Sashe 18
Tantiriya A Gidan Yari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kawai Baban Asmau sabo da shima babban Soja ne sai yace a dawo da bikin sati daya,Spark sai labari yaji wai an dawo da bikinsa sati daya,a fusace ya tafi gidan Mummy, shi yayi driving shi daya yana shiga ya samu Mummy a palonta tana takaba amma Dan masifa sai tayi bikin kamar ba me takaba ba har lallenta take yi, ya durkusa a kasa a gabanta,haka kawai ya fashe da kukan karya,yana hawaye yace wlh bana sonta Dan Allah karku aura min ita,bazan iya rayuwa da ita ba,ni bata min ba,Mummy ko kissing nata bazan iya ba bakinta ya min girma sai ta hadiye min bakina Kinga nawa Mummy ya turowa Mummy karamin bakinsa,yace ki tuna na Asmau kamar kofar ShopRite ya sake fashewa da kukan karya tare da Dora kansa a cinyar Mummy,a boye Kuma Dariya yake, Dariya Mummy tayi ta rike hannayen Spark tace yau Spark da hawaye akan mace,yace wlh bana son ganinta ko a hanya bare ace zan aureta,ni Spark ace za a min auren dole wlh bazan shiga gidan ba ko an kaita gidana.
Mummy tace ka makara ka koyi sonta wlh yau saura kwana shida zaka ganta a gidanka,mikewa yayi Yana cika Yana batsewa hakarsa bata cimma ruwa ba,sai ya koma spark dinsa ya daure fuska Yana kunkuni ya fice cikin fushi dama kukan karya yayi ko za a tausaya Masa sai gashi ba nasara.
Spark Yana ta bincikensa akan Case din Naila ya zaiyi ya fitar da Jamilu a gidan yari ga matsalar aurensa,kamar wasa biki yazo ranar Friday za a daura Kuma a ranar za a Kai amarya ba wani biki za ayi ba sabo da Mummy tana takaba,Spark har ya hakura ma yace Allah yasa haka shine Mafi alkhairi ya zaiyi.
Ana gobe daurin aure tare suke da Kamal suna Hira, Spark yace na kyale yarinyar Nan sabo da son da take min,taci darajar Sona da take yi amma fa bazan ko hada room da ita ba wlh har ta gaji tace na sake ta shine kawai adalcin da zan iya,ni zan hada jiki ne da wacce zuciyata ke so wacce ta kwanta min a rai wacce bana kyankyami, Kamal zamuga wace Yar sa'ar Nan Yar gidan waye idan Kuma Asmau ce zata sace zuciyar to,Spark yace hmmm ya Kalli Kamal yace zaka Gani inshaallah,ai Asmau bazan taba sonta ba,ni ba abinda ta min kawai Allah bai sa min ko digon sonta ba,hasali ma a duniya ba wacce na tsana irinta.
Asmau kuwa Banda murna ba abinda takeyi,itakam shagali take matukar zata zauna gida daya da spark to rayuwa ta mata dadi ko da bazai kulata.
Washe gari Friday daurin auren Spark dukkan Yan uwa da abokan arziki sun hallara har abokinsa Kamal duk sun dauki wanka amma ba ango yace bazai je ba wlh,mahaifinsa da Mima mahaifiyarsu sunyi iya yinsu yaki zuwa,haka aka daura aure ba ango,shi Yana Office ma aikinsa yake ya kashe waya kar ma ayi Masa Allah sanya Alkhairi,haushi yake ji in akace Allah sanya Alkhairi, zuwa Yamma aka Kai Masa Amarya sai kace dole,amarya anci gayu an hade,har aka watse ango bai zo ba,shuru shuru haka Amarya ta mike tayi alwala tare da gabatar da sallah sannan tayi Shirin bacci ta kwanta abinta,Nawwar a ranar a Office dinsa ya kwana ma bai je gidan ba.
