ne ya shugo Chikar gayu ta gane shi sai yau ta ganshi a gidan tace ai da Gani ba tambaya kaga munafuki dama shima a nan yake,kafin Rafeeq ya kalleta ta mike da gudu ta fada kitchen tana cewa shinkafata zata Kone, ba girkin da take yi,lekowa tayi kadan suka yi Ido hudu da Rafeeq Baki ya bude zaiyi magana ta hau rokonsa da hannu yayi shuru kar ya fada tana nuna Masa yayi shuru da hannu,Baki ya tabe,Misam yace ke kawo mana abinci Yana harararta.
Chikar gayu ta shige tana dube dube sai ga kyankyaso kato ya fito daga cikin wani lungu, da sauri tasa tsinken tsintsiya ta tsire kyankyason ta dora a plate ta rufe ta fito kamar abin arziki tace sannunku ta ajiye a gaban Misam tace gashi tana yin kasa da Kai,Misam yunwa yake ji Yana bude plate yaga katon kyankyaso a soke a Jikin tsinke,mikewa yayi Chikar gayu ta mike tare da kwashewa da gudu ya ya bita suka yi waje da gudu,tsayawa yayi yace sai na harbeki idan na sake ganinki Yana huci,ya dawo ya samu Rafeeq ma ya fice shi Yana jinjina rashin Jin Chikar gayu.
Yau cikin dare Umma ta fara nakuda,Abba dole ya farka daga bacci,Umma tace Ina Jin haihuwa ce tashi ka daukeni na rasa Inda zan saka kaina,Abba yace da wannan uban cikin kamar zai taba kasa ga kibarki ta ya zan iya kalleni fa sai kace kazar mayu,Umma tace wayyo bayana ka daukeni Hashimu kaji na fada Maka,Hashimu yayi yayi ya daga Umma ya kasa,Umma haushi yasa da ciwon nakuda ta mike zumbur ta dauki Abba Dolo cak ta jefa shi a Saman bed tana masifa,Abba yace na zaci ma shillo shilloriya zaki min ai da naji dadina,Wani takaici ya kama Umma tace ni mu tafi asibiti,Abba yace yanzu karfe 1 na dare a fita yanzu,Kai dalla in zaka samo me napep ka samo,Abba ya tashi ya fice ya bugawa makwafcinsu kofa yana da Napep ya fito yace Hashimu lafiya? Wlh iyalina ce zata haihu take ta nakuda shine za a kaita asibiti,makwafcin yace Allah sarki ai da ka iya tuki ma da na baka ka kaita kawai,Abba yace ni da ko Keke ban iya ba bare machine ko wani Napep,tunda kake ka taba ganina a kan Keke Ina tukawa, Ido makwafcin ya zaro yace Hashimu duk kiriniyar Yaya Maza suna yara amma baka iya ko Keke ba,Hashimu yace ai ko kyauta ka bani mota sai dai na siyar bazan iya tukawa ba.
Makwafcin key ya dakko yace muje amma Kai mace ma ta fika kwazo,Abba yace hmmm rabani da tuke tuken nan bazan iya ba Allah na Gani ai sai na manta na taka birki a matsayin totir ko naje na daga hand break din mota a tsakiyar titi,Makwafcin yace amma ka cika lusari ,yace Kun Dade Baku fada min lusari ba ko Dolo dama ni nace muku ba Dolo bane ni?,Shuru mutumin yayi yace ni Ina mamakin ma da Kubra take iya rayuwa da wannan Hashimu,Hashimu ya shugo Palo yace to taso uwar biyu,taka a sannu,Umma ta mike da kyar ta nuna masa kayan haihuwar data hada tace dauki muje Dan Allah kayi sauri wayyo Allah marata faya ta fashe,Abba yace Allah yasa fafunga ce ta fashe ba faya ba,ko kogi ne ya tsage kin isheni da kwailo, Allah yasa na kusa Kara aure Batoola tana nan dai tana jira,Umma dakin su Hidaya ta leka tace ke Hidaya,shuru,zafin ciwo yasa ta dirkawa Hidaya duka tace tashi ke mun tafi asibiti kuyi min addua ki tashe su kuyi Nafeela da addua,Abba ya leko yace ku hada Dani, Hidaya harda kuka tace Umma zan biku,Abba yace harkar bata yara bace ku zauna ni na isa komai,Umma Mohsin ta kira bugu daya ya daga dama sabo da cikin Umma ya tsufa shi Kam kullum a ready yake,Yana ganin kira ya daga,kasa magana tayi ta rike ciki tace wash,Abba ya karbi wayar yace Mohsin Umma haihuwa ka taho asibiti Maza private Kuma zaka biya,Mohsin yace to wanne? Abba yace asibitin Uba,Mohsin yace banji ba me? Abba yace faya ta fashe faya sauri muke ya kashe wayar.
