Sashe 44
Soyayya Da Izza Part 1 Complete Hausa Novel · about 10 min read
SOYAYYA DA IZZA
Story and writing by Hadizatu
Mrs (KD)
Ina masu bibiyar books dina
to ina muku albishir da sabon book dina
dana fara rubutawa
me suna YAN BIYU NE ina baku shawara ku bibiye book din nan
dan akwai chakwakwa kiya kala kala zaku nishadantu
zakuma ku wa'azantusosai kudai kawai ku bibiye kafun free page yakare ku biya kan naira
300 kacal ba tsauwalawa
ina alfahari daku
masoyana
kune kwarin gwuiwa ta
i love you so much
my pans
ina godiya da addu'o'in ku
dayacce kuke yabon book dina
duk da shine nafarko, gudiya buhu buhu
nice taku har kullum Hadizatu wacce kukafi sani da (MRS K D) kucika da bibiyata nukuma zanci gaba da nishadantan daku
https://chat.whatsapp.com/FPb99RjggTbAcCFg1aFrVx
page 43
________________Karfe 2:00pm aka fara shirye shiryen kai amarya, bayan kowa ya shirya, su Abba sukace suna bukatar ganin matan zasuyi magana dasu, haka suka rankaya gaba daya suka nufi part din daddy, bayan sunje kowa yanemi guri yazauna, Abba ne yayi gyaran murya kana yace, "ba komai ne yasa muka tara ku ba illa kan maganar auren Ahmad damuka riga muka yanke shawara iya mu, kawai dai zamu fada muku ne a matsayinku na iyayensu mata, Ahmad yazo mana dazancen yanason yarinyar gurin Habiba matar Alhaji Aminu wato dake zaune agida na Zuhura kenan" mom ce ta waro ido tanasan jin karashen zancen "mun fahimci yarannan suna san junansu hakan yasa muka yanke shawarar hadasu aure kamar yadda Ahmad ya bukata" Daddy yafada, "ke kuma kiyi hakuri naba da yarinyarki batare dana ji ta bakinki ba, amma idan bakiso bazamuyi maki dole ba tunda yarinyar kice" Abba ya karashe maganar yana kallon Innna, baki ta bude tace "aini duk abunda kuka yanke akan ya'ya na to bani data cewa saboda bamu da tamkarku, Allah yabasu zaman lafiya" ammeen kowa ya amsa banda mom data cika tayi fam, "amma ni Ahmad be taba sanar dani yanason Zuhura ba" Mamy tayi maganar, Hajiya ce tace "to yanzu yaushe kuka sa bikin"? "Hajiya munyanke idan ta kammala secondary za ai" "to hakan yayi" tunda aka fara mom ce kawai batace kala ba, har aka tashi, Allah Allah take taga Ahmad dan fada na cinta, sedai har aka futo kai amarya bata ganshi ba, futowa akai Ilham tasha alkyabba se kamshi take, aka sata a mota, kodan kukan amarenan ma ita batayi, su Zuhura ma duk suka shiga mota ita da Yasmeen, bawanda yaje raka amarya, saboda ga su Mamy ga Hajiya ga aunty Aisha ga Innar Zuhura, shi Ammar su Abba ya diba da Alhaji Aminu yajasu suka tafi, Ahmad kam sun rigada sunyi sallama da Zuhura, a haka dai suka dau hanyar Kaduna,
basu wani dau lokaci ba suka isa, Mamy ce tace kar a kai Ilham yanzu abari se dare zatayi yar walima kawayenta da ke nan zasuzo, haka a ka fara shirye-shiryen walima, shikam Ammar part dinsa yawuce ya kulle bema san me sukeyi ba, Zuhura Yasmeen da Amira taja suka nufi dakinta, nan sukai wanka suka huta, kana suka kara shiryawa, suka futo gurin walima, malamai Mamy ta gayyato mata sukazo sukai, nasiha, ba laifi ancika sosai, ilham kam wani kayan takara sawa, ba