Sashe 3
Soyayya Da Izza Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Soyayya da izza Story and writing by Hadeexatu(mrs KD) yar amanar jajitattu Typing Page 3 Zuhura kizo ki zuba ruwan wankan lokaci karya kuremikifa ta cikin dakin tace to inna ina zuwa futowa tayi tanacewa inna ina kwana lpy lau dauko bokiti na zuba miki ruwa to tace tanufi bandaki daukowa tayi inna ta zuba mata ruwa tanufi bandaki dan tai wanka bata jimaba ta futa daki tashiga tashirya tsaf cikin uniform dinta farin hijabi da dark green wando da riga futowa tayi tanacewa inna zan wuce bazaki tsaya kisha kokonba ah ah inna nakoshi karna makara to ai kece da nauyin bacci kamar kasa se ai ta tashinki kiki tashi nifa inna banajin lokacin da kike tashinafa ina zakiji kinata sharar bacci, kofa tanufa tana fadin inna sena dawo Allah ya kiyaye adawo lpy amen ta amsa dashi yayinda take fucewa waje, ita kadai take tafiya kasancewar maryam ba makarantarsu dayaba maryam tanazuwa ta masu hali tafe take tana tafiya harta isa bakin gate din makarantar shiga tayi kai tsaye ajinsu tanufa yayinda suke ta shara seda suka kammala sharar malami yashigo wanda suke kira da sir mansir wanda yake daukansu physics mikewa sukai suka gaisheshi yayinda ya umarcesu dasu zauna tambaya yayi akan last topic din dasuka gama bawanda yabasa amsa ganin haka zuhura ta daga hannu pointing dinta yayi yana cewa munajinki bayani tashiga yimai dala dala bashi kadai ba harta yan ajin ta burgesu tunkafin takarasa aka faramata tafi dakatar dasu yayi inda yakalleta yace what's is you name zuhura haruna adamu dakyau zuhura idan anfuta break kisameni staff room to tace yace tazauna yafara lesson dinshi Inna ce takaiwa baba karin kumallo koko ne se dan tuwon data tuka ta kadamai miyar kuka kawomai tayi ci yafarayi bayan yakammala ya futa ya wanke hannunshi yadawo bara natafi kar oganmu yazo banjeba kinsanshi da bala i to seka dawo adawo lpy ameen ya amsa yanafuta bayan yafuta ne tashiga gyare gyaren gidan Iya lami me aikin mamy ce taketa shirya breakfast a dining mamy ce tafuto sanye da doguwar riga tasha duwatsu se kyalli take karasowa dining din tayi inda iya lami ta gaisheta mamy ce tace su muhsin suntafi school eh hajiya suntafi ok jawad fa be futoba ok to ki tasoshi tom hajiya wucewa tayi dakin jawad kwankwasawa tayi waye yafada a hasale iya lami ce to meyafaru hajiya ce take kiranka ok yafada time din yafuto daga wanka sauri sauri yayi ya shirya dan yasan mamy na jiranshi suyi breakfast iya lami ce ta dawo tanafadin hajiya gashinan ok to mamy tafada iya lami wucewa tayi kitchen jawad ne yafuto yana danna wayarsa kujera yaja yazauna yana fadin good morning mamy amsawa tayi tare da cewa school fa se 1:00pm zantafi ok kayi breakfast Bayan an futo break ne tace wa da kawarta sumayya tazo ta rakata staff room sumayya ce tace nidai bazanjeba kije kidawo bara naje na siyo awara to tace mata tanufi hanyar staff room bayan ta shigane ta hango shi a kujerarshi dayake zama gurin tanufa durkusawa tayi tace sir gani yawwa zuhura kinzo kaita gyadamai ok janyo durowar dake jikin table dinshi yayi yadauko littafai dozin daya da biro da pensil da maset ya ajiye asaman table dinshi hannunsa yasa a aljihunsa yaciro yan dari biyar biyar guda hudu dauko littafan da maset din da biron da pensil da kudin yamika mata dagowa tayi tana kallonshi shima kallonta yakeyi