Umma ce zata ruko shi ya kwace da sauri tare da daka tsalle ya koma gefe yace bazan manta yanda kika kusa kasheni ba a haihuwar Hidaya,muje Ina daga baya baya,Umma ta shiga napep tana wash tana cijewa,Abba ya shiga gaba wai Dan kar ma ta ruko shi taje ta shake shi,Umma ita kadai a baya tana ta Jin jiki,Mohsin zai fito ya saka kaya Hanan tace wlh ba Inda zaka ta rike shi Yana Juyowa ya kwada mata Mari ta sake shi ba shiri yaja tsaki ya fice abinsa ya hau machine ya dinga fyalla wuta,Yana kiran Abba yaji Ina suka nufa Abba sai fada Masa yake Mohsin faya ce ta fashe,Sai me napep dinne ya kwace wayar suka yi magana da Mohsin sannan suka wuce private hospital,kafin suje ma Mohsin ya riga su zuwa har ya biya komai ana kawo Umma Mohsin shi ya rike Umma ya shigar da uwarsa har ciki,ya kira Hanan yace ki shirya zanzo na daukeki,tace ni bacci zanyi sanda na haihu ni waye yazo min,dama nifa gaskiya wayata da aka sace min da kayan sawata Ina zarginka ko Kaine ka kwashe ka kaiwa Hidaya,wayarsa ya kashe kawai ransa a bace,ya kira Hajiya Tagwadas kafin ma yaje ya dakkota har tasa an kawota a Napep dinta da ake mata haya,Abba dake asibitin private ne Yana ciki,ance ya fita yaki yace duk haihuwar matata tare muke yi bazan fita ba.
Batoola kuwa an daura mata aure Abba bai ma sani ba shi kuwa Mohsin har daurin aure yaje amma yaki fadawa Abba suka barshi Nan Yana jiran Batoola,sun hada baki akan kar a fada masa Batoola tayi aure sai sanda ya koma zance yaji.
Ana ta jiran Umma ana mata addua Abba yana ciki tare da Hajiya Tagwadas tace Dan Allah Hashimu ka fita ka bamu waje wai me zaka gani ne wannan masifa da me tayi kama Kai ko kyankyammi baka yi? Abba yace gudan jinjina da Rabin raina Umman Mohsin na fita na barta ai bazai yuwu ba Sam,haka aka kyaleshi,mata suna taimakawa Umma ana kokarin fiddo da Baby Hashimu yace kar ku kashe min dana wlh karku soma.