a tashi ba se karfe 6:30pm lokacin za a kira sallar magaruba, futowa yayi dan ya tafi masallaci yaga mutane, be tsaya tambaya ba ya sa kai yafuce, bayan yadawo sallah, still yakoma part dinsa, wanka yashiga, inda yayi wanka yafuto yazauna ya shirya tsaf cikin shadda ruwan omo yayi matukar kyau sosai se tashin kamshi yake, jin cikinsa yayi fayau ba komai, hakan yasa yadau waya ya danna kiran Mamy, tana dagawa tace "son ya akai" "Mamy yunwa nakeji" "ok bara nace Jummai ta hada ma" "Mamy ta hada tabawa Zuhura ta kawo mun" "ok naji zata kawo ma" daga haka Mamy ta kashe wayar, falour tashiga tasamesu gabadayan su a zaune tace "Zuhura jeki gurin Jummai kice tahadama Ammar abinci ki mikamai" amsawa tayi tana mikewa, Mamy taci gaba da sallamar bakin ta, se bayan kowa yatafi tashiga bedroom dinta tayi alawala tayi sallah, sukam su Inna da aunty Aisha tuni sunyi sallar su , bayan tayi tafuto falour tasamesu, "ace Ilham tafara shiryawa time yayi" aunty Aisha ce ta mike tanufi bedroom din Ilham, ita kuma Inna tana zaune , bayan Jummai tahada mata abincin takarba tanufi part dinsa danta kaimai, kofar abude take hakan yasa ta tura tashiga, tana shiga taganshi zaune kan kujera yana kallo, yamata kyau sosai, zuciyarta ce tace mata 'kin manta ango ne fa' wata zuciyar kuma tace 'dama can kullum shi cikin kyau yake' jin shirun yayi yawa yasashi kallon bakin kofar, tana tsaye tana kallonshi katseta yayi da cewa "kona zo na karba ne" dasauri ta dawo daga duniyar tunanin ta wuce ciki, ajiyewa tayi saman centre table, kana tadau plate tafara zuba mai, bayan ta zuba takoma gefe ta tsaya, zauna yafada yana kallonta, zama tayi, shi kuma yafara cin abincin, yanaci yana kallonsa ta kagu yagama ta kwashe kayan tafuce "dagaske kina son Ahmad" tambayar ta doki dodon kunnenta, saurin kallonsa tayi taga bama ita yake kallo ba television din dake falourn yake kallo, shiru tayi ta sunkuyar da kanta, tana wasa da yatsun hannunta, kallonta yayi yace "bake nake tambaya ba" ji take kamar ta kurma ihu saboda kunya, to ita me zata ce, ganin tayi shiru yasashi cewa "ok kina son shi kenan, kuma zaki aure shi, yayi kyau" ita dai bata dago kai ba, amma kana ganin ta kasan amasar eh ce, cokalin ya dire kan plate din, har yana bada sauti, kana yakoma ya jingina da kujera ya rufe idanunsa, baki yabude yace "dauki abincin kije" bata kawo komai ba tamike da sauri tadebe tafuce, ya jima idansa a rufe zuciyarsa na tafarfasar kishi,
kai amarya aka fara tafiya, hakan yasa Zuhura shigewa daki dan batason zuwa, sukam su Inna daga can gida zasu wuce, haka aka ranka ya aka tafi, gidan ta yayi kyau ba karya, falourn ya hadu, saman bene aka wuce da ita, aka kaita dakinta, su aunty Aisha ne sukai mata nasiha sosai kana suka rankaya suka wuce gida, aka barta ita da kawayenta su uku, su Inna gida suka wuce, dansun gaji likis, ita kuma aunty Aisha tabi su Muhsin suka koma gida, dawuri tayi shirin bacci ta kwanta danta gaji, aikam tuni bacci ya dauke ta, Ammar kam har 11:00pm be tafi ba, seda Mamy da aunty Aisha suka bishi part dinsa, suka