Sashe 42
Mar'adams Part 4 Complete Hausa Novel · about 8 min read
d'auke sakamakon tuno irin rungumar da yayi mata a daren jiya ahankali bacci yayi awon gaba dashi washegari bayan maryama tayi sallah asuba ta koma ta kwanta ba ita ta tashe ba sai wajen karfe goma alokcin shi tuni ya dade da tashi yayi wanka yana zaune a gaban computer yana aiki sai dai bini bini yana duba halin da take ciki ta system yana kallonta ta cire kayan jikinta ta d'aura towel ta shige bathroom daga nan bai sake ganinta ba dan bai had'a camera da bath room ba." yana zaune har ta fito jikinta daure da towel ta nufi gaban dress mirrow tana gogge jikinta da gefen towel din dake daure ajikinta wanda hakan ya bashi damar kallon wasu wurare daga sansar jikinta ."saurin lumshe idanunshi yayi yana sauke numfashi ,ahankali yaga ta bude idanunta tana kallon cikinsu ko me ta gani yaga ta 'bata fuska har da jan tsaki sannan ta bud'e man shafawarta ta lakato ta soma shafawa fuskarta zuwa saman k'irjinta dake cike bamm da dukiyar fulani yadda ya tsaya yana kallonta haka itama yaga ta tsaya cak tana kallon abinda yafi daukar hankalinsa yana kallon manyan bobbo dinta masu kyau zooming yayi ya cigaba da kallon yadda brest kamar tasan yana kallonta ta dade tsaye tana karewa k'irjinta kallo tare da mulkesu da cream km duk sanda ta daura hannu ta kan brest dinta sai yaji wani irin mugun shock from no where ajikinshi .lokaci guda zuciyarsa tayi wani irin harbawa har jijiyarsa gabad'aya yanayinsa ya canza jikinsa ya kama rawa yaji kamar yaje d'akin ya sameta a yadda take yayi duk abinda yake so daita sai dai ya kasa tashi yana kallonta ta k'arasa wardrobe din da kayan sawarta ke ciki shirya kanta a lokacin da karfe sha d'aya ta buga ta koma bakin gado ta zauna shiru." lumshe idanunshi yayi yana ture system din gabansa yana mai jin haushin yan'uwansa domin Sun cutar dashi matukar cutarwa tunda suka haddasa mata mummunar tsoronsa acikin zuciyarta wanda kafin ya cire wannan tsoron sai sha bakar wahala itama ta sha bakar wahala ." Duk wuni ranar a tsorace maryama tayi shi acikin d'akin tsoronta kar asirin ta ya tono ta shiga uku a hannunsa da yan'uwansa da tayi imaini shima bazai barta barta ba , dan haka ta ki yarda ta fito parlour'n ma bare ta sauko dan bata kaunar abinda zai sa ta had'u da daya daga cikin halin gidan mahaifiyarsa ballanantana ta kaita da ganin yalla'bai ko wani daga cikin yan'uwansa yayinda mami sam bata damu da saukowarta ba sakamakon bata son ko ganin fuskarta." hajiya zulfa'u kam ta damu sosai da rashin ganin maryama sai take ganin kamar ko wani abu ne dan haka ta kira adamcy tana tambayarsa yace shi bai gidan tun safe amman tana lafiya tace "shikenan sai dai ganin har yamma bata sauko ba kamar jiya ta yunkura ta hau saman ta tsaya a parlour'n tana kiran sunanta." ta fito jikinta duk a sanyaye ta rakube can nisa daita hajiya zulfa'u dake kallonta tun fitowarta tayi murmushi tace "zo nan maryama ta miko mata hannuwanta ahankali ta taka ta isa inda take tsaye sai dai ta durkushe a gabanta tana gaisheta,hajiya zulfa'u tayi shr kawai tana kallonta ita dai bata san dalili ba Allah ya jarabeta da jin son yarinyar da