Allah yasa dai Umma ta haifo yarta mace kyakyawa da ita kamar Yar Mohsin da Naila suna kama,Hashimu bayan an goge jajirya katuwar gaske aka miko Masa yace macece bazan Kalli tsaraicinta ba ku nadeta a zani,haba ai ba tsari na Kalli na uwa na Kalli na 'ya, aka nadeta tare da Mikasa duk ya dame su a dakin,ya karba ya mata adduoi sosai a kunne sannan ya taba kumatunta yace.. Yan... Yan.. Yan kin ganni sunana Abba,Hashimu ne idan kin girma zaki ji inkiyata mummuna wacce baza ta miki dadi ba Hashimu Dolo,Nurses sai dariya suke kamar me, Mohsin Abba ya kawowa Yar Yana cewa kaga kanwarka ya ka ganta katuwa kamarku daya,uhm ansha warin gardawa a ciki da Wiwi Allah sa kar ta samu cutar warin Kashi,irin wannan wari data shaka tun tana ciki sai addua,Mohsin shi kansa Abba dariya yake bashi sai kace a kanta aka fara haifar Masa yara,sai murna yake yace sai nayi sati guda ban siyar da kayan Miya ba sai bayan suna,Mohsin yace Allah ya kaimu shima yayiwa kanwarsa addua sannan yace ya Umman Abba? garau take da ba lafiya ba ai baza ka ganni a waje ba,Mohsin a ransa yace ta wani fannin Uwata tayi dacen miji.
Yau kwana yayi da farin ciki da murna yaga me kama da Jamilunsa,Allah Allah yake su sake haduwa,Naila ma tafiya tayi taji dadin ganinsa Kuma ta fahimci bai ganeta ba,ga kudi zata samu nan take ta bugawa Chikar gayu waya tace ki bar gidan Mima kice za a miki aure ki dawo gidan Mummy ki dinga hada mata tuggu kina gana mata azaba,Chikar gayu ita kaunar Misam tuni ta kama ta ma, bata yin abinda akace tayi iskancinta kawai take a gida,duk abinda akace tayi ba shi zata yi ba ta buwayi kowa ta gallabe su,idan akace ta soya dankalin sai ta soya doya,in akace kosai sai tayi yamballs,kowa yanzu tsoron sata dafa Masa Abu yake sabo da an San ba shi zata kawo ba anyi anyi bata ji,Misam dinma bai san me take ba domin bai cika zuwa gidan ba.
Chikar gayu tace ni bazan koma gidan wata ba na Saba da Nan gaskiya ni nayi miji sabo da haka a gidan surukaina nake bazan zubar da damata ba,Na hadu da wani cool guy,kije kiji da aikinki nima nawa nake yi, Naila tace ba komai wlh sai nazo gidan na tona miki asiri,Chikar gayu tace ba komai nima Ina ji da nawa ai iya shegen sabo da haka na gani Kuma na yaba,Kuma tunda na kulla Masa sai na aure shi inshaallah,kin fasa basu tarbiyyar? ae na fasa idan na aure shi nafi bashi da kyau ,Misam ne ya shugo gidan sanye da yard me tsada fari yayi kyau,Chikar gayu wayar ta kashe ta kalle shi ya galla mata harara,tace an musulunta ashe yau anje masallaci,ashe kana sallah ai ban sani ba,Rafeeq ne ya shugo Chikar gayu ta gane shi sai yau ta ganshi a gidan tace ai da Gani ba tambaya kaga munafuki dama shima a nan yake,kafin Rafeeq ya kalleta ta mike da gudu ta fada kitchen tana cewa shinkafata zata Kone, ba girkin da take yi,lekowa tayi kadan suka yi Ido hudu da Rafeeq Baki ya bude zaiyi magana ta hau rokonsa da hannu yayi shuru kar ya fada tana nuna Masa yayi shuru da hannu,Baki ya tabe,Misam yace ke kawo mana abinci Yana harararta.
Chikar gayu ta shige tana dube dube sai ga kyankyaso kato ya fito daga cikin wani lungu, da sauri tasa tsinken tsintsiya ta tsire kyankyason ta dora a plate ta rufe ta fito kamar abin arziki tace sannunku ta ajiye a gaban Misam tace gashi tana yin kasa da Kai,Misam yunwa yake ji Yana bude plate yaga katon kyankyaso a soke a Jikin tsinke,mikewa yayi Chikar gayu ta mike tare da kwashewa da gudu ya ya bita suka yi waje da gudu,tsayawa yayi yace sai na harbeki idan na sake ganinki Yana huci,ya dawo ya samu Rafeeq ma ya fice shi Yana jinjina rashin Jin Chikar gayu.