sameshi, haryanzu yana yadda yake, sallamar suce tasashi bude ido, yana kallonsu, zama sukayi, kana Mamy tafara magana "son yakamata katashi kaje ankai amarya tun dazu" shiru yayi bece komai ba, kafadarsa Mamy ta dafa tana fadin "Please ka daure ka sauke nauyin da Allah ya dora ma, Ilham yar uwar kace, ko yaya kayi wani abu akanta bazanji dadi ba, ko kanaso ka ganni cikin bacin rai" kada mata kai yayi alamar aha ah "to please ka taimaka mun katashi katafi gidan ka" "kwarai kuwa Ammar yanzu ba kai kadai bane koya zaka iya yin abunda zaka tauye mata hakkin ta kuma kashiga fushin ubangiji" jikinsa ne yayi sanya, hakan yasa yakama hannun Mamy yace "no Mamy base kun rokeniba zanyi abunda kuka ce" "yawwa muje nabaka kayan da aka siyo ka tafi dashi" aunty Aisha tayi maganar, daga haka yamike, kazar dasuka sa asiyo da sauran abubuwa suka mika mai, kana ya musu se da safe yawuce, motarsa ya hau yanufi gidansa, yana zuwa yayi horn me gadi ya wangale mai gate ya shiga, bayan yashiga ya tarar ba kowa a falour hakan yasa ya haye sama, hayaniyarsu yaji, kofar ya isa yatura, suna zazzaune kan bed din, karasawa yayi, kowacce acikin su ta zuba mai idanu, zama yayi yana kallon Ilham yace "me suke har yanzu" "am dama siyan baki suka tsaya" "me baki da hankali ko" tsuru tsuru tayi da ido, ya kallesu yace "ku tashi ku tafi" da sauri kowaccen su taja jakarta suka fuce, bayan sun futa, Feenat takalle su tace "gaskiya yanzu na dena ganin laifin Ilham akan son guy dinan, kut gaskiya ya hadu" "ashe bani kadai nake kallonsa ba, ai dar ne gurin kyau" "nifa wlh nasamu wannan ko da duka sena zauna dan babu abunda babu atare dashi" harsuka shiga mota suna gulmarsa,
ledar ya ajiye mata saman bed yace "gashinan ki dauka kici nasan kinajin yunwa nina wuce dakina se da safe" kafun tayi wata magana har ya bude kofa yafuce" ledar ta kalla kana ta bankade mayafin kanta, tana fadin "wai me wannan mutumin ke nufi ne" yana shiga dakinsa yafada toilet yayi wanka yadau kayan bacci yasa kana ya kwanta da tunaninta a karkashin ransa,
yau bata iya tashi da wuri ba saboda gajiyar da tayi, se karfe 9:00am ta tashi, tayi wanka tashirya ta futo, kitchen tanufa, Mamy ce da aunty Aisha se Jummai dake wanke wanke, Mamy ta tsugunna ta gaisar kana ta gaida aunty Aisha kana ta gaida Jummai, "Mamy ba abunda zan taya ku" "ah ah Zuhura mun kammala ai" daga haka tafuce, aunty Aisha ce takalli Mamy tace "aunty Khadija yarinyar na birge ni akwai hankali" "ah ai Zuhura akawai hankali" bayan sun kammala breakfast, Mamy ta hada a basket tabawa driver yakai gidan Ilham, sukuma suka shirshiriya kan dinning, duk suka hallara suna breakfasta din,
me gadi Bala driver yamikawa ya shigar dashi ciki, dama Mamy ta sanarwa da Ilham za akawo musu, hakan yasa tafuto ta karba, zama tayi a falaour, tazuba taci, kana ta kunna tv tana kallo, se karfe 11:00am yatashi, yana tashi yayi wanka yashirya, yafeshe jikinsa da turare, key dinsa yadauka da wayar sa ya fuce, beyi tunanin shiga bedroom dinta ba, ya sakko da niyayar yafuta, samunta yayi kwance kan kujera, ga kulolin abincin duk a bude, ga jarkokin lemo akasa ta zubar da ledojin chocolate din data shashsha, tsayawa yayi yana kallonta, bama tasan yana kanta ba, hakan yasa takara jefar da ledan data gama cin chocolate din, baki ya bude yace "meye haka kika mayar da falour kamar bola" saurin mikewa tayi tana fa
