← Book details Auren Wata Tara Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 65 OF 129

Sashe 65

Auren Wata Tara Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Motar waye naga an sauke ki," A matuk'ar firgice ta d'ago ta Kallesa sai kuma.ta kalli motar da har lokacin yaki tafiya sosai Zarah ta shiga rud'u "nace motar waye kika fito.daga ina kike tun d'azu nazo school d'innan ina jiranki ina kikaje?Zarah rudewar da tayi batasan sanda taji hawaye na zubo mata ba hangosu da Asmy tayi ya sanya gabanta fad'uwa tasan Hafiz yazo tun d'azu yake jiran Zarah dalilin karyar da zatayi masa ma ta rasa hakan ya sanyata kin fitowa Dan tunda ta fito ta ganshi tamaza ta koma yanzunma fitowa tayi Dan ta kirkira k'aryar da zata masa saita iske abunda ya k'ara tayar mata da hankali tundaga saukar Zarah a motar MD har zuwa yanzu da Hafiz ke daga mata murya akan idonta komai ya faru dak'yal tayi jarumta tare da karasawa Inda suke ta ce " Ya Hafiz Kaine kuwa da gaske ko gizau ne kake mun?Dukda Hafiz hankalinshi tashe yake bai hana yiwa Asmy murmushin k'arfin hali ba ya ce "Nayi 30 minutes a nan nayi ta Kiran layin ta kashe shiyasa na tsaya najirayi b'ullowarta ashe mugun Abu zangani dubi motar da aka sauke Zarah a ciki Asmy na tambayeta waye shine Kinga ta durkushe ta sanyamun kuka"Kallon motar Asmy tayi saikuma ta kalli Hafiz ta ce " wayyo ya Hafiz Motar malamin muce kasan itace amirar makaranta to shine dazu da safe aka gayyacesu 'a wata makaranta da za ayi safka shiyasa ya tafi da ita saboda shine shugaban mss din na makaranta kaga kuma sundawo inaga to sabani ma kukayi Dan itama bata wuce 30 minutes ba da fita"y'ar Ajiyar zuciya Hafiz ya sauke ya ce "Dukda haka bai kamata ta shiga ba motarsa ba sanadin yace yana sonta ne ko yayi sha'awar wani Abu daga gareta Gaskiya bazan lamunta da haka ba " Tsohone fa yaya Hafiz Ya haifeta sannanma matanshi hud'u kuma malami ne ustaz kuma ba ita kadai suka tafi ba yanzu haka da diyarsa a cikin motar "Ajiyar zuciya Hafiz ya sauke ya ce " Wlh har Naji sanyi karkiji yanda hankali na ya tashi Ina son Zarah sosai Asmy kinsan da haka Ina tsananin kishinta da zanso ko kuda bazan bari ya tab'a ta ba sannan Ko k'aramun yaro bazai kallemun ita ba please Ki dinga lurarmun da ita na damk'a miki amarta a hannunki "murmushi asmy ta saki. Ta ce Uhm su ya Hafiz manyan kishi karka damu ai aski yazo gaban goshi insha Allah nan da wata biyu munbar sch d'innan kaga kuwa kana gab da mallakar kayanka " kasaitaccen murmushi Hafiz ya saki ya ce "Gaskiya kinci kyauta fa " Y'ar Dariya Asmy tayi nan ta gaishe shi kafin ta wuce Lectures durkusawa Hafiz yayi daidai saitin kunnanta ya ce "Sorry my bride banzata haka abun yake ba kiyi hakuri" Shiru Zarah tayi ta cigaba da shasheka"Oh My god "ya fad'a yana daga kanshi kafin ya k'ara cewa " Kiyi Hakuri my Zarah Bazan sake ba Kinga laifinkine da bakiyimun bayani ba "Sai lokacin ta d'ago turo baki tayi tare da cewa " shine saika rufe ni da fad'a "wara idanu yayi ya ce " ni na isa nayiwa gimbiyata fad'a kiyi hakuri baki ma murnar gani na ki Mike please "Goge hawayenta tayi tare da mik'ewa Shima ya Mike murmushi suka sakarwa juna Zarah ta ce " amma kayi surprised Dina sosai ya Hafiz "Fuskarsa sauke da murmushi ya ce " Daman surprised d'inki naso yi shysa banfad'a maki na dawo ba "Yaushe ka dawo" Jiya Tun jiyan naso nazo naga gimbiyata yanda ta koma sai dare yayi Kinga Ko yanda kika k'ara kyau da komai my Zarah Gaskiya nayi sa'a fa ba kadanba "murmushi Zarah tayi tare da rufe fuska ta ce " kai ya Hafiz kaima ka k'ara kyau wlh"ai ban kaiki ba ke fa komai kika kara Ai ji nake kamar na janyo gama sch d'innan naku fa ji nake kamar a daura mana Aure yau"Nan ma Kara rufe fuska tayi ta ce "kana bani kunya fa ya Hafiz " Ai Gaskiya Ce dole na fad'a "karan tashin motar da tajine ya sanyata Kallon wurin a guje taga motar tabar wajen tab'e baki tayi a zuciyarta ta ce " ko ubanme ya tsaya tun d'azu yi mtwss"hafiz ko baima lura da tashin motar ba dan gaba daya hankalinsa yana gurin zarar sa sosai Zarah suka sha fira ita da Hafiz Wanda sosai ya dinga fallasa mata sirrin zuciyarsa da yanda ya matsu lokacin bikinsu yayi lectures din da bataje ta ba kenan Har lokacin sallah yayi yana nan yaje yayi salla ya dawo Hafiz shine bai tafi ba sai Bayan la'asar sosai yaji dadin arba da abar k'aunar tasa Zarah ko hostel ta koma ina ta samu Chuchu nayiwa Asmy kitso waje ta samu ta zauna tana hararar Chuchu ta ce "Shine ko kije ku gaisa" Tana turo baki ta ce "Na hangesa da na dawo daga lectures keda kikasan ni bamun yayiba har zanje mu wani gaisa ni banga abunda kika gani kikeso a jikin wannan mutumin ba wlh kikaga yayana saikin manta da wani Hafiz yayana ya had'u y'an mata har tuntube suke a kansa dashi kuka dace wlh tako ina kunyi match har cikin zuciya ta nake maganar nan wlh Zarah zanzo ki zama mallakin yayana saboda kece type dinsa yayana yana son mace mai ilimin addini da na boko,yana son mace mai kamun kai da Jan aji da tarbiya ,yana son mace mai tsafta gayu iya girki da sauran duk abunda yake so game da mace kina da su momcy tako ina kin hadu baki da makusa wlh Ammy ma tana son ki zama surukarta Saboda karkiga yanda take sonki" girgiza kai kawai Zarah tayi ta ce "Mubar maganar nan Chuchu kiyi mana fatan alkhairi kawai" tab'e baki ta kumayi Chuchu ta ce"Allah ya kaimu lokacin A nan Funtua ai za ayi ko?Eh "Insha Allahu tun satin bikin zantaho dukda ba son Angon nake ba" Dariya Asmy tayi ta ce "Kina yanda kikaso Chuchu wai Bason Angon kike ba keda bake zaki zauna dashi ba ita ai ta gani kuma tana so" y'ar Dariya Chuchu tayi ta ce "Allah da gaske nake kawai ina taya yayana bakincikin rasa ta da yayi ne" Asmy na Dariya ta ce "Auta baki da dama to shi Yayan naki cewa yayi yana sonta da zaki dinga tada jijiyoyin wuya" Ai nasan idan ya ganta din zaice yana so shiyasa "Sosai Asmy ta shiga yiwa Chuchu Dariya Inda suka dinga hirar Wanda Zarah bama tasan sunayi ba Dan tuni bacci yayi awon gaba da ita kallonta Asmy tayi tace " ikon Allah Daga Hira sai Bacci baccinma na la'asr"Chuchu ce ta ce "Jiyama wlh bata gama lecture ba tataho wai bacci takeji saida tayi kusan awa Ukku tana