Yau cikin dare Umma ta fara nakuda,Abba dole ya farka daga bacci,Umma tace Ina Jin haihuwa ce tashi ka daukeni na rasa Inda zan saka kaina,Abba yace da wannan uban cikin kamar zai taba kasa ga kibarki ta ya zan iya kalleni fa sai kace kazar mayu,Umma tace wayyo bayana ka daukeni Hashimu kaji na fada Maka,Hashimu yayi yayi ya daga Umma ya kasa,Umma haushi yasa da ciwon nakuda ta mike zumbur ta dauki Abba Dolo cak ta jefa shi a Saman bed tana masifa,Abba yace na zaci ma shillo shilloriya zaki min ai da naji dadina,Wani takaici ya kama Umma tace ni mu tafi asibiti,Abba yace yanzu karfe 1 na dare a fita yanzu,Kai dalla in zaka samo me napep ka samo,Abba ya tashi ya fice ya bugawa makwafcinsu kofa yana da Napep ya fito yace Hashimu lafiya? Wlh iyalina ce zata haihu take ta nakuda shine za a kaita asibiti,makwafcin yace Allah sarki ai da ka iya tuki ma da na baka ka kaita kawai,Abba yace ni da ko Keke ban iya ba bare machine ko wani Napep,tunda kake ka taba ganina a kan Keke Ina tukawa, Ido makwafcin ya zaro yace Hashimu duk kiriniyar Yaya Maza suna yara amma baka iya ko Keke ba,Hashimu yace ai ko kyauta ka bani mota sai dai na siyar bazan iya tukawa ba.
Makwafcin key ya dakko yace muje amma Kai mace ma ta fika kwazo,Abba yace hmmm rabani da tuke tuken nan bazan iya ba Allah na Gani ai sai na manta na taka birki a matsayin totir ko naje na daga hand break din mota a tsakiyar titi,Makwafcin yace amma ka cika lusari ,yace Kun Dade Baku fada min lusari ba ko Dolo dama ni nace muku ba Dolo bane ni?,Shuru mutumin yayi yace ni Ina mamakin ma da Kubra take iya rayuwa da wannan Hashimu,Hashimu ya shugo Palo yace to taso uwar biyu,taka a sannu,Umma ta mike da kyar ta nuna masa kayan haihuwar data hada tace dauki muje Dan Allah kayi sauri wayyo Allah marata faya ta fashe,Abba yace Allah yasa fafunga ce ta fashe ba faya ba,ko kogi ne ya tsage kin isheni da kwailo, Allah yasa na kusa Kara aure Batoola tana nan dai tana jira,Umma dakin su Hidaya ta leka tace ke Hidaya,shuru,zafin ciwo yasa ta dirkawa Hidaya duka tace tashi ke mun tafi asibiti kuyi min addua ki tashe su kuyi Nafeela da addua,Abba ya leko yace ku hada Dani, Hidaya harda kuka tace Umma zan biku,Abba yace harkar bata yara bace ku zauna ni na isa komai,Umma Mohsin ta kira bugu daya ya daga dama sabo da cikin Umma ya tsufa shi Kam kullum a ready yake,Yana ganin kira ya daga,kasa magana tayi ta rike ciki tace wash,Abba ya karbi wayar yace Mohsin Umma haihuwa ka taho asibiti Maza private Kuma zaka biya,Mohsin yace to wanne? Abba yace asibitin Uba,Mohsin yace banji ba me? Abba yace faya ta fashe faya sauri muke ya kashe wayar.
