← Book details Soyayya Da Izza Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 21 OF 97

Sashe 21

Soyayya Da Izza Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

SOYAYYA DA IZZA
Story and writing by Hadizatu
Mrs (KD)
Yar amanar jajirtattu
https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
*JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan
asaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sau
page 20
________________Memakon tagansu agida seta ga yatsaya bakin wani tankamemen gate, ita dai batayi maganaba ta zubawa sarautar Allah ido, wayarsa yadauka ya danna call, ana dauka yace, "gani nazo kifuto" daga dayan
angaren aka ce, "bazaka shigo ba"? " no patreshia kinsan banasan zuwa hotel kawai kifuto" ok ganinan" wayar ya katse ya ajiye ta, gaba
aya ya rasa me zeyiwa yarinyar nan ta dena bibiyarsa, kodai yafadamata yakusa aure ne, zuciyarsa ce tace, 'kawai kafada mata watakillaha takyaleka' kwankwasa glass din da akayi ne yadawo cikin hayyacinshi, glass din yazuge yace mata ta zagayo tashigo, kallon Zuhura yayi yace" koma seat din baya" tasan da ita yake duk da be kalleta ba, hakan yasata futa takoma baya tazauna, patreshia kallonta kawai takeyi tana tunanin wace wannan yarinyar, mota tashiga tazauna a gidan gaba, kallonshi tayi tace, "Ammar yaushe ne kafara neman mata" saurin kallonta yayi yace" bangane ba " wannan yarinyar nake nufi" "ke kinma raina ni idan ma neman matan zanyi se in nemi wannan yar ta tsitsiyar yarinyar mezan tsinta ajikinta" bama wannan ba yaushe zaki koma USA" bayanzuba se lokacin dakace kana sona zankoma" kinga nafada miki gaskiya nan da two week zanyi aure"aure kuma"! " aure " wacece wadda zaka aura" juyawa yayi ya kalli Zuhura da hankalinta ma baya kansu ta nacan tanata kallon jama'ar dake kai kawo cikin harabar hotel din, patreshia yakalla yayi murmushi yace, "gatan nan abayanmu itace wacce zan aura
in" haba Ammar wannan karamar yarinyar zaka aura me zata ma"daga mata hannu yayi yace kinga ya isa "Mamy nace tazaba mun ita kuma kinga bana tsallake maganar Mamy" saboda haka nanda two weeks zanyi aure Kinga dole ki koma USA yanzu" cikin kuka tafara magana tana cewa" Ammar bakamun adalciba ko kadan, kasan yadda nake sonka, ba wulakancin da bakamunba danna rabu dakai amma nadage , "shikenan Ammar nagode", kinga patreshia nagaya maki Mamy ce tazabamun ita, daga mai hannu tayi tana bude murfin motar tafuce, kallonta yake harta kule mai, ajiyar zuciya yayi kana yajuya yakalli Zuhura daketa kalle-kalle hankalinta kwance bama tasan me sukeyiba, "ke dawo inda kike mutafi" bataji shiba hakan yasa bata amsaba ,hankalinta yanacan kan masu wucewa tanata kallonsu tana mamakin shigar jikinsu, wata tsawa yadaka mata wacce tasata dawowa cikin hayyacinta, "ke nizan dinga maki magana kujiyamun kai" "wlh banjikaba" to seki dawo gun dakike kizauna mutafi, tom tace, ta bude tafuto takoma gidan gaba, motar ya tayar suka tafi.
