Sashe 11
Tantiriya A Gidan Yari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tace Yaya? Ya amsa da Naam,tace ka dinga yiwa Umma fada ta tsaneni su Hidaya take so kullum suyi tace min Yar kauye jahila,Wani furucin da Umma take yi wallahi tambade yaranta take bata sani ba,kanaji wai naje Abuja na samu masu kudi na dinga cin kudinsu ai wannan jefa yarinya ne a hanyar banza,ni da nayi haka ai gwara na bada kaina a caca, nace sana'a zanyi taki yarda yanzu sabo da Allah wa na sani a Abuja da za ace nabi wata Hajiya Tagwadas,Kai daga Jin sunan kasan ba na kirki bane wai Tagwadas,Kuma idan nace bazan je ba ta dinga zage zage da lafazi marasa dadi,gaskiya kayi mata magana ato ana shiga hakkina a gidan nan,gashi nan sai ramewa nakeyi kullum,Mohsin yaga yanda take uwar kiba da kyau amma tace ramewa take.
Mohsin murmushi yayi yace ashe dai kina da hankali Kanwata,Ina da shi mana amma Kai kadai nake nunawa hankalina a wajen kowa ni bani da hankali ato Kuma bance ka fadawa kowa ni Ina da hankali ba,abin sirri ne,dariya Mohsin yayi ya mika mata hannu yace give me five, ta mika Masa hannu suka tafa,yace idan ta takura kije kawai amma ki nutsu ai tace rako zaki yi just 2weeks zaku dawo ko ai ba matsala idan ta takura kije, shike nan ta furta tace sai da safe,idan ka koma kar ka kula Yar banzar matar Nan taka ko kaji sha'awarta ka makale kafada kace a'a,idan yaki hakura ka fada min zan baka magani shike nan sai kayi wata baka ji kana son mace ba, Baki Mohsin ya tabe,tace ka daina rainawa da gaske nake nazo dasu ni nake da sirrin,lakani ne Dani I can fix you, gwasaleta yayi yace oummm ke dalla rufe min baki,jeki good night ta shiga ciki ta rufe gidan gaba daya .
Ashe Abbansu Yana waje bai shugo ba,
Naila tana shiga ta same su masu Assignment duk suna ta yi wasu suna kallo,Umma zaginta tayi tace Dan iskanci sai ki tafi waje ki Dade haka har dare ki zauna baza ki dawo ba,sabo da ni ban isa ba ubanku dolo ne,ni Kun rainani banza bagidajiya,Naila tace amma ai na fada miki na tafi gidan Yaya,shine zaki Kai dare haka sabo da hauka irin taku ta Yan kauye, Naila baki bude take kallon Umman tasu, ledarsu ta mika musu tace gashi inji Yaya,da sauri Umma ta fisge ledar tace miko min waccen ta hannunki
Ai nawa ne wannan shi ya siya min daban,to Baki isa kinci ke kadai ba,Naila ga taurin Kai tace wlh bazan baki ba ai nawa ne ai ga naku na baku,kune bakin nama ni a can ci muke mu koshi sai ya ishe mu kullum,Naila kika sake fada min magana baza ki samu albarkata ba,da sauri Naila ta bude baki,tace wai ku me kuke yi haka ne komai akayi sai ku dinga furta munanan kalamai akan yaranku wani abinda da iyaye basa ganewa duk Baki ne,amma ni kikewa su Hidaya me yasa ba a musu wai? Ko sabo da ba a nan na girma ba,karku bari nayi fushi wlh Ina da taurin Kai duk duniya babu me sakko Dani,ai samun lafiyarki Naila kiyi aure ko ki bi Hajiya Tagwadas Abuja kiyi kwana biyu kiyi samari ki dawo masu kudi nake so yawwa.
Naila tace ai bance miki bazan je ba amma ni ana matsa min zan fasa Kuma babu me sani,ai kuwa da na tsine miki,Su Hidaya suna jinsu, Hidaya irin mugayen nan ne da basa magana sai bakar zuciya da hassadar tsiya,amma a haka sai ka rantse tafi kowa hali me kyau,tunda taga Naila ta fita kyau da komai shike nan take Dan Jin haushi amma ba sosai ba.
Naila tana cin Dan tsirenta Umma tasa hannu ta kwashe guda hudu ta karawa Hidaya biyu ta bawa Zara daya sai Aslam ta bashi shima suna ci,Naila zuciya tayi ta tura musu tsirenta tace ku hada ku cinye na koshi,suka dauke kuwa.