Asmau kuwa bayan ta kwanta bacci, sai da safe dangin Amarya suka zo zasu mata sallama zasu tafi garinsu amma sallamar duniya a palon ba a bude ba,har suka gaji tare da shiga ciki suka zauna a Palo nan ma shuru shuru,suka fara duba bedroom dinta sai kuwa suka hangota a kwance ta Kalli sama idonta a kafe,da sauri suka isa kanta suna tabata shuru har ta sandare ta kame, Dake akwai dattijai a ciki suka tabbatar ta rasu,wuyanta ga shatin igiya Nan da alama igiya aka sa tare da shake mata wuya har ta mutu,sai kuka da kuka suna cewa dama angon yace sai ya kasheta to kuwa da gaske ya kasheta shike nan sai bige bigen waya azo ango ya kashe Amarya ya gudu baya gidan ma.
Hankalin kowa ya sake tashi a family gaba daya,iyayen Spark kowa suka tattaro sai katafaren gidan Spark, Kamal ma da gudu yazo gidan,iyayen Asmau kuka suke suna cewa wallahi baza mu yarda ba,mahaifiyar Asmau ta fada kan gawa tana kuka tace Asmau...Asmau na....wayyo ya kashe min Yata bai San zafin haihuwa ba, Mummy da gudu ta shugo gidan tana wallahi Dana bazai yi kisa ba ban yarda ba karya ne sharri ne ta Fadi a kasa tana kururuwa,Mummy a duniya tana son spark ko uwar data haife shi baza ta fada mata son Spark ba,kamar ranta haka yake,tace wallahi da nasan haka zaku ce bazan daure gindin Spark ya auri Asmau ba.
Mutane ba Wanda ya yarda da Mummy duba da halin Spark da Kuma furucinsa Kuma an San baya karya shi yasa har iyayensa na gaskiya suka yarda, Baban spark shima Soja ne ya Kalli Baban Asmau yace kuyi bincike ku dauki mataki akan Ashraf ya girbi abinda ya shuka,Mima uwa to fa uwa ce amma Mummy ta fita son Spark itama tace idan an tabbatar shine a hukunta shi, sai kuka take tana cewa tabbas yara haihuwarsu jarabawa ce,mu iyaye muna ganin jarabawa akan yaran da muka haifa, Rafeeq zuwa yayi shima Yana ta al'ajabi amma bai yarda Spark zaiyi haka ba sabo da yasan halin Spark.
Baban Asmau dama kadan yake jira yasa aka Kai gawa asibiti duk wani gwaje gwaje anyiwa gawa amma komai normal bata ci wata guba ba da wire ko igiya aka shaketa har ta mutu,Spark aka shiga nema lungu da sako babu Wanda yayi zaton Yana Office,sai da Yan sanda suka dangana da Building dinsa,gashi Baban Asmau ya musu alkawarin mahaukatan kudade na mamaki shi yasa suka dage.
Suna shiga ciki ko Ina a bude yake sabo da ma'aikatansa duk sun zo aiki,har Office dinsa suka shiga sai kallon tsaruwar office din suke,akwai Palo a ciki suka karasa a Nan suka same shi Yana ta bacci hankalinsa kwance kasancewar jiya baiyi bacci da wuri ba Yana ta aiki.
Tashinsa suka yi sun san da kudi shi yasa ba raini suka tashe shi,a hankali ya bude idonsa ya kallesu da uban yawa a kansa sun zagaye shi,kallonsu ya sake yi yace lafiya? daya daga ciki yace matarka Asmau....kafin ya rufe Baki Spark yace Allah yasa ta mutu na huta da mayya,me ya faru? Sheda ta Kuma tabbata sai suka fito da sarka tare da furta You are under arrest, ana tuhumarka da kashe matarka,Idanuwa Spark ya zaro yace kisa Kuma ni? Yaushe ma na kwana a gidan? Mamaki ya kamashi,Asmau ce ta mutu? Su dai yanda suka ce zai raina musu hankali ne kawai suka sakala Masa sarka a hannaye yace ba sai Kun sa min sarka ba zan iya binku normal cire min chain,ba musu suka cire Masa.
Spark yana furta innalillahi wa innailayhirrajun yaci gaba da cewa ko a lahira Allah karka hadani da Asmau, ya Allah ka gafartawa Asmau ka yafe mata,Allah ka gafarta mata irin shiga hakkina da tayi ta aure ni bada izinina ba l,Allah na yafe mata ka yafe mata,kansa ya jinjina yace uhhmmmm su Asmau an matsa min lamba Allah ya yafe miki,Sadakin ma sai da Papa ya biya min,Allah ya miki Rahma uhmm rabo to..dama ance rabo Yana kisa,sai da nace a hakura rabon wata ne aka ki ji, Yana magana ya tattara documents dinsa da kudadensa da duk wani Abu nasa me amfani ya fito dasu tare da Yan sandan motocinsu sunfi biyar suna ta jiniya.