"Ilham kaffa kisha dayawa ki bugu ki kasa zuwa gida dan sedai ki kwana anan" daga wannan kwalba biyun shikenan bazan karaba" idan ma kin kara ke zakije gida a buge kuma kinsan idan Ammar yaganki a buge maganar auranku ta ruguje" ke wannan wanne irin bakin bakine babu abunda nafiso aduniyar nan sama da yaya Ammar, lallai nina rasa me wannan Ammar din yake miki da su bash boy basamiki" ke yaya Ammar nadabanne ai" wannan kuma ke kika sani" wata budurwa ce ta fito daga toilet alamar wanka tayi, "wai Ilham kinanan kinata shaye-shaye nan naki ko" wlh Feenat maganar danake mata ne kenan" kinsanta ita bata iya shan kadanba" tacigaba setaje gida a buge Ammar din nata yaganta yace yafasa dama kiris yake jira" Ilham ce tadire kwalban hannunta tace"ku baradai na ajiye kar inje bakinku yakamani kuda bakwawa mutum maganar kirki"ai maganar kirki se dan kirki" feenat tafada tana cire rigar wankan dake jikinta, wai naga kinasa kaya inazakije"? wlh tj ne yakirani yanasan ganina" se kije ai kwakularki zeyi ba wani abuba" Iham ce tagyara zama tana bude ido dakyar tace, ni narasa mekikeji ajikin maza wanda mu bamu dashi" rabu da ita dai nifa wlh namiji baya gabana banga abunda zemunba wanda yar uwata mace bazatamunba" to dan Allah karku cijeni a inda bazan warkeba mana" nifa saboda inasanshi ne yasa nake bashi abunda yabukata" to seki tabashi ai" naga kema yanzu da Ammar zece kibashi da gudu zaki bashi" Ammar kika ce aishi na dabanne" Ilham ce tafada tana mikewa takalli Rufee tace, "nizan wuce gida dare nayi" oh yanzu kenan nikadai zanzauna adakinnan" to ni dai gaskiya tafiya zanyi saboda dare yafarayi" tom shikenan " to kema kitafi club mana me bi ma kisamo wata ki rage zafi da ita" wlh Ilham yau bansan zuwa club amma bara nakira Mufeeda tazo" Feenat ce takalleta tace " kinsan halin Mufeeda sekin biyata zatazo" ai dama zan cake mata kudinta cas " to shikenan nidai natafi" tom ki gaida gida ki gaishe da su Ammar din" tom zangaisheshi kinji".

SOYAYYA DA IZZA
Story and writing by Hadizatu
Mrs (KD)
Yar amanar jajirtattu
https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
*JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan
asaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sau
page 21
_________________Gate din gidan megadi ya bude mai, yashiga ciki, parking space yanufa yayi parking din motar,
alle murfin motar yayi yafuta, itama futa tayi, sotake ta tambayeshi kayan amma saboda tsoro takasa, zagayawa yayi yabude boot din motar yafuto da kayan ya ajiye"ga kayanki nan kizo kidauka" tom, tace ta tsugunna takwashi ledoji guda biyu, dakyar ta iya dagawa saboda kayan sunmata nauyi, ganin dakyar take tafiya yasashi kiran Bala driver dan ya karbar mata, ciki yashige yabarsu a wajen, Bala driver ne yace "kawo nashigar dasu ciki" mikamai tayi tana fadin nagode, wucewa gaba yayi ita kuma tabishi abaya, Muhsin ne da Ahmad azaune afalon, shigowa yayi , Ahmad ne yakalleshi yace "ah abokina daga ina"? duk inda zani sena fadama ne kai ina kaje tun safe" Ahmad ne yakalleshi yace kaima kasan ai inda naje" no bansaniba ba ruwana" dariya ahmad yayi, "ina Mamy "? tana kitchen "ok , yana fadin haka yayi hanyar part dinshi. bala driver be yashigo , Zuhura tafe abayansa, q falour ya ajiye mata kayan yafuta, falour n tashiga gnanin Ahmad azaune afalon yasata tsugunnwa ta gaishesa, amsawa yayi cikin fara'a, Muhsin ne yakalleta yace su aunty Zuhura ina akajene" unguwa naje tafada tana dariya" Ahmad ya shagalta da kallon