← Book details Mar'adams Part 4 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 34 OF 94

Sashe 34

Mar'adams Part 4 Complete Hausa Novel · about 8 min read

BOOK 4 *AYSHA A BAGUDO* WATTPAD @HAUESH AREWABOOKS USERNAME AYSHAABAGUDO bismillahirrahmanirrahim Page 13 shiru yayi kawai yana kallonta cikin hasken dum light,dan take kwakwaluwarsa ta kulle ta samu shutdown na wani lokaci kafin daga baya ta dawo daidai ta fara aiki tare da mikewa zaune.yayi kamar yadda tayi,wani kallon galala adamcy ke jifan maryama dashi wanda yafi kama dana rainin hankali,sannan ya gyara zamansa ya cigaba da kallonta,dan tunda tayi mganar yake kallon k'irjinta da fuskarta,hannuwanta ta kai ta kare kirjinta tare da kawar da fuskarta gefe tana jin wani irin mummunar fad'uwar gaba da tsoro shi kuwa kallonta yake yana kare ma jikinta kallo ahankali ya dawo da fuskarta garesa ya soma k'ok'arin kamo yatsun hannunta cikin nashi cikin sa'a ya kamosu ya matsesu gam cikin tafukan hannunsa yana cigaba da kallonta tamkar wata sabuwar halitta da dabam".nan take jikinta ya kama rawa,cikin tsananin tashin hankali ta fixge hannunta"ni ka sakar min hannu ka matse min hannu ciwo yake min ." fizgota yayi gaba d'aya zuwa jikinsa ya sake rungumeta tsam tsam yana sauke naunauyen ajiyar zuciya da numfashi atare."wani irin sanyi dadi ne ya dinga bin ko wane ga'ba dake aiki a jikinsa sakamakon had'uwar da jikinsu yayi guri d'aya, bakinsa ya kai daidai saitin kunnenta yana sauke mata numfashinsa dan gabad'aya ya rasa ma abinda zai ce dan bai ta'ba ganin yar rainin hankali irinta ba ,anya kuwa gaskiya ta fad'a masa ba wahalar ta sha a hannun tsohon mijinta bace yasa ta fad'a masa haka ?"my princess!"ya kira sunanta cikin wata irin kasalalliyar murya mai tsananin kashe sansar jiki ,duk da tana cikin wani hali mai wutar misaltuwa amman sai data ji sauyi a gabad'aya ilahirin jikinta"mai yasa baza ki bari muyi rayuwar auren mu cikin natsuwa da kwanciyar hankali ba ?"tai shiru zuciyarta na wani irin bugawa da matsanancin karfin gaske" "nasan may be dan kin sha wahala ne a baya yasa kika fad'a min haka amman ni bazan miki yadda zakiji ciwo ko zafi ba hasalima zan biki ahankali ne ta yadda zaki ji dadin dake cikin rayuwar aure." hawaye ne ya shiga zubo mata ganin bai yarda daita ba, ta runtse idanunta gam tana kokarin zare jikinta daga faffad'an k'irjinsa da take jinsa a murd'e shi kad'ai ma ya isa ya canza ma mutun lissafi "wallahi da gaske nake ban ta'ba yi ba shi yasa nake jin tsoro"ta k'arasa mgnr muryarta a tsarke cike da rauni, lokaci d'aya kuma hawaye na gangaro mata sake rungumeta yayi a jikinsa a yanzu kam bazai karyata mganrta ba domin dukkanin alamu sun nuna masa haka ,sosai ya dinga jin soyayyarta na sake ratsa shi ,sannan ya dinga ji aransa kamar zaiyi wuya a samu kamarta hakurin ,natsuwarta sadaukarwa kamun kai kai komai ma, tabbas ba duk mace zata sha irin wahalar data sha irin haka ba kuma ace virgin ce. " bazan ta'ba son wata ba kamar ki soyayyarki ita kad'ai ce bangon da zata k'ara danganta ni dake bayan ke babu wata acikin zuciyata .""to yaya ma zai iya had'a soyayyarta da wata ?"never!" ya furta a kasan ranshi." sosai zuciyarsa tayi sanyi ta k'ara samun natsu wa akanta ya sake kamota ya rungumeta tsam kamar zai rabata gida biyu yana shafa