Sashe 53
Mar'adams Part 4 Complete Hausa Novel · about 8 min read
cikin nashi tare da juyawa ta soma taku ahankali dan har lokacin tana jin zafi ajikinta bayanta ya biyo ji tayi yayi sama daita bai sauketa akoina ba sai bedroom dinsa ya ajiyeta akan kujerar sofa ya rusuna a gabanta yana kallonta tayi shiru tare da tsura masa ido tana kallonsa tana tunani tabbas tasan yana sonta itama kuma tana son shi sai dai bata jin zata iya zama cikin ahlinsa dan zama acikinsu ba alkhairi bane agareta." Ahankali ya kamo hannunta ya rike cikin nashi yana murzawa yana kallon cikin kwayar idanunta "mahaifiyata tana matukar sona maryama idan nace miki tafi sona akan duk ya'yanta banyi karya ba domin tun dana taso nake gani so da kulawa atare daita."haka ma yan'uwana suna sona ni d'an gata ne a wajensu, inda aka samu matsalar shine aurena da mmn khaira amamn yanuwana suna sona mahaifiyata kuma uwa ce jajurtacciya akan ya'yanta a tun sanda mahaifinmu yake raye haka bayan babu ran mahaifinmu , itace ta d'auki duk wani dawainiyarmu ta tsaya ta kula da ya'yanta guda biyar kula da ya'ya biyar har da mutun irina kinga ba abu ne mai sauki ba ta sadaukar da rayuwarta akanmu abinda tafi damuwa dashi shine ta bamu kariya ina tsananin sonta."shiru maryama tayi tana kallonsa cike da shukin son shi "duk da nasan a yanzu ta d'auki wata hanya da ba daidai ba domin ba halinta bane, ban kuma santa da wannan halin ba sai dai nasan a dalilinki na rasa duk wata kulawa da soyayyar da gata ta uwa data yan'uwa duk wannan abun dana rasa kice na rabu dake kin min adalci kenan ?"ya fad'a yana sake kamo tafin hannunta cikin nashi " . "Ya sauke numfashi ahankali ya cigaba da mgn "maryama nayi miki alk'awarin zan kasance tare dake duk runtse duk wuya kuma nayi imani sweetheart zata sauko yayinda ta fahimci irin son da mukeyiwa junanmu zata amince dan na tabbata muddin ta fahimci bazaki cutar dani ba zata soki ."kana ganin mahaifiyarka zata soni ?" ya gyad'a mata kai tare da kai yatsun hannunta cikin bakinsa yana tsotsa yana lumshe mata idanunshi wanda hakan ya sake kashe mata sansar jiki ." da kyar ta fixgo magana "gasky bana jin zatayi haka araina"zatayi domin tun farko itace ta zaba min ke amatsayin mata batare data gane ke din mafarkina bace ,nasan akwai inda nayi kuskuren kuma na gano kuskurena wanda ya jaza miki bakin jini a wajenta shiyasa a yanzu bazata karbeki da sauki ba ,amman zata soki tunda kina raina sai dai ba a yanzu ba "naji amman zuwa yaushe ne zata soni ?"zata soki !ni dai idan da Hali ka d'auke zuwa wani guri mu cigaba da rayuwarmu acan "zuwa Ina kenan kike nufi ?" Yayi mata tambayr yana tsura mata tsumammun idanunshi "bansani ba amman zaka iya tafiya dani koina muyi rayuwarmu dan wallahi tsoronsu nake ji ." "bazan iya gudun mahaifiyarta ba dan idan na aikata haka laifina zai fi kuskuren da nayi a baya bazan iya gudunta ba domin a yanzu ma ina jin rashin kyautatawata da na kasancewa dake na barta cikin damuwa "bata san sanda murmushi ya bayyana akan fuskarta ba "gasky kana sonta sosai".haka ne Ina sonta fiyye da komai acikin duniya"kema kuma kina cikin raina !"ya fad'a yana shafa fuskarta sannna ya sake tsarke hannuwansu yayi kissing din bayan hannunta ahankali ya