in oh katashi ashe, "tambayar ki nake" "idan natashi zan kwashe ai" "kije ki gyara mun bedroom dina" wani kallo tamai kana ta kawar da kai, shi kuma yasa kai ze fuce, da sauri tace "bakai breakfast ba fa" juyowa yayi ya kalli kulolin abincin dukansu a bude kana yakalle ta yace "ahaka zanyi breakfasts din" kana ya fuce, waige waige take dan ita bataga abunda tayi ba, komawa tayi ta kwanta, tana cigaba da shan alawoyinta
bayan yafuta gida yanufa, yana zuwa ya tarar da Abba ze futa, gaisawa sukai, kana yashiga cikin gidan, duk suna falour banda Zuhura da tanacan tana bitar karatun islamiyya dan sunfara screening din sauka, asabar ta gaba za a gudanar da saukarsu, zama yayi kana ya gaishe su gaba daya, suka amsa, aunty Aisha ce takalle shi tace "ah ah naganka da sassafe" "aunty zanje office ne" "bazaka bari ka gama cin amarcin ba" "aunty aimu aikinmu ba a mai haka na ceton rai ne" "gaskiya kam naceton rai ne" Hajiya tayi maganar tana kallonshi "Mamy inason coffee" "ok Muhsin ina Zuhura ta hada mai" anzo gabar da yake so dama ita yakeson gani, "Mamy tanacan tana bita na screening din saukar mu" "oh hakane fa to fadawa Jummai ta hada mai" amsawa Muhsin yayi yana mikewa, kallon Mamy Ammar yayi yace "saukar me kuma" "next week saukar sufa" girgiza kai kawai yayi, Jummai ce tazo dauke da cup din coffee din, tdugunnawa tayi ta gaishe shi ya amsa kana ta mikamai, karba yayi ya fara sha,
seda ta tabbatar karatunta ya zauna ba gargada, futowa tayi, daga dakin nata, falour ta nufa, lokacin shikuma ya mike ze tafi, karasowa falourn tayi, tana zama kusa da Mamy, kallonshi tayi tace "ina kwana" batare daya kalle taba yace "lafiya lau" daga haka yace "Mamy zan wuce" Muhsin ne yazo yana fadin "yaya Zuhura ana nemanki a waya" yafada yana mikamata wayar, karba tayi takara a kunnenta, kawarta ce ta islamiyya takira tace Muhsin y hadata da Zuhura, mikewa tayi ta bar gurin, da kallo Ammar yabita, zuciyarsa ce tace 'watakila fa yarinyar nan Ahmad ne yakirata' "me kake kallo kuma kace kuma katafi" Hajiya tafada tana kallon sa, se lokacin yadawo hayyacinsa, daga haka yasa kai yafuce, bayan ta gama wayar tazo takawowa Muhsin wayarsa,
"ai naga yaron ba laifi yanada hankali shima" "to nidai kawai sedai nace Allah yabasu zaman lafiya tunda tanasansa" "ammeen dai" "yawwa nace inasan naje gurin yaya ta, rabona da ita tunda muka rabu" "hakan yayi kyau yaushe kenan zakije" "da sonake bayan saukar Zuhura, muje tare tunda yanzu makaranta, kaga sena sanar da ita ansa ranar auren Zuhura" "gaskiya kam idan zakuje sai direba ya kaiku" "to shikenan" "bara natashi na wuce karna makara" daga haka ya mike ita kuma tabishi abaya dan ta rakashi, su Yasmeen ne a falourn suna zaune suna kallo, adawo lafiya sukai mai gaba-daya, yafuce, har bakin mota Inna ta rakashi, kana ta dawo