Umma ce zata ruko shi ya kwace da sauri tare da daka tsalle ya koma gefe yace bazan manta yanda kika kusa kasheni ba a haihuwar Hidaya,muje Ina daga baya baya,Umma ta shiga napep tana wash tana cijewa,Abba ya shiga gaba wai Dan kar ma ta ruko shi taje ta shake shi,Umma ita kadai a baya tana ta Jin jiki,Mohsin zai fito ya saka kaya Hanan tace wlh ba Inda zaka ta rike shi Yana Juyowa ya kwada mata Mari ta sake shi ba shiri yaja tsaki ya fice abinsa ya hau machine ya dinga fyalla wuta,Yana kiran Abba yaji Ina suka nufa Abba sai fada Masa yake Mohsin faya ce ta fashe,Sai me napep dinne ya kwace wayar suka yi magana da Mohsin sannan suka wuce private hospital,kafin suje ma Mohsin ya riga su zuwa har ya biya komai ana kawo Umma Mohsin shi ya rike Umma ya shigar da uwarsa har ciki,ya kira Hanan yace ki shirya zanzo na daukeki,tace ni bacci zanyi sanda na haihu ni waye yazo min,dama nifa gaskiya wayata da aka sace min da kayan sawata Ina zarginka ko Kaine ka kwashe ka kaiwa Hidaya,wayarsa ya kashe kawai ransa a bace,ya kira Hajiya Tagwadas kafin ma yaje ya dakkota har tasa an kawota a Napep dinta da ake mata haya,Abba dake asibitin private ne Yana ciki,ance ya fita yaki yace duk haihuwar matata tare muke yi bazan fita ba.
Batoola kuwa an daura mata aure Abba bai ma sani ba shi kuwa Mohsin har daurin aure yaje amma yaki fadawa Abba suka barshi Nan Yana jiran Batoola,sun hada baki akan kar a fada masa Batoola tayi aure sai sanda ya koma zance yaji.
Ana ta jiran Umma ana mata addua Abba yana ciki tare da Hajiya Tagwadas tace Dan Allah Hashimu ka fita ka bamu waje wai me zaka gani ne wannan masifa da me tayi kama Kai ko kyankyammi baka yi? Abba yace gudan jinjina da Rabin raina Umman Mohsin na fita na barta ai bazai yuwu ba Sam,haka aka kyaleshi,mata suna taimakawa Umma ana kokarin fiddo da Baby Hashimu yace kar ku kashe min dana wlh karku soma.
Allah yasa dai Umma ta haifo yarta mace kyakyawa da ita kamar Yar Mohsin da Naila suna kama,Hashimu bayan an goge jajirya katuwar gaske aka miko Masa yace macece bazan Kalli tsaraicinta ba ku nadeta a zani,haba ai ba tsari na Kalli na uwa na Kalli na 'ya, aka nadeta tare da Mikasa duk ya dame su a dakin,ya karba ya mata adduoi sosai a kunne sannan ya taba kumatunta yace.. Yan... Yan.. Yan kin ganni sunana Abba,Hashimu ne idan kin girma zaki ji inkiyata mummuna wacce baza ta miki dadi ba Hashimu Dolo,Nurses sai dariya suke kamar me, Mohsin Abba ya kawowa Yar Yana cewa kaga kanwarka ya ka ganta katuwa kamarku daya,uhm ansha warin gardawa a ciki da Wiwi Allah sa kar ta samu cutar warin Kashi,irin wannan wari data shaka tun tana ciki sai addua,Mohsin shi kansa Abba dariya yake bashi sai kace a kanta aka fara haifar Masa yara,sai murna yake yace sai nayi sati guda ban siyar da kayan Miya ba sai bayan suna,Mohsin yace Allah ya kaimu shima yayiwa kanwarsa addua sannan yace ya Umman Abba? garau take da ba lafiya ba ai baza ka ganni a waje ba,Mohsin a ransa yace ta wani fannin Uwata tayi dacen miji.