Manager dinsa ya mikawa yace ka kaiwa Mummy kace ta ajiye min ba Mima ba Mummy nace,yace angama sir,ya shiga mota yaransa masu aiki a karkashinsa suna kallo Yan sanda suka tafi dashi.
Yana can aka sallaci Asmau tare da kaita makwanci,Yana motar Yan sanda ya Kalli Inspector guda yace iceko takaba bata hau kaina ba? sabo da tsabar ya raina musu hankali,Kuma wulakanci Spark ne,Yana da kudi to ba uwar da suka iya Masa,dama duk jaraba akan talaka take karewa, Spark sai kallon raini yake musu,suna ta Shan wulakanci iri iri.
Inspector yace Kai nifa Inspector ne,Spark yace no Inspectataatatatataaaa,yaja wani tsaki Kuma ba uwar da suka iya yi,shuru ya musu fuskar nana hade, har suka kaishi tare da tsare shi,ko tambaya suka Masa baya basu amsa a mutunce,shine ya Kara basu haushi sosai.
Duk wasu bincike an fara yinsu akan Spark amma ba hujja shi ya kashe Asmau,Baban Asmau kudi yake dannawa Yan sanda akan a Masa duka to shima Spark Yana da kudi Kamal Yana kawo kudi dole basa iya dukansa ko farcensa basa iya tabawa gashi tsagera Yana da kwarjini,Inda Allah ya saukaka ma da wuri Baban Asmau ya Kai Kara kotu ta can Lagos,ana ta faman bincike yaga zasu bata Masa lokaci ya Maida karar Kaduna,Nan ma yaga Spark ya fishi hanya ana ta daga sharia gashi ma za a bada bailing Spark,tsoro yaji kar ya cale kasar waje,yasa aka sake tsare shi sosai aka Maida case kotun dake Kano state.
Yayi hakane Dan ma kar Ashraf ya bada cin hanci a sake shi,duka dangi ma sai labari suka ji ai an Maida shi kano.
Wani mugun azzalumin Alkali ya samu sannan da lauyoyi azzalumai, Spark Yana tsare ba dama yayi katabus,Mummy duk kulla kullarta Baban Asmau ya fita gashi babban Soja ga kudi kamar yayi, gashi namiji ya fita basira,iyayen Spark da danginsa sunki shiga cikin case din sabo da spark ba Wanda ya kyale shi yasa suka kyale shi.
Mummy tace ka makara ka koyi sonta wlh yau saura kwana shida zaka ganta a gidanka,mikewa yayi Yana cika Yana batsewa hakarsa bata cimma ruwa ba,sai ya koma spark dinsa ya daure fuska Yana kunkuni ya fice cikin fushi dama kukan karya yayi ko za a tausaya Masa sai gashi ba nasara.
Spark Yana ta bincikensa akan Case din Naila ya zaiyi ya fitar da Jamilu a gidan yari ga matsalar aurensa,kamar wasa biki yazo ranar Friday za a daura Kuma a ranar za a Kai amarya ba wani biki za ayi ba sabo da Mummy tana takaba,Spark har ya hakura ma yace Allah yasa haka shine Mafi alkhairi ya zaiyi.
Ana gobe daurin aure tare suke da Kamal suna Hira, Spark yace na kyale yarinyar Nan sabo da son da take min,taci darajar Sona da take yi amma fa bazan ko hada room da ita ba wlh har ta gaji tace na sake ta shine kawai adalcin da zan iya,ni zan hada jiki ne da wacce zuciyata ke so wacce ta kwanta min a rai wacce bana kyankyami, Kamal zamuga wace Yar sa'ar Nan Yar gidan waye idan Kuma Asmau ce zata sace zuciyar to,Spark yace hmmm ya Kalli Kamal yace zaka Gani inshaallah,ai Asmau bazan taba sonta ba,ni ba abinda ta min kawai Allah bai sa min ko digon sonta ba,hasali ma a duniya ba wacce na tsana irinta.