Sai lokacin ta lura ba Abbansu ta shiga nemansa tace Umma wai Abba fa? Shi yasan Inda yake cewar Umma ta share zancen,
Naila ta mike zata bude kofa tace idan kika bude wallahi sai ranki ya baci,Umma a waje zai kwana fa,ya kwana a bola ma mece matsalarki uwar shishigi cewar Umma.
Tsabar dolonci irin na Abban su Naila da yazo yaga an rufe gida bai iya kiran kowa a waya ba,har yayi niyyar bubbuga musu kofa ya Kai hannu kenan sai ya fasa yace bazan tashe ku ba haka kawai,uhm uhm Ina Sam sai ya juya ya koma masallaci ya kwanta a ciki,a Nan yayi bacci idan ya farka ya tashi yayi Ibada ya koma bacci a haka ya kwana,bayan anyi Sallar asuba ma bacci ya koma a masallacin,yace bazan shiga hakkin su ba suyi baccinku, sai 10am ya fito ya nufi gidan.
Lokacin su Hidaya duk sun tafi makaranta sai Naila sai Umma,Naila ta tasa kokonta a gaba da ta Saba da dashi kullum ita bata Shan shayi kullum sai ta siyo Koko da kosai, Bata ga Abba ya dawo gida ba sai ta kasa Sha ta zauna tayi tagumi,Umma kuwa ko a jikinta wanke wanke take yi a Jikin pampo tana faman zubar da yawu, 10:11am Abba ya shugo gidan dauke da Sallama,Naila tace ahhh.... Alhmdllh Abba Sannu da zuwa Ina ka tafi ne?
Ita kuwa Kubra Umman tasu ko kulashi Bata yi ba sabo da bashi da kudi gashi baya iya komai,shi ba a fada da shi,yace Naila a masallaci na kwana nazo naga Kun rufe kofa kar na tashe ku Kuna bacci shi yasa na kwana masallaci,Yanzu ma nasan Kun tashi shi yasa nazo gidan,Tausayin Abbanta ya kama Naila matuka
Tace Abba kana zuwa ka dinga bugawa komai dare Kai da gidanka,tsaki Kubra ta ja tace gidan Mohsin dai ai shi ya siyi filin ya gina mana da ai a wani wulakantaccen gida muke ,wannan me zai iya tsinanawa kansa bare wani ta ja tsaki taci gaba da wanke wankenta karshe ma ta gaji tace na gaji ka gama kazo ka karasa wanke wanken,da sauri Abba yace to,Naila ta fara hawayen Tausayin Abbansu tace haba Umma haba Umma ni zanyi a madadinsa,Abba bai iya cewa komai ba,.
Naila tace sai kiyi ta cewa Abba bai iya komai ba bayan gashi ya haife mu ai kuwa ya tsinana miki,tunda gashi ma yanzu wani cikin ne Dake na Abba ai kuwa shike tsinana abubuwa, Naila ta mike ta riko hannun Abba ta kaishi Palo ya zauna a kujera tace Abba kaima Dan birni ne shayin? Yace ae Ina da ulcer bana Shan Koko,Naila ta mike ta shige kitchen ta hado Masa tea ta fito,Umma ta mike tana harararta tace dan ubanki mu gani
Ta sa cokali ta juya shayin tace madarar da kika gambaza Masa a ciki shi yake siya mana ko kece? Ai Yaya Mohsin ke siya dansa ne Kuma ai kuwa kayansa ne cewar Naila
Ae to naji bread din da kika dakko na ubanki ne? Ko kina sana'a ne Umma naga dai Mohsin shi ke bada kudin sabo da haka Abba Yana da Iko da shi,kwafa Umma ta ja haka Naila ta kaiwa Abba,shi Kuma ba zuciya ya fara Shan abinsa, Naila juck din kokonta daga kwat kwat kwat sai da kusa shanyewa ta huta ta sake yin kwat kwat kwat, sanye take cikin dan gajeren wandonta buje da shi ba kyan kama da vest a jikinta wai kayan baccinta ne tun a dajinsu, gashinta buzu buzu a cukurkude
A haka Mohsin ya isketa ya Sha wankan shadda fara ya zuba kyau Yana ta kamshi ya shugo,Umma ya fara gaisarwa har kasa,kamar wani sarki ne yazo haka Umma take murna sabo da shike daukan nauyinsu komai da komai, Cikin Palon ya shiga Naila ta kalle shi sama da kasa ta juya ta Kalli Abbansu ta tabe Baki ta zurawa Abban ido.