tausayinta ko dan taga duk ahlin gidan basa sonta ne ?"Allah ya sani bata son abinda zai raba adam da ita domin sunyi matukar dacewa da juna gashi yarinyar tana da natsuwa sosai ."bayan ta amsa mata gaisuwarta ta kai hannu ta kamota ta ta zaunar daita akan kujera itama ta zauna kusa daita tana kallonta tana nazarin yanayinta gani tayi jini ya kwanta a gaefen idanuta na hagu tace "wani abu na damunki ne ?"maryama ta girgiza mata kai alamun babu" amman ya naga kamar baki da lafiya ?"muryata a raunane kamar zatai kuka tace "babu komai lafiyata lau ." "amman mai ya samu idanunki haka ?"shiru tayi ta kasa cewa" ko kina kewar gida ne ?"kamar tasan abinda yafi damunta kenan a yau din duk bata ji murya ko mutun d'aya daga 'yan gidansu ba ,hajiya zulfa'u ta kamo tafin hannu maryama cikin nata ta soma magana 'cikin tautausan harshen"abinda nake so dake maryama ki saki ranki damu domin kuwa mu ma tamkar iyayenki da yanuwanki muke ,mahaifiyar adam kuma tamkar uwa ce gareki dan haka duk abinda ke damunki ki sanar min ko ki sanar mata kinji karki duba halin ko in kula da take nuna miki idan kuma bazaki iya sanar mata ba to ni ki sanar min domin nima uwa ce agurin mijinki da mahaifinsa dani uwar d'aya uba d'aya muke ." Nan take hawaye ya cika idanun maryama har suka soma zuba sai dai bazata ta'ba fad'a mata matsalata ba ko abinda yalla'bai yayi mata a Daren jiya ba,dan tayi imani ko yan'uwanta bata jin zata iya fad'a masu "zan baki numbata duk abinda yake damunki a gidan nan ko ta bangaren adam ki kirani ki fad'a min zan baki sharawa idan na d'aukar mataki kuma zan tsawatar dan banji ajikina cewar ke din bata gari bace sai dai ki kara hakura da rayuwa kiyiwa mahaifiyar mijikin biyayya ki kyautata mata." " nasan a nuna ba'a sonka akwai zafi da ciwo amman kiyi hakuri wata rana zai wuce tunda ta fara magana maryama take kuka har da shesheka domin ta ta'bo mata inda ke mata ciwo Allah ya sani tana son mijinta kuma tana son zama dashi har karshen rayuwarta tana son ta kyautata masa amamn anfi karfinta, haka nan ma tasani ko babu batun sharadi a iya kiyayyarsu gareta ma ya isa ya tsoratata "nasan duk daren dadewa kowa zai dawo ya soki a yanzu fushi da jin haushin adam bai zauna da yaruwarsu bane yasa suke jin haushinki amman kisani kyakkwar dabiarki da yadda zaki muamulancesu ne zai sausauta komai agareki,ki daina kuka haka ta fad'a tana goge mata hawaye "karki damu da duk tarin kiyayya da damuwar da za'a nuna miki acikin gidan nan kullum ki dinga sauka kina gaishe da hajiya mami kamar yadda kika faro idan ma akwai abinda zaki mata kiyi mata Allah ya kawo mana mafuta Ina miki kyakkwan fatan alkhairi arayuwar aurenku ." Kusan mintuna talatin hajiya zulfa'u ta d'auka tare da maryama tana mata nasiha da zata wuce tace d'auko wayarki na saka miki numberta muryarta a sanyaye tace "wayar na hannu yall'bai murmushi tayi sakamakon jin yadda ta kirasa da suna na girma mawa "to shikenan idan ya dawo ki zo ki amsa ko kuma idan kin sauko da safe ni na karbi taki tare suka sauko har kasa ta gaishe da mami kamar jiya fuskarta a had'e ta amsa mata daga hakan kuma bata ce mata komai ba tana ganin tabawa ta shiga kitchen