Sashe 1
Tantiriya A Gidan Yari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
[12/4/2023, 2:39 AM] AsmaBaffa: 🏫 TANTIRIYA 🏫
A GIDAN YARI
Official
By
AsmaBaffa
SADAUKARWA
GARE KI ❤️
AIDA MAMAN TASNIM
1-5
INA GODIYA GA ALLAH DA YA BANI IKON FARA SABON LITTAFIN NAN
INA MIKO GAISUWA DA JINJINA GA MASOYA MASU BIBIYAR NOVELS DINA INA MUKU ADDUA ALLAH YA AMSA MUKU BUKATUNKU BAKI DAYA DA WANDA NA SANI DA WANDA MA BAN SAN SU BA.
Page naki ne
MRS CHIEF
*👭GARKUWAR MATA👭*
*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa! kuma muna bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi💯
Nono💯
Sanyi💯
Karin kiba💯
girmar hips💯
Ni'ima💯
Sabulai💯
Humra💯
Turarukan wuta💯
Matsi💯
Miski💯
Dilka💯
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI
08089965176
07084653262
BISMILLAH
GA MASU AUDIO..BAN YARDA A JUYA MIN NOVEL ZUWA AUDIO BA.
Gidane me kyau Dan madaidaici da shi na rufin asiri haka gidan yake a unguwa wacce take ta masu rufin asiri daidai gwargwado,gidan dauke yake da dakuna hudu sai Palo da toilet a tsakar gida guda biyu ko Ina siminti ne Palo da toilet ne kawai da tiles, gidan dai babu makusa Dake cikin birnin Kano, wani matashi ne kyakyawan gaske da shi, fari amma haskensa ba can ba a kalla zai Kai 31yrs,dauke da sallama ya shigo gidan hannunsa rike da Yar yarinya wacce zata Kai 3yrs itama yarinya kyakyawa wacce ke kama da matashin me suna Mohsin.
Yaran gidan ne suka Masa sannu da zuwa Yaya Mohsin,murmushi yayi ya amsa,Hidaya ce tazo ta rike Masa hannu suka shiga palon gidan,bayan sun gaisar da shi yace Umma fa? Hidaya Ido ta runtse sabo da kunya tana danne dariyarta tace Yaya wai ta tafi shako warin gardi kasan cikin da Umma ta samu ita me son wari ne,ban gane ba Mohsin ya tambaya,Hidaya ta sake fashewa da dariya tace kaga Yaya Umma tayi tayi akan lallai Abba sai ya daina wanka sabo da ta samu warin hammatarsa ta shaka Yana sata nutsuwa amma yaki sam sai yayi wanka, bata Jin warin shine take ficewa wajen masu aikin gini ta Dan sinsino sai ta dawo,wlh munyi munyi amma taki dainawa gashi Aunty Naila tana gidan yari, itace dama zata iya taka mata birki, Mohsin shi kanshi mamaki yake yi wai duk cikin da Ummansu ta samu ne yasa ko yaushe ita dai ta shaki warin gardi shine dai dai, suna zancen sai suka ji Muryar Umma tayi sallama ta shugo sanye cikin doguwar riga bubu me Fadi ta silk material ta yafa mayafin sai cikinta kato a gaba, sai wani annuri take yi da nishadi.