gadon bayanta "dan girman Allah yalla'ba ka barni karka min komai "!bakinsa ya sake kai wa kunnenta ya soma mata magana cikin rad'a"naji bazan miki komai ba kiyi kwanciyarki kinji my princess ,ya gyara mata pillow sannan ya kwantar daita ya lullu'be mata jiki da tautausan blanket dinsa dake makale da sanyayyen kamshin turarensa ,shi kuma ya sauko ya samu guri ya zauna akan kujera yayi rigingine tare da tsura mata tsumammun idanunshi daga inda yake yana kallonta cikin hasken da bai gama haskaka d'akin ba ."a hakan zaka d'auka shima bacci yake nan kuwa idanunshi biyu hasalima wani abu yaji yana tsarga masa ta koina a jikinsa tamkar ana jona masa wutar lantarki wanda baya raba d'ayan biyu na tsananin sha'awarta ne sai faman mutsu mutsu yake, a qalla ya d'auki sama da mintuna goma shabiyar zaune yana tunanin dalilin da yasa wani abu bai shiga tsananinta da tsohon mijinta ba ." wani irin sauyi mai tsanani ya dinga ji a gaba d'aya ilahirin jikinsa ya dafe mararsa da tayi masa wani irin d'aurewa dan gabad'aya wani irin sha'awa ne ke sake taso masa ,runtse idanunshi yayi kawai sannan ya yunkura ya tashi dafe da mararsa ya nufi bathroom ,ita kuwa duk halin da yake ciki tana hankalce dashi ganin yadda ya shiga bathroom dafe da mararsa yafi komai d'aga mata hankali tsoronta kar ya fito ya farmata yasa tana jin ya kullo kofar bathroom din ta zabura ta mike ta rarumo zaninta ta d'aura ta fito da sauri ta nufo parlour'n ,d'akin datai k'ok'arin shiga d'azu ya hanata nan ta isa jikinta na rawa ta soma k'ok'arin bud'e kofar ganin ta bud'e ta soma kokarin zare key tana gama zare key ta shige ta maida kofar ahankali ta rufe tare da murd'a key sai dai tsananin tsoron dake tattare daita yasa ta zare key'n din batare data san tayi hakan ba . Sai a lokacin ta d'an samu natsuwa ta samu waje abayan kujera ta taku'be jikinta na wani irin bari ." shi kuwa yana can yana watsawa jikinsa ruwa ko zai rage jin abinda yake ji akanta ,yana fitowa daga bathroom idanunshi ya sauka akan gadon sai dai wayam ya gani babu ita babu alamunta ."cikin sauri yay filinging da towel din da yake goge jikinsa ya zira jallabiyarsa ya fito hankalinsa a matukar tashe ,sai dai karin tashin hankalinsa bai ganta a parlour'n ba,da sauri ya karasa ya bud'e kofar d'akin dake kusa da nashi daman kuma yayi tunanin haka ya shiga ya duba koina bai ganta ba ,shiru yayi yana sauke numfashi da sauri sauri dan wani irin lugud'e bugu zuciyarsa ke yi sannan ya fito daga parlour'n ya sauko zuwa falon kasa amatukar rikice yake kiran sunanta" "maryama !! kina Ina dan allah ki fito babu abinda zan miki ai kinga akan kujera na kwanta karki min haka ,amman shiru kofar fita daga bangaren mami ya nufa ya duba numbobi yaga kofar a rufe take alamun ba'a fita ba ."nan take zuciyarsa ta d'an samu natsuwa domin dai ya tabbatar tana cikin gidan a natse ya juyo ai yana gama juyowa tsumammun idanunshi suka sauka akan mami tsaye cikin zuba masa idanunta ." Kallo d'aya tai sama daga sama zuwa kasa ta fahimci ba'a haiyacinsa yake ba tace "adamcy menene haka ?"tai masa tambayar cike da 'bacin rai."ya kai hannunsa ya d'an tsotsa keyarsa yana tunanin abinda zai fad'a mata bai gama tunani ba yaji ta sake jiho masa wata tambayar "me ne ne zaka damu mutane ka hanasu bacci ? ahankali ya juya kanshi kamar