Asmau kuwa Banda murna ba abinda takeyi,itakam shagali take matukar zata zauna gida daya da spark to rayuwa ta mata dadi ko da bazai kulata.
Washe gari Friday daurin auren Spark dukkan Yan uwa da abokan arziki sun hallara har abokinsa Kamal duk sun dauki wanka amma ba ango yace bazai je ba wlh,mahaifinsa da Mima mahaifiyarsu sunyi iya yinsu yaki zuwa,haka aka daura aure ba ango,shi Yana Office ma aikinsa yake ya kashe waya kar ma ayi Masa Allah sanya Alkhairi,haushi yake ji in akace Allah sanya Alkhairi, zuwa Yamma aka Kai Masa Amarya sai kace dole,amarya anci gayu an hade,har aka watse ango bai zo ba,shuru shuru haka Amarya ta mike tayi alwala tare da gabatar da sallah sannan tayi Shirin bacci ta kwanta abinta,Nawwar a ranar a Office dinsa ya kwana ma bai je gidan ba.
Asmau kuwa bayan ta kwanta bacci, sai da safe dangin Amarya suka zo zasu mata sallama zasu tafi garinsu amma sallamar duniya a palon ba a bude ba,har suka gaji tare da shiga ciki suka zauna a Palo nan ma shuru shuru,suka fara duba bedroom dinta sai kuwa suka hangota a kwance ta Kalli sama idonta a kafe,da sauri suka isa kanta suna tabata shuru har ta sandare ta kame, Dake akwai dattijai a ciki suka tabbatar ta rasu,wuyanta ga shatin igiya Nan da alama igiya aka sa tare da shake mata wuya har ta mutu,sai kuka da kuka suna cewa dama angon yace sai ya kasheta to kuwa da gaske ya kasheta shike nan sai bige bigen waya azo ango ya kashe Amarya ya gudu baya gidan ma.
Hankalin kowa ya sake tashi a family gaba daya,iyayen Spark kowa suka tattaro sai katafaren gidan Spark, Kamal ma da gudu yazo gidan,iyayen Asmau kuka suke suna cewa wallahi baza mu yarda ba,mahaifiyar Asmau ta fada kan gawa tana kuka tace Asmau...Asmau na....wayyo ya kashe min Yata bai San zafin haihuwa ba, Mummy da gudu ta shugo gidan tana wallahi Dana bazai yi kisa ba ban yarda ba karya ne sharri ne ta Fadi a kasa tana kururuwa,Mummy a duniya tana son spark ko uwar data haife shi baza ta fada mata son Spark ba,kamar ranta haka yake,tace wallahi da nasan haka zaku ce bazan daure gindin Spark ya auri Asmau ba.
Mutane ba Wanda ya yarda da Mummy duba da halin Spark da Kuma furucinsa Kuma an San baya karya shi yasa har iyayensa na gaskiya suka yarda, Baban spark shima Soja ne ya Kalli Baban Asmau yace kuyi bincike ku dauki mataki akan Ashraf ya girbi abinda ya shuka,Mima uwa to fa uwa ce amma Mummy ta fita son Spark itama tace idan an tabbatar shine a hukunta shi, sai kuka take tana cewa tabbas yara haihuwarsu jarabawa ce,mu iyaye muna ganin jarabawa akan yaran da muka haifa, Rafeeq zuwa yayi shima Yana ta al'ajabi amma bai yarda Spark zaiyi haka ba sabo da yasan halin Spark.
Baban Asmau dama kadan yake jira yasa aka Kai gawa asibiti duk wani gwaje gwaje anyiwa gawa amma komai normal bata ci wata guba ba da wire ko igiya aka shaketa har ta mutu,Spark aka shiga nema lungu da sako babu Wanda yayi zaton Yana Office,sai da Yan sanda suka dangana da Building dinsa,gashi Baban Asmau ya musu alkawarin mahaukatan kudade na mamaki shi yasa suka dage.
Suna shiga ciki ko Ina a bude yake sabo da ma'aikatansa duk sun zo aiki,har Office dinsa suka shiga sai kallon tsaruwar office din suke,akwai Palo a ciki suka karasa a Nan suka same shi Yana ta bacci hankalinsa kwance kasancewar jiya baiyi bacci da wuri ba Yana ta aiki.