Story and writing by Hadizatu
Mrs (KD)
Ina masu bibiyar books dina
to ina muku albishir da sabon book dina
dana fara rubutawa
me suna YAN BIYU NE ina baku shawara ku bibiye book din nan
dan akwai chakwakwa kiya kala kala zaku nishadantu
zakuma ku wa'azantusosai kudai kawai ku bibiye kafun free page yakare ku biya kan naira
300 kacal ba tsauwalawa
ina alfahari daku
masoyana
kune kwarin gwuiwa ta
i love you so much
my pans
ina godiya da addu'o'in ku
dayacce kuke yabon book dina
duk da shine nafarko, gudiya buhu buhu
nice taku har kullum Hadizatu wacce kukafi sani da (MRS K D) kucika da bibiyata nukuma zanci gaba da nishadantan daku
https://chat.whatsapp.com/FPb99RjggTbAcCFg1aFrVx
page 43
________________Karfe 2:00pm aka fara shirye shiryen kai amarya, bayan kowa ya shirya, su Abba sukace suna bukatar ganin matan zasuyi magana dasu, haka suka rankaya gaba daya suka nufi part din daddy, bayan sunje kowa yanemi guri yazauna, Abba ne yayi gyaran murya kana yace, "ba komai ne yasa muka tara ku ba illa kan maganar auren Ahmad damuka riga muka yanke shawara iya mu, kawai dai zamu fada muku ne a matsayinku na iyayensu mata, Ahmad yazo mana dazancen yanason yarinyar gurin Habiba matar Alhaji Aminu wato dake zaune agida na Zuhura kenan" mom ce ta waro ido tanasan jin karashen zancen "mun fahimci yarannan suna san junansu hakan yasa muka yanke shawarar hadasu aure kamar yadda Ahmad ya bukata" Daddy yafada, "ke kuma kiyi hakuri naba da yarinyarki batare dana ji ta bakinki ba, amma idan bakiso bazamuyi maki dole ba tunda yarinyar kice" Abba ya karashe maganar yana kallon Innna, baki ta bude tace "aini duk abunda kuka yanke akan ya'ya na to bani data cewa saboda bamu da tamkarku, Allah yabasu zaman lafiya" ammeen kowa ya amsa banda mom data cika tayi fam, "amma ni Ahmad be taba sanar dani yanason Zuhura ba" Mamy tayi maganar, Hajiya ce tace "to yanzu yaushe kuka sa bikin"? "Hajiya munyanke idan ta kammala secondary za ai" "to hakan yayi" tunda aka fara mom ce kawai batace kala ba, har aka tashi, Allah Allah take taga Ahmad dan fada na cinta, sedai har aka futo kai amarya bata ganshi ba, futowa akai Ilham tasha alkyabba se kamshi take, aka sata a mota, kodan kukan amarenan ma ita batayi, su Zuhura ma duk suka shiga mota ita da Yasmeen, bawanda yaje raka amarya, saboda ga su Mamy ga Hajiya ga aunty Aisha ga Innar Zuhura, shi Ammar su Abba ya diba da Alhaji Aminu yajasu suka tafi, Ahmad kam sun rigada sunyi sallama da Zuhura, a haka dai suka dau hanyar Kaduna,
basu wani dau lokaci ba suka isa, Mamy ce tace kar a kai Ilham yanzu abari se dare zatayi yar walima kawayenta da ke nan zasuzo, haka a ka fara shirye-shiryen walima, shikam Ammar part dinsa yawuce ya kulle bema san me sukeyi ba, Zuhura Yasmeen da Amira taja suka nufi dakinta, nan sukai wanka suka huta, kana suka kara shiryawa, suka futo gurin walima, malamai Mamy ta gayyato mata sukazo sukai, nasiha, ba laifi ancika sosai, ilham kam wani kayan takara sawa, ba a tashi ba se karfe 6:30pm lokacin za a