dariyar tata ba karamin kyau tamata ba" ina Mamy" yar gidan Mamy " Muhsin yafada yana dariya" kodai kana kishi ne" eh gaskiya inayi" tom shikenan nasan inda zan ajiyeka" daya daga cikin ledojin tadauka dakyar tanufi hanyar dakinsu, Ahmad ne yakalli Muhsin yace" kashigar mata da sauran" to yaya Ahmad" yafada yana mikewa, kayan yadiba yabi bayanta, dakinsu tashiga ta ajiye kayan" lah Muhsin ashe ka biyoni da sauran" eh " amsa tayi tana fadin" to nagode" bayan ta shigar dasu tafuto tanufi kitchen, Mamy ce da inna suke aikin girki sunata hira suna raha, tana shiga tanufi gurin Mamy tana rungumeta tace "Mamy mundawo" to sannunku da zuwa" Mamy kizo muje kiga kayana" tom kibari mu karasa girki se muje mugani ko" tom tafada tana nufar inda Inna take tana fadin" Inna yaukuma me ake dafamana" to sarkin ci hala yanzu zakicemun kinajin yunwa ko" aikam Inna kamar kinsani" ai nasan karshen zancen kenan" Mamy ce tayi dariya kana tace" am Innar zuhura namanta ban fadamiki ba gobefa munada bakuwa, duk da ba bakuwa bace mahaifiyar me gidan ce" gobe insha Allah zata dawo daga Saudiyya, Innar Zuhura kezaki mata girki tafuson abincin gargajiya, "tom hajiya insha Allah, ammeen Mamy tafada, futa zuhura tayi, dakinsu tanufa tashiga toilet ta watsa ruwa daya daga cikin kayan baccin dasuka suyo tadauka tasa, doguwar riga ce mara nauyi se hularta, futowa tayi ta iske Mamy tana shirya dinner kan dining, gurin tanufa tana fadin, "Mamy dakanki meyasa bikinkiraniba kawo nayi, "to ai naga yanzu kika dawo ne kuma kin gaji" ah ah Mamy bangajiba yanzu ke kije ki hutu a dakinki ko ko kuma kibari kiyi dinner" kai kinaji dani dayawa" dariya tayi tace "ai dole ya ta kula da mahaifiyyrta" hakane kam " kije ki kirasu suzo suyi dinner" tom Mamy" daga haka tabar gurin,
Gate yabude mata tashigo ganin zata bi takansa yasashi kaucewa, kallonta yake yana mamkin meke damun yarinyar nan, "anya kuwa hajiya kalau" yafada cike da mamaki, parking dinma ba dai-dai tayiba, shidai Yunusa me gadi komawa yayi yazauna yaci gaba dajin rediyonsa, duk suna zaune afalourn amma banda Ammar dake part dinsa, Jawad ma yadawo saboda gargadin Ammar dabe mantaba, shigowa falourn tayi bata kalli kowaba tayi hanyar dakinta tana hada hanya, Jawad ne yabita da kallo, seda ta kule mai, yajuya yakalli Ahmad dabemasan meke faruwaba, "yaya Ahmad anya kuwa aunty Ilham kalau take" meka gani"? "ganinai kamar ma bata ganmuba" kyaleta can ina ruwanmu da ita" yafada yana maida kanshi kan wayarsa, Zuhura ce tashigo falaourn , Ahmad ta gaisar kana tace , "Mamy ce tace nazo nafadamaku angama abinci" amsawa sukai da to, part din Ilham tanufa knocking tayi, akace, "waye" aunty Ilham nice" to meye" Mamy ce tace nazo na fadamiki angama abincin dare" ok jeki zanzo, daga haka Zuhura tawuce ta tafi, part din Ammar tanufa , daga bakin kofar ta tsaya tayi knowking , ba alamar ma da mutum ko motsi batajiba, tura kofar tayi tashiga a hankali, falourn tsaf_tsaf hakan yasata cewa ko kara futa yayi, juyawa tayi danta tafuta, muryarsa taji kamar daga sama, yana fadin, ke meya shigo dake part dina, cikinta ne yaduri ruwa, ga fitsari kamar ya zubo, kwata-kwata tama kasa juyowa, takunsa taji abayanta, seda yazo daf da ita yace, "ba magaan nakemikiba kibani amsa" juyowa taya bata yadda sun hada ido bata ce, "Mamy ce tace nazi nafadama angama abincin dare" bakinta kawai yake kalla ,yadda take maganar cikin natsuwa, "ok kice ina zuwa" kafun ma yakarasa tayi maza tafuce,
Chapter 21 · 0% Book details