Abba yace lafiya Naila? Naila tace me yasa kuka haifo wannan a Nan gidan ne muka zama Yaya da kani,ai kunyi hadama sai ku barshi a haife shi a wani gidan mu hadu can muyi aure,har Umma dake waje sai da tayi dariya,tace wannan kwai sakara, Mohsin Yana dariya yace sannu Naila,hannu ta mika Masa suka gaisa harda dunkule hannu ta mika Masa shima ya dunkule nasa ya mika suka hade yanda gayu suke gaisawa.
Naila tace kayi kyau Yaya.
Abuja birnin tarayya Zaune yake a katafaren palonsa Saman kujera ta alfarma da files a gabansa Yana ta rubuce rubuce ga laptop a gefe Yana dubawa,babu Sallama Asmau ta fado palon tare da furta hey Baby,ko kallonta baiyi ba bai ma San iskar data ajiyeta ba,kamar ba mutum take yiwa magana ba,gefensa tazo ta zauna, wata uwar tsawa ya buga mata wacce ba shiri ta mike tsaye zumbur, ba tare da ya kalleta ba yace waye yace ki shigo min gida har Palo ba sallama ba komai, zata yi magana kenan cikin tsawa yace get out.
Asmau ta Sha Abaya me tsada tayi kyau itama kyakyawa ce wankan tarwada taci make up,tace karfa ka manta Spark an mana baiko aure zamuyi,kwana nan zamu zama miji da mata,tunda Mummy ni ta zaba Maka a matsayin mata amma sai ka dinga wulakanta ni,ko da yake ai kowa ma Kai wulakantashi kake yi, Mima ma baka kyaleta ba bare wasu Kai kawai wacce ta raineka itace mutum a wajenka, ko wacce mace an kawo Maka kaki aurenta gashi Nan har ka Kai 31yrs baka yi aure ba ga kannenka nan su suke Shirin yin aure, anya kuwa kalau kake baka da wata cuta ko aljana ta aure ka,Kai duk wankan da mace zata yi bata birgeka duk kyawunta ko kallon mata baka yi,ai kuwa ni nasan Aljana ce ta aureka ma.
Waya ya dauka fuskarsa kyakyawa a murtuke ya kira securities suka shugo mutum biyu yace ku dauki wannan abin kuyi waje da shi karku sake na sake ganinta a gidana ,sorry sir suka furta suka dauki Asmau tana ihu da karaji tana tsine tsine suka jefo ta waje, dama bata shigo da motar ba haka ta shiga motarta sai gidan Mummy wacce ta raini Ashraf Spark.
Mohsin murmushi yayi yace ashe dai kina da hankali Kanwata,Ina da shi mana amma Kai kadai nake nunawa hankalina a wajen kowa ni bani da hankali ato Kuma bance ka fadawa kowa ni Ina da hankali ba,abin sirri ne,dariya Mohsin yayi ya mika mata hannu yace give me five, ta mika Masa hannu suka tafa,yace idan ta takura kije kawai amma ki nutsu ai tace rako zaki yi just 2weeks zaku dawo ko ai ba matsala idan ta takura kije, shike nan ta furta tace sai da safe,idan ka koma kar ka kula Yar banzar matar Nan taka ko kaji sha'awarta ka makale kafada kace a'a,idan yaki hakura ka fada min zan baka magani shike nan sai kayi wata baka ji kana son mace ba, Baki Mohsin ya tabe,tace ka daina rainawa da gaske nake nazo dasu ni nake da sirrin,lakani ne Dani I can fix you, gwasaleta yayi yace oummm ke dalla rufe min baki,jeki good night ta shiga ciki ta rufe gidan gaba daya .