Palon ta shugo ta zauna tana furta wash Alhmdllh dadi ya ratsani amma gardin nan kazami ne na gaske malam na shaki irin Wanda nake so,Mohsin ya Kalli mahaifiyarsu yace Yanzu Umma da aurenki da mijinki amma kije shakar wani warin gardi duk da ciki ne ya jawo ai bai dace ba, Kubra wacce suke kira da Umma tace ahhh kaga laifina? Ubanku tsaftar tsiya gare shi nayi nayi ya fasa wanka na kwana uku yaki yarda ai kuwa dole na fice Inda zan samu kwanciyar hankali,tunda nake fita sai yau nayi dace na shaki irin Wanda nake so tun da ya daga hammatarsa mallam sai naji wata nutsuwa,Umma tana labarin har wani lumshe Ido takeyi tana cewa wlh wani ni'ima da salama sai wani ratsani take,duk damuwar da nake ciki ta garkame Naila a gidan yari sai naji ta yaye yau bacci harda munshari,idan Kuma Bakin ciki kake min to ka daina wanka da aske hammata kazo na dinga shakar warin naka,Mohsin ya yatsina fuska yace Allah ya kiyaye min,Umma tace Ina Hanan matar taka? Mohsin yace tana Nan lafiya.
Uhmm wannan matar taka marowaciya ita ko irin kyautar nan da ake yiwa surukai a dan siye suruka bata yi,sisinta banci ba me za ayi da mace irin Hanan,Mohsin yace haba Umma duk irin girmamakin da take yi ai shi ake so...kafin ya rufe Baki Umma tace a'a ai babban girma shine Yan kyaututtuka a zamanin Nan waye yake yayin wani girmamawa ai kawai ace ungo shine girma
Canja zancen Mohsin yayi yace Umma yaushe zamu je ziyarar Naila Kinga ta kusa sati daya a gidan yari ya kamata muje,Umma tace ba Wanda zai je mata da wuri ita tasan me ta aikata dama Naila a rashin jinta nasan zata aikata sabo da haka kar Wanda yaje sai ta gane kurenta,Mohsin yace haba Umma haka ma fa Abba yace bazai je ba ko su Hidaya duk babu Wanda zaije mata,sharri aka mata ni ban yarda Naila zata iya kisan Kai ba,nace babu Wanda zai je duk Wanda yaje ko ban sani ba ban yafe muku ba,Naila da tuntuni take da samari na kirki masu kudi Inda zamu huta wannan solobuyon uban naku dolo ne ba abinda ya iya, nace ta zabi daya ta aura taki ai gashi nan yanzu garin shegen kinibibi da taurin kanta ya ja mata,ni na haifi Naila amma kowa yasan halinta bata ji ga taurin Kai,gaba daya Dana sanin kaita wajen ubana nake,ya gama kashe min yarinya,idan na tuna Alhaji Ibrahim da yake son auren Naila amma ta koreshi mutumi me kudi taki yarda da shi idan na tuna abin nan sai naji Naila ta sire min....Umma ta saki kuka yiiiii.....tace raina baci yake,cikin masifa tana zaro Idanuwa nace sabo da haka ba Wanda zai je mata.
Yarinyar Nan sabo da rashin gaskiya ta fita da atamfa a jikinta suka tafi ashe aski taje aka mata tayi shigar Maza kawai Dan ta siyar da magani,gashi Nan taje gidan yari bangaren Maza a matsayin namiji Dandaudu yanzu so kuke muje a tona mata asiri cewar macece? Billahillazi idan suka gano duk sai kotu taci kwal uban mu
Mohsin Yana mamakin halin Ummansu yace amma Umma da taje Abuja Inda kaddarar ta fada mata ba kece kika ce taje ba tunda Abuja ne zata samo kudi,Sai nace taje ta shiga matsalar me gida? Kaga karka dameni wallahi zan dura Maka ashar tashi ka ja yarka ku bar min gida,Mohsin mikewa yayi Yana gyara Karin gugan shaddarsa milk ya dauki Amal yarsa ya sabata a kafada ya bar gidan ransa a bace.