Tashinsa suka yi sun san da kudi shi yasa ba raini suka tashe shi,a hankali ya bude idonsa ya kallesu da uban yawa a kansa sun zagaye shi,kallonsu ya sake yi yace lafiya? daya daga ciki yace matarka Asmau....kafin ya rufe Baki Spark yace Allah yasa ta mutu na huta da mayya,me ya faru? Sheda ta Kuma tabbata sai suka fito da sarka tare da furta You are under arrest, ana tuhumarka da kashe matarka,Idanuwa Spark ya zaro yace kisa Kuma ni? Yaushe ma na kwana a gidan? Mamaki ya kamashi,Asmau ce ta mutu? Su dai yanda suka ce zai raina musu hankali ne kawai suka sakala Masa sarka a hannaye yace ba sai Kun sa min sarka ba zan iya binku normal cire min chain,ba musu suka cire Masa.
Spark yana furta innalillahi wa innailayhirrajun yaci gaba da cewa ko a lahira Allah karka hadani da Asmau, ya Allah ka gafartawa Asmau ka yafe mata,Allah ka gafarta mata irin shiga hakkina da tayi ta aure ni bada izinina ba l,Allah na yafe mata ka yafe mata,kansa ya jinjina yace uhhmmmm su Asmau an matsa min lamba Allah ya yafe miki,Sadakin ma sai da Papa ya biya min,Allah ya miki Rahma uhmm rabo to..dama ance rabo Yana kisa,sai da nace a hakura rabon wata ne aka ki ji, Yana magana ya tattara documents dinsa da kudadensa da duk wani Abu nasa me amfani ya fito dasu tare da Yan sandan motocinsu sunfi biyar suna ta jiniya.
Manager dinsa ya mikawa yace ka kaiwa Mummy kace ta ajiye min ba Mima ba Mummy nace,yace angama sir,ya shiga mota yaransa masu aiki a karkashinsa suna kallo Yan sanda suka tafi dashi.
Yana can aka sallaci Asmau tare da kaita makwanci,Yana motar Yan sanda ya Kalli Inspector guda yace iceko takaba bata hau kaina ba? sabo da tsabar ya raina musu hankali,Kuma wulakanci Spark ne,Yana da kudi to ba uwar da suka iya Masa,dama duk jaraba akan talaka take karewa, Spark sai kallon raini yake musu,suna ta Shan wulakanci iri iri.
Inspector yace Kai nifa Inspector ne,Spark yace no Inspectataatatatataaaa,yaja wani tsaki Kuma ba uwar da suka iya yi,shuru ya musu fuskar nana hade, har suka kaishi tare da tsare shi,ko tambaya suka Masa baya basu amsa a mutunce,shine ya Kara basu haushi sosai.
Duk wasu bincike an fara yinsu akan Spark amma ba hujja shi ya kashe Asmau,Baban Asmau kudi yake dannawa Yan sanda akan a Masa duka to shima Spark Yana da kudi Kamal Yana kawo kudi dole basa iya dukansa ko farcensa basa iya tabawa gashi tsagera Yana da kwarjini,Inda Allah ya saukaka ma da wuri Baban Asmau ya Kai Kara kotu ta can Lagos,ana ta faman bincike yaga zasu bata Masa lokaci ya Maida karar Kaduna,Nan ma yaga Spark ya fishi hanya ana ta daga sharia gashi ma za a bada bailing Spark,tsoro yaji kar ya cale kasar waje,yasa aka sake tsare shi sosai aka Maida case kotun dake Kano state.
Yayi hakane Dan ma kar Ashraf ya bada cin hanci a sake shi,duka dangi ma sai labari suka ji ai an Maida shi kano.
Wani mugun azzalumin Alkali ya samu sannan da lauyoyi azzalumai, Spark Yana tsare ba dama yayi katabus,Mummy duk kulla kullarta Baban Asmau ya fita gashi babban Soja ga kudi kamar yayi, gashi namiji ya fita basira,iyayen Spark da danginsa sunki shiga cikin case din sabo da spark ba Wanda ya kyale shi yasa suka kyale shi.