Ashe Abbansu Yana waje bai shugo ba,
Naila tana shiga ta same su masu Assignment duk suna ta yi wasu suna kallo,Umma zaginta tayi tace Dan iskanci sai ki tafi waje ki Dade haka har dare ki zauna baza ki dawo ba,sabo da ni ban isa ba ubanku dolo ne,ni Kun rainani banza bagidajiya,Naila tace amma ai na fada miki na tafi gidan Yaya,shine zaki Kai dare haka sabo da hauka irin taku ta Yan kauye, Naila baki bude take kallon Umman tasu, ledarsu ta mika musu tace gashi inji Yaya,da sauri Umma ta fisge ledar tace miko min waccen ta hannunki
Ai nawa ne wannan shi ya siya min daban,to Baki isa kinci ke kadai ba,Naila ga taurin Kai tace wlh bazan baki ba ai nawa ne ai ga naku na baku,kune bakin nama ni a can ci muke mu koshi sai ya ishe mu kullum,Naila kika sake fada min magana baza ki samu albarkata ba,da sauri Naila ta bude baki,tace wai ku me kuke yi haka ne komai akayi sai ku dinga furta munanan kalamai akan yaranku wani abinda da iyaye basa ganewa duk Baki ne,amma ni kikewa su Hidaya me yasa ba a musu wai? Ko sabo da ba a nan na girma ba,karku bari nayi fushi wlh Ina da taurin Kai duk duniya babu me sakko Dani,ai samun lafiyarki Naila kiyi aure ko ki bi Hajiya Tagwadas Abuja kiyi kwana biyu kiyi samari ki dawo masu kudi nake so yawwa.
Naila tace ai bance miki bazan je ba amma ni ana matsa min zan fasa Kuma babu me sani,ai kuwa da na tsine miki,Su Hidaya suna jinsu, Hidaya irin mugayen nan ne da basa magana sai bakar zuciya da hassadar tsiya,amma a haka sai ka rantse tafi kowa hali me kyau,tunda taga Naila ta fita kyau da komai shike nan take Dan Jin haushi amma ba sosai ba.
Naila tana cin Dan tsirenta Umma tasa hannu ta kwashe guda hudu ta karawa Hidaya biyu ta bawa Zara daya sai Aslam ta bashi shima suna ci,Naila zuciya tayi ta tura musu tsirenta tace ku hada ku cinye na koshi,suka dauke kuwa.
Sai lokacin ta lura ba Abbansu ta shiga nemansa tace Umma wai Abba fa? Shi yasan Inda yake cewar Umma ta share zancen,
Naila ta mike zata bude kofa tace idan kika bude wallahi sai ranki ya baci,Umma a waje zai kwana fa,ya kwana a bola ma mece matsalarki uwar shishigi cewar Umma.
Tsabar dolonci irin na Abban su Naila da yazo yaga an rufe gida bai iya kiran kowa a waya ba,har yayi niyyar bubbuga musu kofa ya Kai hannu kenan sai ya fasa yace bazan tashe ku ba haka kawai,uhm uhm Ina Sam sai ya juya ya koma masallaci ya kwanta a ciki,a Nan yayi bacci idan ya farka ya tashi yayi Ibada ya koma bacci a haka ya kwana,bayan anyi Sallar asuba ma bacci ya koma a masallacin,yace bazan shiga hakkin su ba suyi baccinku, sai 10am ya fito ya nufi gidan.
Lokacin su Hidaya duk sun tafi makaranta sai Naila sai Umma,Naila ta tasa kokonta a gaba da ta Saba da dashi kullum ita bata Shan shayi kullum sai ta siyo Koko da kosai, Bata ga Abba ya dawo gida ba sai ta kasa Sha ta zauna tayi tagumi,Umma kuwa ko a jikinta wanke wanke take yi a Jikin pampo tana faman zubar da yawu, 10:11am Abba ya shugo gidan dauke da Sallama,Naila tace ahhh.... Alhmdllh Abba Sannu da zuwa Ina ka tafi ne?
Ita kuwa Kubra Umman tasu ko kulashi Bata yi ba sabo da bashi da kudi gashi baya iya komai,shi ba a fada da shi,yace Naila a masallaci na kwana nazo naga Kun rufe kofa kar na tashe ku Kuna bacci shi yasa na kwana masallaci,Yanzu ma nasan Kun tashi shi yasa nazo gidan,Tausayin Abbanta ya kama Naila matuka
Tace Abba kana zuwa ka dinga bugawa komai dare Kai da gidanka,tsaki Kubra ta ja tace gidan Mohsin dai ai shi ya siyi filin ya gina mana da ai a wani wulakantaccen gida muke ,wannan me zai iya tsinanawa kansa bare wani ta ja tsaki taci gaba da wanke wankenta karshe ma ta gaji tace na gaji ka gama kazo ka karasa wanke wanken,da sauri Abba yace to,Naila ta fara hawayen Tausayin Abbansu tace haba Umma haba Umma ni zanyi a madadinsa,Abba bai iya cewa komai ba,.