Direct Inda babansa yake aikin gadin petrol din turawa da suke aikin kwalta da shi,can ya nufa da yamma likis,Babansu irin dolayen Nan Wanda haka Allah ke hallitarsu, wasu gasu nan ne dai,Mutane suna zuwa satar petir din shi yasa suka zuba masu gadi,yau abokan aikin nasa basu zo ba sai dare shi dama da safe yake nasa zuwa yamma,Yan iskan gari ganinsa wani dolo sai suka Masa wayo suka samo aron jaki harda Mangala a Saman jakin sai kace a kauye suka zubo gallon 50ltr guda biyu suka taho Abban su Naila yana can Yana dolancinsa ya wani kwanta a Jikin bishiya ya saki baki har suka zo suka saka tiyo suka ja petir din sai da suka cika jarkokinsu sun Dora tsaf a Saman jakin kenan ya farka,daga nesan ya musu magana Kai lafiya barayine? Matasan barayin petir suka ce a'a dama petir muka kawowa turawa ko zasu siya, da masifa ya dinga korasu da hannaye Yana ku tafi ba'a so ba'a so baza su siya ba shegu sarakan son kudi sabo da a siya da araha ku tafi,suka juya da jakin da jarkokinsu cike da petir din da aka sashi gadi,Mohsin yaga duk abinda ya faru Yana Saman lifan dinsa da yarsa Amal a gabansa shi kanshi wannan abin na Abbansu ya bashi dariya matuka mutane sun saci petir Yana kwance Kuma sun Masa wayo kiri kiri ya kore su da kansu,barayin suma suna barin wajen suka tsaya suka dinga sheka dariya kamar ba gobe gashi motar tank ce ta petir bare a gane an sata.
Mohsin nan ya karaso wajen Abban nasa sannan ya sauka daga kan machine din,Abban nasu ya kalle shi yace Mohsin idan na kalleku sai naga kamar ba ni na haife ku ba kyawawan yara Yan gayu ga nutsuwa kar dai ace na yabi kaina amma na iya tarbiyya,dariya Mohsin yayi yace Abba Kaine mana kana gani muna kama ma,Abba yace a'a yanda nake kamar birin da ake wasa da shi ta ya muka yi kama gaku dogaye charas da ku amma ni kana gani kafata ma kamar fatar Kura,Mohsin Yana ta dariya ya gaida Abban nasa yace Abba wai baza aje wajen Naila bane?
A GIDAN YARI
Official
By
AsmaBaffa
SADAUKARWA
GARE KI ❤️
AIDA MAMAN TASNIM
1-5
INA GODIYA GA ALLAH DA YA BANI IKON FARA SABON LITTAFIN NAN
INA MIKO GAISUWA DA JINJINA GA MASOYA MASU BIBIYAR NOVELS DINA INA MUKU ADDUA ALLAH YA AMSA MUKU BUKATUNKU BAKI DAYA DA WANDA NA SANI DA WANDA MA BAN SAN SU BA.
Page naki ne
MRS CHIEF
*👭GARKUWAR MATA👭*
*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa! kuma muna bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi💯
Nono💯
Sanyi💯
Karin kiba💯
girmar hips💯
Ni'ima💯
Sabulai💯
Humra💯
Turarukan wuta💯
Matsi💯
Miski💯
Dilka💯
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI
08089965176
07084653262
BISMILLAH
GA MASU AUDIO..BAN YARDA A JUYA MIN NOVEL ZUWA AUDIO BA.
Gidane me kyau Dan madaidaici da shi na rufin asiri haka gidan yake a unguwa wacce take ta masu rufin asiri daidai gwargwado,gidan dauke yake da dakuna hudu sai Palo da toilet a tsakar gida guda biyu ko Ina siminti ne Palo da toilet ne kawai da tiles, gidan dai babu makusa Dake cikin birnin Kano, wani matashi ne kyakyawan gaske da shi, fari amma haskensa ba can ba a kalla zai Kai 31yrs,dauke da sallama ya shigo gidan hannunsa rike da Yar yarinya wacce zata Kai 3yrs itama yarinya kyakyawa wacce ke kama da matashin me suna Mohsin.