wani k'aramin yaro tare da had'e hannayensa waje d'aya yana kallonta cikin kasalalliyar murya yace"amm....." amm.... daman mar.."sai kuma yayi shiru ya kasa k'arasa mgnar "daman me ?"no babu komai sweetheart !"ya tsinci kanshi da fad'a mata haka atakaice tare da nufar step har yayi taku biyu ya sake jiyo sautin muryarta "ai kaga irinta nan, sai da'aka ce karka auri yarinyar nan kaki ,yanzu kaje ka aurowa kanka bagidajiya,ai duk abinda idanuwa suka gani su suka jawa kansu".tana gama fad'ar haka ta juya a fusace ". hankalinsa a matukar tashe yabi bayanta da kallo cike da matsanancin mamaki sai daya d'auki more then two seconds a tsaye yana kallon bayanta da tsantsar mamaki a fuskarsa yana assessing maganarta"sai da'aka ce karka auri yarinyar nan kaki ,yanzu kaje ka aurowa kanka bagidajiya,ai duk abinda idanuwa suka gani su suka jawa kansu ya sake maimaitawa kanshi maganarta still yana tsaye yana kallon bayanta sai dai zuwa wannan lokacin fuskarsa d'auke take da mummunar'bacin rai domon kuwa ya gama gane ma'anar maganarta dama inda maganar ta dosa"yanzu maryama zata kira da kalmar bagida jiya?"a duk lissafinsa ya tabbatarwa kanshi ba bagidajiya bace, abu ne da mutun bai saba ba bare kuma ya had'e mata da bakunta da bullying dinta da ya'yanta sukai mata ." Sosai maganarta ta doki kunnuwansa ta wuce har cikin zuciyarsa ta k'ara masa damuwa akan wanda yake ciki "yanzu akan ya auri zabin ransa muradin ransa yasa sweetheart ta canza masa irin canzawar da bai yi tsammani daga gareta ba ?"duk yadda yake son ya kawar da zafin zuciyarsa akanta da ya'yanta lallai so take ta tunzura shi hakurinsa ya kare yayi abinda bazai so faruwarsa ba ,a yanzu ban cin ita din mahaifi ya ce da shi kad'ai yasan matakin da zai d'auka akan wannan kalmar data fad'a akan marayama girgiza kanshi yayi sannan ya haye sama biyu biyu ya dinga taka step bayan kujerun parlour'n ya soma dubawa dan kwata kwata hankalinsa bai kai ga zata shiga d'akin sirrinsa ba."bayan ya gama duba kaf bangarensa bai ganta ba kuma ya tabbatarwa kanshi tana cikin bangaren ya kai hannunsa ya shafa goshinsa can kuma ya dawo da hannun kan lip's dinsa yana shafawa yana zurfafa tunaninsa." kai tsaye yayi tunanin ya duba cctv aiko da wani irin sauri ya koma d'akin sa acan ya gano d'akin data shiga da wani irin sauri ya fito ya nufi d'akin yana murd'awa yaji kofar a kule alamun ta kulle ta ciki goshinsa ya dafe kafin ahankali ya soma kiran sunanta ahankali yana bata umarnin ta bud'e ,tana jinsa ta sake takure jikinta waje d'aya shiru yayi yana tunanin yana kallon kofar dan bazai ta'ba yin ganganci buga kofar ba bare sweetheart ta samu wata damar da zata ci masu mutunci .har zai juya idanunshi yaga key kwaya d'aya a kasa da alamun wajen zare sauran key'n din ne ya fita wani sanyayyen numfashi ya sauke da hanzari ya duka ya d'auka ya bud'e d'akin ya shiga koina duhu ya kai hannunsa jikin bango yana neman abun kunna wuta ai yana gama kunnawa nan ma yaga wayam bai ganta ba ." batare da 'bata lokaci ba ya fara duba bayan doguwar kujera dake d'akin anan ya ganta kwance a bayan kujera kwaya d'aya dake ajiye a d'akin ta kundundune jikinta waje d'aya jikinta sai bari yake ,da wani irin saurin ya janyo kujerar gaba tare da durkushewa a gabanta kamar zai yi
Chapter 34 · 0% Book details