cigaba da kissing din hannunta "idan baki sani ba "kece rayuwata maryama kece macen da nake k'auna, macen da nake son na aura na ajiyeta a gidana muddin rai ".kallonsa kawai take ko kifta idanuta bata son yi ." "tun taso wata ban ta'ba furtawa kowace mace kalmar so ba sai ke "ahankali ya dinga fad'a mata matsayinta acikin zuciyarsa "a yanzu wani irin farinciki take ji da ya sake tabbatar mata da cewar ita din rayuwarsa ce " batai tsamanin soyayyarsa zata zamo abun farinciki arayuwarta ba ,dan bata san farinciki ba sai daya fara nuna mata tai farinciki ko da iyakar rayuwar da take dashi ne,ya sauya mata rayuwarta bayan iyayenta tana jin cewar ta samu wanda zai kula daita har karshen rayuwarta "bata son ta rasashi arayuwarta bata son ta rasashi bata son ta rasa shi ."nan take idanunta ya cika da kwalla."karki min asarar hawayenki "?a duk lokacin dana gansu suna daga min hankali "fad'a min me kike tunani akaina ?" "ba...bana son na ra .."sai tayi shiru ta kasa k'arasa maganarta saboda kukan da ya ci karfinta "karkiyi tunanin zaki rasani muna tare nayi miki alkawari kasancewar dake har karshen numfashi na kema kiyi min alkwarin ."shiru tayi ta kasa cewa komai sai ma sukuyar da kanta da tai kasa tana zubar da hawaye" "maryama !" ya Kira sunanta yana murza tafin hannunta dake cikin nashi "kin min alkawari duk runtse bazaki barni ba "kasa magana tayi domin bazata masa alkawarin ba dan tasan bazata iya cika masa alkawari ba idan yan'uwansa suka sakota gaba fa tayi yaya da alkwari ?"matsowa yayi kusa daita sosai ya d'ago ha'barta yayi kiss din foreign head dinta yana kallonta fuskarsa cike da damuwa domin baya son abinda zai nisanta shi daita ko abinda zai raba tsakaninsu "karki yi tunani komai ta bangarena komai zai tafi normal ". still dai shiru tayi taki cewa uffan idanunshi ya zuba mata yana kallonta kafin ahankali yace "ki daina tunanin su khadija tun farko kece kika basu dama da kin fad'a min da al'amarin bai kai haka ba ,amman kika dinga boye min bayan koda sharadinsu ko babu ke din tawa ce dan bazan bari ki auri wani ki barni ba ki manta dasu muyi rayuwarmu dan bazan iya rabuwa dake ba." ya kai hannunsa yana shafa wuyanta zuwa k'irjinta saurin d'auke numfashi tayi tana dubansa ya rabbi" yaushe ne zata iya rabuwa dashi "?ta Ina ma zata fara rayuwa babu shi da irin wannan sabon da yayi mata ?" a ina zata samu mijin da zai mata irin wannan son mai tafiyar da ruhi ?". tayiwa kanta tamabayar tana lumshe idanunta tana jin yadda soyayyarsa ke kutemimiya da ruhinta da zuciyarta,wallahi bata san son da take masa ya Kai haka ba sai a yanzu." Cigaba da shafa k'irjinta yayi yana had'iyar yawu sake matsota yayi ya kamo lip's dinta yana tsotsa ahankali aiko nan take numfashinta ya dinga fita da sauri sauri ,ta yarda ta sadaukar masa da rayuwarta da komai nata akanshi, zata rayu dashi acikin kowani hali domin kota rabu dashi tasan bazata ta'ba samun kamarsa ba zata d'aure zata zama jajurtacciya a gidan aurenta daman auren gwagwarmaya ne ."sai daya tsotse bakinta sosai sannna ya zare bakinsa "ina jinki ki min alkwarin bazaki barni ba zaki kasance dani muddin rai "naji !" tai maganar tana sauke wani wahalallen numfashi "ba kinji ba kiyi kamar yadda