kira sallar magaruba, futowa yayi dan ya tafi masallaci yaga mutane, be tsaya tambaya ba ya sa kai yafuce, bayan yadawo sallah, still yakoma part dinsa, wanka yashiga, inda yayi wanka yafuto yazauna ya shirya tsaf cikin shadda ruwan omo yayi matukar kyau sosai se tashin kamshi yake, jin cikinsa yayi fayau ba komai, hakan yasa yadau waya ya danna kiran Mamy, tana dagawa tace "son ya akai" "Mamy yunwa nakeji" "ok bara nace Jummai ta hada ma" "Mamy ta hada tabawa Zuhura ta kawo mun" "ok naji zata kawo ma" daga haka Mamy ta kashe wayar, falour tashiga tasamesu gabadayan su a zaune tace "Zuhura jeki gurin Jummai kice tahadama Ammar abinci ki mikamai" amsawa tayi tana mikewa, Mamy taci gaba da sallamar bakin ta, se bayan kowa yatafi tashiga bedroom dinta tayi alawala tayi sallah, sukam su Inna da aunty Aisha tuni sunyi sallar su , bayan tayi tafuto falour tasamesu, "ace Ilham tafara shiryawa time yayi" aunty Aisha ce ta mike tanufi bedroom din Ilham, ita kuma Inna tana zaune , bayan Jummai tahada mata abincin takarba tanufi part dinsa danta kaimai, kofar abude take hakan yasa ta tura tashiga, tana shiga taganshi zaune kan kujera yana kallo, yamata kyau sosai, zuciyarta ce tace mata 'kin manta ango ne fa' wata zuciyar kuma tace 'dama can kullum shi cikin kyau yake' jin shirun yayi yawa yasashi kallon bakin kofar, tana tsaye tana kallonshi katseta yayi da cewa "kona zo na karba ne" dasauri ta dawo daga duniyar tunanin ta wuce ciki, ajiyewa tayi saman centre table, kana tadau plate tafara zuba mai, bayan ta zuba takoma gefe ta tsaya, zauna yafada yana kallonta, zama tayi, shi kuma yafara cin abincin, yanaci yana kallonsa ta kagu yagama ta kwashe kayan tafuce "dagaske kina son Ahmad" tambayar ta doki dodon kunnenta, saurin kallonsa tayi taga bama ita yake kallo ba television din dake falourn yake kallo, shiru tayi ta sunkuyar da kanta, tana wasa da yatsun hannunta, kallonta yayi yace "bake nake tambaya ba" ji take kamar ta kurma ihu saboda kunya, to ita me zata ce, ganin tayi shiru yasashi cewa "ok kina son shi kenan, kuma zaki aure shi, yayi kyau" ita dai bata dago kai ba, amma kana ganin ta kasan amasar eh ce, cokalin ya dire kan plate din, har yana bada sauti, kana yakoma ya jingina da kujera ya rufe idanunsa, baki yabude yace "dauki abincin kije" bata kawo komai ba tamike da sauri tadebe tafuce, ya jima idansa a rufe zuciyarsa na tafarfasar kishi,
kai amarya aka fara tafiya, hakan yasa Zuhura shigewa daki dan batason zuwa, sukam su Inna daga can gida zasu wuce, haka aka ranka ya aka tafi, gidan ta yayi kyau ba karya, falourn ya hadu, saman bene aka wuce da ita, aka kaita dakinta, su aunty Aisha ne sukai mata nasiha sosai kana suka rankaya suka wuce gida, aka barta ita da kawayenta su uku, su Inna gida suka wuce, dansun gaji likis, ita kuma aunty Aisha tabi su Muhsin suka koma gida, dawuri tayi shirin bacci ta kwanta danta gaji, aikam tuni bacci ya dauke ta, Ammar kam har 11:00pm be tafi ba, seda Mamy da aunty Aisha suka bishi part dinsa, suka sameshi, haryanzu yana yadda yake, sallamar suce