ganin yana kallonta yasa tayi kasa da kanta ki karba mana kai ta gyadamai alamar bazata karba ba kikarba nace ah ah sir kabarshi ke namiki kyauta kice nabarshi kokarinki ne yasa nabaki da buki bani amsaba bazan bakiba dan haka ki karba karba tayi tana yimai godiya zuhura yafada yana kallonta kamar zeyi magana se kuma yayi shiru ok tashi kije kici gaba da kokari kinji tom tafada tana dadaimai godiya tafuta tanafutane kai tsaye gurin da suke zama ita da kawarta sumayya in an futo break tanufa tarar da ita tayi a zaune zama tayi itama kusa da ita tana mikamata kayan daya bata sumayya ce ta karba tana kallon zuhura shiya baki wanan kayan eh shiyabani da ni nama ki karba seda yamatsamun sannan nakarba jinjina kai sumayya tayi tace anya kuwa zuhura ba sonki yakeba haba dai so kuma ai yace saboda nabashi amsa shiyasa yabani to ai shikenan aji suka koma sanadiyyar an kada kararrawa ta komawa break se 1:15pm aka tashesu kai tsaye gida tanufa tana shiga tafara kwalawa inna kira inna inna nadawo daga cikin dakin inna tace to sannu da dawowa inna mekikeyine tafada tana shiga dakin gari nake lalube kinganninan nagama miya banga gariba to inna kuma yunwa nakeji sarkin ci saboda ke naketa hanzari nagama inna kumafa ban karyaba to sarkin mita jeki cire unigorm din harta tafi ta dawo tana fadin inna anbani kyauta a makaranta to me aka baki hannunta ta zura cikin Jakarta ta fito da kayan da sir mansir yabata tana nunawa inna karba inna tayi tana fadin wane yabaki wannan kaya haka kuma me kikaimai inna tambaya yayi nabasa amsa shine yabani to ungo boye in babanki yadawo kinunamasa to tace tafuce tana fadin inna ina amira da auta sun fice wasa bama su dade da fucewaba Wacece zuhura Malam adamu abdulahi mahaifin malam haruna wato kakan zuhura yanada mata biyu matarshi tafarko habiba tanada yaya biyar sama'ila se hafasatu se hauwau se idiris se mika'il se matarshi ta biyu suwaiba kakar zuhura danta daya malam haruna mahaifin zuhura yana shekara 5 mahaifinshi ya rasu dan haka ya girma a dangin mahaifiyarshi sanadiyar shine yasa taki aure saboda batasan rabuwa dashi mahaifin malam haruna yabarmusu gonaki har kusan biyar amma sanadiyar Shiba a gidan yakeba yasa kanin mahaifinshi yadage seya karbi kudin ze juyamai ahaka aka bashi tunda aka bashi ko labarin kudin yadenayi sukuma kamar anrufe musu baki seda yakai shekara 11 mahaifiyarshi ta rasu nan aka rinka rigima waye ze rikeshi gashi kakaninsa sun rasu ahaka yayan mahaifiyarshi yadaukeshi ya rikeshi yake tayashi aikin gona da haka har yakai shekara 25 malam haruna yarone me kwazo bashida kiwa sanadiyar haka yayan mahaifiyarshi yadauki son duniya yadorawa yaron da haka har matarshi take jin haushi ta tsaneshi yasha wuya a hannunta, nan ne yayan mahaifiyarshi yace yasamomai matar aure yar gidan abokinshi malam garba wato innar zuhura babanta malamine yana koyar da almajirai nan yaje yaganota yaji ta kwantamai arai macace me kamala da mutunci kuma kyakyawa mahaifiyarta bafulatanace dan haka kana ganin habiba kasan jinsin fulanice anan aka daura musu aure seda tayi shekara kusan 5 bata haihuba har abun yafara basu tsoro inda wan mahaiyarshi yaketa ziryar karbo musu magani saboda acewarsa kan ya mutu yanaso yaga dan haruna, tunda matarshi taga yadda ya kwallafawa dan gidan haruna kota nata jikokin bayayi nan tashiga yawon bokaye nan wata kawarta ta rakata