Yaran gidan ne suka Masa sannu da zuwa Yaya Mohsin,murmushi yayi ya amsa,Hidaya ce tazo ta rike Masa hannu suka shiga palon gidan,bayan sun gaisar da shi yace Umma fa? Hidaya Ido ta runtse sabo da kunya tana danne dariyarta tace Yaya wai ta tafi shako warin gardi kasan cikin da Umma ta samu ita me son wari ne,ban gane ba Mohsin ya tambaya,Hidaya ta sake fashewa da dariya tace kaga Yaya Umma tayi tayi akan lallai Abba sai ya daina wanka sabo da ta samu warin hammatarsa ta shaka Yana sata nutsuwa amma yaki sam sai yayi wanka, bata Jin warin shine take ficewa wajen masu aikin gini ta Dan sinsino sai ta dawo,wlh munyi munyi amma taki dainawa gashi Aunty Naila tana gidan yari, itace dama zata iya taka mata birki, Mohsin shi kanshi mamaki yake yi wai duk cikin da Ummansu ta samu ne yasa ko yaushe ita dai ta shaki warin gardi shine dai dai, suna zancen sai suka ji Muryar Umma tayi sallama ta shugo sanye cikin doguwar riga bubu me Fadi ta silk material ta yafa mayafin sai cikinta kato a gaba, sai wani annuri take yi da nishadi.
Palon ta shugo ta zauna tana furta wash Alhmdllh dadi ya ratsani amma gardin nan kazami ne na gaske malam na shaki irin Wanda nake so,Mohsin ya Kalli mahaifiyarsu yace Yanzu Umma da aurenki da mijinki amma kije shakar wani warin gardi duk da ciki ne ya jawo ai bai dace ba, Kubra wacce suke kira da Umma tace ahhh kaga laifina? Ubanku tsaftar tsiya gare shi nayi nayi ya fasa wanka na kwana uku yaki yarda ai kuwa dole na fice Inda zan samu kwanciyar hankali,tunda nake fita sai yau nayi dace na shaki irin Wanda nake so tun da ya daga hammatarsa mallam sai naji wata nutsuwa,Umma tana labarin har wani lumshe Ido takeyi tana cewa wlh wani ni'ima da salama sai wani ratsani take,duk damuwar da nake ciki ta garkame Naila a gidan yari sai naji ta yaye yau bacci harda munshari,idan Kuma Bakin ciki kake min to ka daina wanka da aske hammata kazo na dinga shakar warin naka,Mohsin ya yatsina fuska yace Allah ya kiyaye min,Umma tace Ina Hanan matar taka? Mohsin yace tana Nan lafiya.
Uhmm wannan matar taka marowaciya ita ko irin kyautar nan da ake yiwa surukai a dan siye suruka bata yi,sisinta banci ba me za ayi da mace irin Hanan,Mohsin yace haba Umma duk irin girmamakin da take yi ai shi ake so...kafin ya rufe Baki Umma tace a'a ai babban girma shine Yan kyaututtuka a zamanin Nan waye yake yayin wani girmamawa ai kawai ace ungo shine girma
Canja zancen Mohsin yayi yace Umma yaushe zamu je ziyarar Naila Kinga ta kusa sati daya a gidan yari ya kamata muje,Umma tace ba Wanda zai je mata da wuri ita tasan me ta aikata dama Naila a rashin jinta nasan zata aikata sabo da haka kar Wanda yaje sai ta gane kurenta,Mohsin yace haba Umma haka ma fa Abba yace bazai je ba ko su Hidaya duk babu Wanda zaije mata,sharri aka mata ni ban yarda Naila zata iya kisan Kai ba,nace babu Wanda zai je duk Wanda yaje ko ban sani ba ban yafe muku ba,Naila da tuntuni take da samari na kirki masu kudi Inda zamu huta wannan solobuyon uban naku dolo ne ba abinda ya iya, nace ta zabi daya ta aura taki ai gashi nan yanzu garin shegen kinibibi da taurin kanta ya ja mata,ni na haifi Naila amma kowa yasan halinta bata ji ga taurin Kai,gaba daya Dana sanin kaita wajen ubana nake,ya gama kashe min yarinya,idan na tuna Alhaji Ibrahim da yake son auren Naila amma ta koreshi mutumi me kudi taki yarda da shi idan na tuna abin nan sai naji Naila ta sire min....Umma ta saki kuka yiiiii.....tace raina baci yake,cikin masifa tana zaro Idanuwa nace sabo da haka ba Wanda zai je mata.