tasashi bude ido, yana kallonsu, zama sukayi, kana Mamy tafara magana "son yakamata katashi kaje ankai amarya tun dazu" shiru yayi bece komai ba, kafadarsa Mamy ta dafa tana fadin "Please ka daure ka sauke nauyin da Allah ya dora ma, Ilham yar uwar kace, ko yaya kayi wani abu akanta bazanji dadi ba, ko kanaso ka ganni cikin bacin rai" kada mata kai yayi alamar aha ah "to please ka taimaka mun katashi katafi gidan ka" "kwarai kuwa Ammar yanzu ba kai kadai bane koya zaka iya yin abunda zaka tauye mata hakkin ta kuma kashiga fushin ubangiji" jikinsa ne yayi sanya, hakan yasa yakama hannun Mamy yace "no Mamy base kun rokeniba zanyi abunda kuka ce" "yawwa muje nabaka kayan da aka siyo ka tafi dashi" aunty Aisha tayi maganar, daga haka yamike, kazar dasuka sa asiyo da sauran abubuwa suka mika mai, kana ya musu se da safe yawuce, motarsa ya hau yanufi gidansa, yana zuwa yayi horn me gadi ya wangale mai gate ya shiga, bayan yashiga ya tarar ba kowa a falour hakan yasa ya haye sama, hayaniyarsu yaji, kofar ya isa yatura, suna zazzaune kan bed din, karasawa yayi, kowacce acikin su ta zuba mai idanu, zama yayi yana kallon Ilham yace "me suke har yanzu" "am dama siyan baki suka tsaya" "me baki da hankali ko" tsuru tsuru tayi da ido, ya kallesu yace "ku tashi ku tafi" da sauri kowaccen su taja jakarta suka fuce, bayan sun futa, Feenat takalle su tace "gaskiya yanzu na dena ganin laifin Ilham akan son guy dinan, kut gaskiya ya hadu" "ashe bani kadai nake kallonsa ba, ai dar ne gurin kyau" "nifa wlh nasamu wannan ko da duka sena zauna dan babu abunda babu atare dashi" harsuka shiga mota suna gulmarsa,
ledar ya ajiye mata saman bed yace "gashinan ki dauka kici nasan kinajin yunwa nina wuce dakina se da safe" kafun tayi wata magana har ya bude kofa yafuce" ledar ta kalla kana ta bankade mayafin kanta, tana fadin "wai me wannan mutumin ke nufi ne" yana shiga dakinsa yafada toilet yayi wanka yadau kayan bacci yasa kana ya kwanta da tunaninta a karkashin ransa,
yau bata iya tashi da wuri ba saboda gajiyar da tayi, se karfe 9:00am ta tashi, tayi wanka tashirya ta futo, kitchen tanufa, Mamy ce da aunty Aisha se Jummai dake wanke wanke, Mamy ta tsugunna ta gaisar kana ta gaida aunty Aisha kana ta gaida Jummai, "Mamy ba abunda zan taya ku" "ah ah Zuhura mun kammala ai" daga haka tafuce, aunty Aisha ce takalli Mamy tace "aunty Khadija yarinyar na birge ni akwai hankali" "ah ai Zuhura akawai hankali" bayan sun kammala breakfast, Mamy ta hada a basket tabawa driver yakai gidan Ilham, sukuma suka shirshiriya kan dinning, duk suka hallara suna breakfasta din,
me gadi Bala driver yamikawa ya shigar dashi ciki, dama Mamy ta sanarwa da Ilham za akawo musu, hakan yasa tafuto ta karba, zama tayi a falaour, tazuba taci, kana ta kunna tv tana kallo, se karfe 11:00am yatashi, yana tashi yayi wanka yashirya, yafeshe jikinsa da turare, key dinsa yadauka da wayar sa ya fuce, beyi tunanin shiga bedroom dinta ba, ya sakko da niyayar yafuta, samunta yayi kwance kan kujera, ga kulolin abincin duk a bude, ga jarkokin lemo akasa ta zubar da ledojin chocolate din data shashsha, tsayawa yayi yana kallonta, bama tasan yana kanta ba, hakan yasa takara jefar da ledan data gama cin chocolate din, baki ya bude yace "meye haka kika mayar da falour kamar bola" saurin mikewa tayi tana fa