Naila tace sai kiyi ta cewa Abba bai iya komai ba bayan gashi ya haife mu ai kuwa ya tsinana miki,tunda gashi ma yanzu wani cikin ne Dake na Abba ai kuwa shike tsinana abubuwa, Naila ta mike ta riko hannun Abba ta kaishi Palo ya zauna a kujera tace Abba kaima Dan birni ne shayin? Yace ae Ina da ulcer bana Shan Koko,Naila ta mike ta shige kitchen ta hado Masa tea ta fito,Umma ta mike tana harararta tace dan ubanki mu gani
Ta sa cokali ta juya shayin tace madarar da kika gambaza Masa a ciki shi yake siya mana ko kece? Ai Yaya Mohsin ke siya dansa ne Kuma ai kuwa kayansa ne cewar Naila
Ae to naji bread din da kika dakko na ubanki ne? Ko kina sana'a ne Umma naga dai Mohsin shi ke bada kudin sabo da haka Abba Yana da Iko da shi,kwafa Umma ta ja haka Naila ta kaiwa Abba,shi Kuma ba zuciya ya fara Shan abinsa, Naila juck din kokonta daga kwat kwat kwat sai da kusa shanyewa ta huta ta sake yin kwat kwat kwat, sanye take cikin dan gajeren wandonta buje da shi ba kyan kama da vest a jikinta wai kayan baccinta ne tun a dajinsu, gashinta buzu buzu a cukurkude
A haka Mohsin ya isketa ya Sha wankan shadda fara ya zuba kyau Yana ta kamshi ya shugo,Umma ya fara gaisarwa har kasa,kamar wani sarki ne yazo haka Umma take murna sabo da shike daukan nauyinsu komai da komai, Cikin Palon ya shiga Naila ta kalle shi sama da kasa ta juya ta Kalli Abbansu ta tabe Baki ta zurawa Abban ido.
Abba yace lafiya Naila? Naila tace me yasa kuka haifo wannan a Nan gidan ne muka zama Yaya da kani,ai kunyi hadama sai ku barshi a haife shi a wani gidan mu hadu can muyi aure,har Umma dake waje sai da tayi dariya,tace wannan kwai sakara, Mohsin Yana dariya yace sannu Naila,hannu ta mika Masa suka gaisa harda dunkule hannu ta mika Masa shima ya dunkule nasa ya mika suka hade yanda gayu suke gaisawa.
Naila tace kayi kyau Yaya.
Abuja birnin tarayya Zaune yake a katafaren palonsa Saman kujera ta alfarma da files a gabansa Yana ta rubuce rubuce ga laptop a gefe Yana dubawa,babu Sallama Asmau ta fado palon tare da furta hey Baby,ko kallonta baiyi ba bai ma San iskar data ajiyeta ba,kamar ba mutum take yiwa magana ba,gefensa tazo ta zauna, wata uwar tsawa ya buga mata wacce ba shiri ta mike tsaye zumbur, ba tare da ya kalleta ba yace waye yace ki shigo min gida har Palo ba sallama ba komai, zata yi magana kenan cikin tsawa yace get out.
Asmau ta Sha Abaya me tsada tayi kyau itama kyakyawa ce wankan tarwada taci make up,tace karfa ka manta Spark an mana baiko aure zamuyi,kwana nan zamu zama miji da mata,tunda Mummy ni ta zaba Maka a matsayin mata amma sai ka dinga wulakanta ni,ko da yake ai kowa ma Kai wulakantashi kake yi, Mima ma baka kyaleta ba bare wasu Kai kawai wacce ta raineka itace mutum a wajenka, ko wacce mace an kawo Maka kaki aurenta gashi Nan har ka Kai 31yrs baka yi aure ba ga kannenka nan su suke Shirin yin aure, anya kuwa kalau kake baka da wata cuta ko aljana ta aure ka,Kai duk wankan da mace zata yi bata birgeka duk kyawunta ko kallon mata baka yi,ai kuwa ni nasan Aljana ce ta aureka ma.
Waya ya dauka fuskarsa kyakyawa a murtuke ya kira securities suka shugo mutum biyu yace ku dauki wannan abin kuyi waje da shi karku sake na sake ganinta a gidana ,sorry sir suka furta suka dauki Asmau tana ihu da karaji tana tsine tsine suka jefo ta waje, dama bata shigo da motar ba haka ta shiga motarta sai gidan Mummy wacce ta raini Ashraf Spark.