bacci" zuwan driver d'inta ne ma yasa na tasheta saboda Yusuf ya kirani yace ana kiranta"Asmy ta ce "Kuma fa wlh da bata da yawan bacci Zarah baccin rana ma ba fiya damunta yayi bare na la'asr " Kilan hada gajiya"hakane kuma Asmy ta fad'a "Zarah itace bata tashi ba sai magriba Shima saida Asmy ta tasheta tayi sallah Ranar a hostel ta kwana " kwananta biyu bata koma gidan MD ba Wanda sosai taji dad'in Rashin waiwayarta da baiyi ba cikin kwana na hud'u ta fito daga lectures ta Hango wata dalleliyar mota a gab da hostel d'insu har tayi gaba "mamy" ta tsinkayi muryarsa daga mota "harta tsaya saikuma ta juya ganin ta Cikin mota yayi mata magana amma da.Alamun saida ya Zage glass din motar waigawa tayi gabanta na fad'uwa Allah yasa ba Mutane sosai a wajen da batasan wasu mutanen suyi mata fassara harzatayi gaba saikuma ta tuno karya biyota ko ya kamata a gaba mutane ta shiga ukku Juyawa tayi kamar wacce kwai ya fashewa a ciki ta nufi Inda motarsa take tana shirin shiga taji wasu y'an mata na gefenta wata daga cikinsu na cewa " Ai daman bana fad'a muku ba wlh salahan nan kamar na Allah sunfi shek'e ayarsu yanda suke so ana fakewa da hijab ana yanda akaso yanzu wlh idan ka fad'awa wani saiya karyataka amma da yake akan idonku ai kungani daman na fad'a muku amirar nan cikin wayau take barikancinta mune dai da muka fito namu fili aka fi gani"Juyawa Zarah tayi ta kallesu dukda maganar da ta jefe ta tayi mata ciwo girgiza kai tayi tare da yi musu murmushin da yafi kuka ciwo ta bud'e motar ta shiga taja ta rufe tana maida hawayen da suka zubo mata"Ko Kallon MD batayi ba ta hade kai da gwuiwa ta fara hawayen zarginta da wasu daga cikin sch din suka fara Wanda tasan duk shi ya ja mata Jan motar yayi batare da yabi ta kanta ba a hanya ganin har lokacin kamar kuka ta ke "ya sanyashi kallonta a takaice ya ce " me akayi maki"Kamar mai jira nan ta d'ago tana Goge hawaye Cikin muryarta ta shagwaba ta ce "Y'an sch d'inmu ne suka fara zargina akan daukata da kazo please kadaina zuwa sch d'inmu kar mutane su farayimun wani irin kallo" hankalinshi na kan driving din da yake ya ce "Bani naja maki suke zarginki ba samarin da kike kawowa suka ja maki yaushe na tab'a zuwa wajenki idan ba Yau ba?ni ba samarin da nake kawowa ko motar saurayi bantaba shiga ba ," ta fad'a tana turo baki"Shi Wanda yazo rannnan din har kina masa murmushi shiba saurayinki bane?ohhh ya Hafiz kake nufi?Harararta yayi ta gefen ido ya ce "Bansaniba" Murmushi tayi ta ce "Aishine Wanda zan aura wata guda da Gama school dina za Ayi bikin" tsaki yaja tare da cigaba da tukin sa "Tab'e baki Zarah tayi a ranta ta ce "Mai mugun hali kawai" Duk Auren da akace an daura Koda a wasa ne ya dauro kuma Aure ne ingantacce inhar ba rabuwa akayi ba Mu'amula da maza ko abunda yayi kama da makamancin haka haramun ne ki bari lokacin da Na rabu dake kinyi mu'amula da duk Wanda kikaga damar yi amma yanzu ina nusar dake girman zunubin da kike d'auka kuma nasan kema kinsan da hakan saboda kina da Ilimi karki d'auki nayi maganar nan da wata manufa a a
Chapter 65 · 0% Book details