in oh katashi ashe, "tambayar ki nake" "idan natashi zan kwashe ai" "kije ki gyara mun bedroom dina" wani kallo tamai kana ta kawar da kai, shi kuma yasa kai ze fuce, da sauri tace "bakai breakfast ba fa" juyowa yayi ya kalli kulolin abincin dukansu a bude kana yakalle ta yace "ahaka zanyi breakfasts din" kana ya fuce, waige waige take dan ita bataga abunda tayi ba, komawa tayi ta kwanta, tana cigaba da shan alawoyinta
bayan yafuta gida yanufa, yana zuwa ya tarar da Abba ze futa, gaisawa sukai, kana yashiga cikin gidan, duk suna falour banda Zuhura da tanacan tana bitar karatun islamiyya dan sunfara screening din sauka, asabar ta gaba za a gudanar da saukarsu, zama yayi kana ya gaishe su gaba daya, suka amsa, aunty Aisha ce takalle shi tace "ah ah naganka da sassafe" "aunty zanje office ne" "bazaka bari ka gama cin amarcin ba" "aunty aimu aikinmu ba a mai haka na ceton rai ne" "gaskiya kam naceton rai ne" Hajiya tayi maganar tana kallonshi "Mamy inason coffee" "ok Muhsin ina Zuhura ta hada mai" anzo gabar da yake so dama ita yakeson gani, "Mamy tanacan tana bita na screening din saukar mu" "oh hakane fa to fadawa Jummai ta hada mai" amsawa Muhsin yayi yana mikewa, kallon Mamy Ammar yayi yace "saukar me kuma" "next week saukar sufa" girgiza kai kawai yayi, Jummai ce tazo dauke da cup din coffee din, tdugunnawa tayi ta gaishe shi ya amsa kana ta mikamai, karba yayi ya fara sha,
seda ta tabbatar karatunta ya zauna ba gargada, futowa tayi, daga dakin nata, falour ta nufa, lokacin shikuma ya mike ze tafi, karasowa falourn tayi, tana zama kusa da Mamy, kallonshi tayi tace "ina kwana" batare daya kalle taba yace "lafiya lau" daga haka yace "Mamy zan wuce" Muhsin ne yazo yana fadin "yaya Zuhura ana nemanki a waya" yafada yana mikamata wayar, karba tayi takara a kunnenta, kawarta ce ta islamiyya takira tace Muhsin y hadata da Zuhura, mikewa tayi ta bar gurin, da kallo Ammar yabita, zuciyarsa ce tace 'watakila fa yarinyar nan Ahmad ne yakirata' "me kake kallo kuma kace kuma katafi" Hajiya tafada tana kallon sa, se lokacin yadawo hayyacinsa, daga haka yasa kai yafuce, bayan ta gama wayar tazo takawowa Muhsin wayarsa,
"ai naga yaron ba laifi yanada hankali shima" "to nidai kawai sedai nace Allah yabasu zaman lafiya tunda tanasansa" "ammeen dai" "yawwa nace inasan naje gurin yaya ta, rabona da ita tunda muka rabu" "hakan yayi kyau yaushe kenan zakije" "da sonake bayan saukar Zuhura, muje tare tunda yanzu makaranta, kaga sena sanar da ita ansa ranar auren Zuhura" "gaskiya kam idan zakuje sai direba ya kaiku" "to shikenan" "bara natashi na wuce karna makara" daga haka ya mike ita kuma tabishi abaya dan ta rakashi, su Yasmeen ne a falourn suna zaune suna kallo, adawo lafiya sukai mai gaba-daya, yafuce, har bakin mota Inna ta rakashi, kana ta dawo