nayi "nayi alkwarin zan karar da rayuwata gabad'aya da kai "thank you so much my princess ".ya fad'a yana sak had'e bakinsu waje d'aya ."a kalla sun d'auke sama da mintuna shabiyar suna makale da juna suna sucking din bakin juna ringin wayarsa ne yasa shi zare bakinsa cikin nata ya tsura mata idanunshi da suka canza numfashi maryama ta sauke sannan tayi kasa da idanunta tana kallon yatsun kafafunsa ,shi kuwa cigaba da kallonta yayi yana jin kamar ana fixgar ransa akanta." Wayarsa ya ciro sunan hajiya zulfa'u ya gani ya d'aga tana jin muryarsa tace "to adamcy ni zan wuce sai wani lokaci kuma ka kara hakuri Kai ne mai halakin kare yan'uwanka da mahaifiyarka kada ka bari soyayyar mace ta rufe maka ido ka wulakanta yan'uwanka da mahaifiyar datai silar zuwanka duniya kuma wacce aljanarka take tafin kafafunta ,kabi komai ahankali ku rabu lafiya in sha allahu komai zai zama normal ka kara hakuri kaji "jikinsa a sanyaye yace "na gode sosai aunty bari na fito nayi miki rakiya "aa kayi zamanta ga yanuwnaka nan zasu rakani salim da hisham ka kula da maryama sannan ka d'aga mata kafa da Allah."hannu ya kai ya shafa sumar kanshi yana kallon face din maryama sannan yace "Aunty ga maryama kuyi sallma tace "to !"ya saka wayar a hands free tare da mata alamar tai magana "ina wuni aunty ?lafiya lau maryama ni zan wuce sai wani lokaci kiyi hakuri da abinda ya faru in sha allahu zai zama matakin daukaka haka zalika kibi mijinki sau da kafa ki kuma bi uwar mijinki ki zauna da kowa lafiya in sha allahu zamu dinga waya kinji "maryama tace "to na gode Allah ya saukeki lafiya tace ameen ."sukai sallama " Bangaren mami kam fushi tayi sosai dasu aunty khadija suna shiga d'akinta bata bari sunyi mata magana ba ta rufesu da fad'a ta inda take shiga bata nan take fita ba ,babu shiri suka tattara suka bar gidan akan hanayarsu ta komawa gida ne aunty khadija ta dubi aunty shahida tace "jikina na bani zabiba ce ta fito da magnar nan har wannan d'an iskan ya san komai "ba lallai ba, bakiji yace duk abinda yake tafiya yana sane ba nafi tunanin yayi connecting din komai da wayarta ne "ki dai yi tunnain da kyau kafin yayi bincike lallai an samu wanda ya fad'a masa ta bangaren zabiba ko kuma ita makirar yarinyar ." bana tunanin zabiba zata mana haka nafi tunnain yarinyar dan nasan zabiba bazata ta'ba aikata haka ba ".shiru aunty khadija tayi tana cizan lip's dinta "yanzu menene abunyi ".?numfashi aunty khadija ta sauke da karfi kana tace "a duk wani abinda zamuyi a yanzu ya rushe dole mu ajiye komai saboda kwanciyar hankali mami, zamu dawo mu bata hakuri sannna mu fad'a mata manufarmu abinda tace dashi zamuyi aiki idan tace muyi muyi idan tace abarshi shikenan yaci lafiya ammna wannna makirar yarinyar sai naci uwarta da kyau bazan ta'ba raga mata ba ko d'aga mata kafa ba da kanta zata tattara ta gudu ta barshi idan taji uwar bari "da wannna tautaunawar direban aunty shahida ya sauke aunty khadija a gidanta suka kara gaba ." ******** "Da misalin karfe goma na daren ranar adamcy na zaune yana kallon labarai a aljazera yayinda maryama ke kwance a saman cinyarsa yana shafa mata jiki shiru tayi tana jin yadda tsigar jikinta suke mikewa kusan mintuna talatin tana kwance yana faman