ta mike a natse tabi bayanta tana shiga tace" sannuku da aiki gabad'aya masu aikin suka juyo suka bita da kallo har ta samu waje ta tsaya tana kallonsu d'aya bayan d'aya fuskarta da bayanannen murmushi cike da girmama wa suka gaisheta tabawa tace "ranki ya dade akwai abinda kike bukata ne?" ta girgiza mata kai tana murmushi tare da kallon tsarin hadadden kitchen din kafin ahankali ta kai hannunta tana shafa gefen wuyanta." Gabad'aya duk suka natsu suna kallonta ko akwai abinda zata bukata ne yasa ta shigo shiru ne ya biyo baya "ranki dade ko wani abun kike so ?"tabaw ta sake tambayarta"karku damu bana bukatar komai kawai dai na shigo mu gaisa ne duk sukai shiru suna binta da kallo kafin daga baya duk suka koma bakin aikinsu tayi taku biyu ta tsaya kusa da tabawa tana duba yadda take had'a miyar waina "waina zaki yi ne ?"tace eh hajiya za'a yiwa ko kema ayi dake ne ?"ta k'arasa maganar da girmamawa maryama ta girgiza kai tace "aa ni ba komai nake ciki ba amman bari na kama miki aiki da sauri tabawa ta ware idanunta tana cewa "ranki ya dade ki rufa mana asiri idan yallabai yaga kina aiki ai karshen aikinmu yazo a gidan nan "maryama ta kai hannu ta dafa kafad'ar tabawa tace "karki manta ni matarsa ce kuma ko ba wannan lokacin ba dole zan shigo kitchen ko dan girka masa abinda zai ci tabawa ta d'an gyad'a mata kai "a ra'ayina nafi son na girkawa mijina abinci da hannuna domin na samu ladan aure ".suna cikin magana mami ta shigo kitchen din tare da rungume hannunwanta duka a k'irji tana kallonsu d'aya bayan d'aya fuskarta babu annuri take maryama tai shiru yayinda masu aiki kowacce ta juya ta maida hankalinta akan aikinta mummunar kallon da mami tai dingawa maryama ne yasa ta ra'ba ta gefenta ta fice daga kitchen din tana fita mami tace "me ya shigo daita ?" Nan take tabawa ta fad'a mata gyad'a Kai tayi sannan ta fito zuwa parlour'n bata ga maryama ba da alamun ta koma sama karfe tara na dare adamcy ya shigo sai dai bai nemi inda take ba dan ya rigada yasan duk halin da take cikin a gidan, bayan ya gama shirin kwanciya ya janyo laptop dinsa ya jona a caji ya shiga bangarenta alokcin itama da alamun wanka ta fito dan tana tsaye tana shirya kanta ne wata yar riga hamless yaga ta dauko ta saka daidai cinyarta ko bra babu ajikinta hakan ya bawa adamcy damar hango kan nipples dinta dake 'cikin rigar suna tsukonoshi , idanunshi kyam akan kirjinta ko kiftawa baya son yi ta feshe ilahirin jikinta da turaren tayi tsab daita ainihin sihirtaccen kyawun surar jikinta ya sake fitowa muraran adamcy dake zaune yana kallonta duk ilahirin jikinsa babu inda baya rawa yayinda jikinsa ya soma mutuwa yana samun special reaction ajikinsa most especially jijiyarsa dake harbawa da sauri sauri ya dinga ji tamkar ana watsa masa ruwan tsanyi ne ajikinsa.ahankali ya lumshe tsumammun idanunshi ya sake budesu fess akanta har lokacin tana nan tsaye gaban wannan karon ba komai take ba sai dai tayi shr alamun tunani 'cikin mutuwar jiki ya kamo lip's dinshi na kasa ya soma tsosa ahankali ahankali yana ji tamkar ya fixgota ta cikin tv ya soma ladabtar daita ta hanyar saukewa kanshi tarin sha'awarta na tsawon shekaru ,bashi