gurin wani boka aka tushewa habiba mahaifa habiba tashiga damuwa ko bacci batayi kullum kuka anan ne mahaifinta yasa aka rubutamata alkur'ani tasha cikin kuddurar ubangiji ko wata ba ai ba tasamu ciki murna ba a magana gurin yayan mahaiyafiyarshi bakin ciki kamar ya kashe matar wan mahaifiyarshi nan cikinta yakai wata 8 a watanne yayan mahaifiyar haruna marikinsa ya rasu yaji mutuwarnan baka danba yaso yaga ya haifarmai jika , habiba bata shiga wata na taraba tafara nakuda inda haruna ya gigice yatafi yakira matar wan mahifiyarshi yadauketa kamar uwa tunda agurinta ya karasa girma yayin da tazo habiba ta jigata sosai dakyar ta haihu ta haifi mace matar wan mahaifiyarshi gwago larai taso takashe abunda ta haifa dangin habiba suka zo anan yarinya taci suna fatima suke kiranta da zuhura yarinyace kyakyawa ga gashi ga hanci ba fara bace tanada farin jini kowa yaganta seya dauketa seda takai shekara 4 anan ne gwago larai da yayanta sukace alallai se malam haruna yabar gidan tunda wanda yakawosa ya rasu haka suka tattara kayansu suka bar gidan gashi basuda gurin zuwa hakan yasa habiba ta tafi gidansu kafun ya nemomusu muhalli nan yaje gurin abokinshi da suka tashi tare tunda shi yanada hali, yaji tausayinsa sosai hakan yasa yabashi gida yazauna ya sanar da yayanshi cewa yabawa abokinshi gida kar wanda yayi yunkurin karbar gidannan sedai bayan ranshi anan suka koma gidan suka cigaba da zama inda malam haruna yake fafutukar neman aiki dakyar yasamu awani gareji aka daukeshi aikin gadi shize dinga budewa kuma yana rufewa, zuhura takai shekara10 habiba tasamu cikin amira, a lokacinne mahaifiyyar habiba tarasu, amira takai shekara 5 ta haifi halifa, mahaifin habiba ya rasu bata da kowa daga ita se yayarta suka rage, halifa ayanxu yanada shekara 5 amira na shekara 10 zuhura kuma nada shekara 17, zuhura kyawunta yafuto sosai tanada dogon hanci fatarta chocolate colour ce tanada manyan idanu da dan karamin baki zuhura nada gashi dan idan tasakeshi yana kaiwa gadon bayanta bata da kiba kuma ba doguwabace can sedai tanada diri sosai inda inna ke mamakin yarinya karama tayi diri irin wanan maza dayawa sunsha biyota har gida amma bata sauraronsu saboda babanta yace yarinyace ita Mu koma ainahin labarin Yau suke graduation dinsu na kammala makaranta dan haka dawuri yafuta makaranta yana zuwa kayanshi yasa se alokacin yatuna da Ahmad wayarshi yadauka yana kiranshi dagawa yayi sorry abokina na makara ina hanya tokai sauri ka karaso ok wayar yakashe Ahmad be jimaba ya karaso anan ne akafara gudanar da bikin graduation din, seda aka kammala binkin, Ammar yagaji sosai garden din school din ya tafi dan ya huta wata budurwce take takowa gurinsa tanazuwa ruwan roba ta mikamai karba yayi batare daya dago yaga wayeba idanshi nakan wayarshi bude ruwan yayi yana kafawa abakinshi dama kishi yakeji seda yagama sha yace kazauna mana kodai dan sanda zakaine budurwarce tazauna tana facing dinshi kallonta yayi yace yadai bakomai sunana humaira ni yar nigeria ce inba damuwa zamu iya zama abokai, ah ah yafada yana mikewa baki tasaki tana kallonshi inda tace ko tayaya Ammar sena sameka, Ahmad yashiga nema dan su wuce gida ya dubashi ko ina be ganshiba dan haka kawai yanufu parking space hango motar ahmad din yayi da alama akunne take karasawa yayi daf da motar bakin tintek ne a glass din dan haka ya kwankwasa glass