Yarinyar Nan sabo da rashin gaskiya ta fita da atamfa a jikinta suka tafi ashe aski taje aka mata tayi shigar Maza kawai Dan ta siyar da magani,gashi Nan taje gidan yari bangaren Maza a matsayin namiji Dandaudu yanzu so kuke muje a tona mata asiri cewar macece? Billahillazi idan suka gano duk sai kotu taci kwal uban mu
Mohsin Yana mamakin halin Ummansu yace amma Umma da taje Abuja Inda kaddarar ta fada mata ba kece kika ce taje ba tunda Abuja ne zata samo kudi,Sai nace taje ta shiga matsalar me gida? Kaga karka dameni wallahi zan dura Maka ashar tashi ka ja yarka ku bar min gida,Mohsin mikewa yayi Yana gyara Karin gugan shaddarsa milk ya dauki Amal yarsa ya sabata a kafada ya bar gidan ransa a bace.
Direct Inda babansa yake aikin gadin petrol din turawa da suke aikin kwalta da shi,can ya nufa da yamma likis,Babansu irin dolayen Nan Wanda haka Allah ke hallitarsu, wasu gasu nan ne dai,Mutane suna zuwa satar petir din shi yasa suka zuba masu gadi,yau abokan aikin nasa basu zo ba sai dare shi dama da safe yake nasa zuwa yamma,Yan iskan gari ganinsa wani dolo sai suka Masa wayo suka samo aron jaki harda Mangala a Saman jakin sai kace a kauye suka zubo gallon 50ltr guda biyu suka taho Abban su Naila yana can Yana dolancinsa ya wani kwanta a Jikin bishiya ya saki baki har suka zo suka saka tiyo suka ja petir din sai da suka cika jarkokinsu sun Dora tsaf a Saman jakin kenan ya farka,daga nesan ya musu magana Kai lafiya barayine? Matasan barayin petir suka ce a'a dama petir muka kawowa turawa ko zasu siya, da masifa ya dinga korasu da hannaye Yana ku tafi ba'a so ba'a so baza su siya ba shegu sarakan son kudi sabo da a siya da araha ku tafi,suka juya da jakin da jarkokinsu cike da petir din da aka sashi gadi,Mohsin yaga duk abinda ya faru Yana Saman lifan dinsa da yarsa Amal a gabansa shi kanshi wannan abin na Abbansu ya bashi dariya matuka mutane sun saci petir Yana kwance Kuma sun Masa wayo kiri kiri ya kore su da kansu,barayin suma suna barin wajen suka tsaya suka dinga sheka dariya kamar ba gobe gashi motar tank ce ta petir bare a gane an sata.
Mohsin nan ya karaso wajen Abban nasa sannan ya sauka daga kan machine din,Abban nasu ya kalle shi yace Mohsin idan na kalleku sai naga kamar ba ni na haife ku ba kyawawan yara Yan gayu ga nutsuwa kar dai ace na yabi kaina amma na iya tarbiyya,dariya Mohsin yayi yace Abba Kaine mana kana gani muna kama ma,Abba yace a'a yanda nake kamar birin da ake wasa da shi ta ya muka yi kama gaku dogaye charas da ku amma ni kana gani kafata ma kamar fatar Kura,Mohsin Yana ta dariya ya gaida Abban nasa yace Abba wai baza aje wajen Naila bane?