← Book details Auren Wata Tara Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 45 OF 129

Sashe 45

Auren Wata Tara Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Na ce Wace y'ar kutumar uban ce wannan Mustapha " Kallonta MD ya tsayayi da mamaki Ganin bazai bata amsa ba Amera ji tayi kamar a mafarki cikin zafin nama tayi kukan kura tare da shako wuyan Zarah cikin wani irin Hargagi ta ce "zakisan kin shiga gona ta Dan kutumar ubanki shegiya y'ar iska karuwa yau saidai uwarki ta haifi wata amma yau d'innan saikin bakunci lahira tunda har kika iya bin mijina bakisan Kallon mijina ma mace batayi bare har na ganku tare Tabbas ajaline ya kawoki gidan nan Dan saidai a fitar da gawarki daga gidan nan billahillazilla'ila illa huwa" iya rudewa Zarah ta rude ga ta kasa kwatar kanta daga shak'ar da Amera tayi mata Cikin b'acin rai MD ya daka mata Tsawa ya ce "Sakarta Amera kafin ranki ya b'aci banason hauka" Cikin kuka da Hargagi Amera ta ce "Wlh saina kasheta " Kokarin kwatar Zarah MD ya fara amma ya kasa saboda cike da zuciya Amera tayi ruko ganin zata illatata Dan harta fara numfaffashi ya sanya MD d'auke Amera da wani irin gigitaccen Mari Wanda ba shiri ta saki Zarah tana dafe kumcinta ta ce "Ni ka Mara Mustapha " An mareki din stupid mahaukaciya da kishi zai haukatar dake kasheta zakiyi ko Me?ka fad'a kome zaka fad'a indai akan wannan ne na shirya wlh kaji na rantse saina kashe tsinanniyar yarinyar nan saidai nima a kasheni munafiki maci amana ashe Fasik'anci kake shiyasa kake tahowa k'asar kak'i waiwayata ashe karuwai kake kawomun har cikin gida wlh da wani ne ya bani labari bani na gani da idona ba zan yarda ba fasiki maci ama....bata k'arasa maganar ba sakamakon Saukar Marin da taji Tass tass har guda Ukku "wani ihu ta buga tare da nuna kanta ta ce " ni ka mara akan wannan karuwar mustapha Aiko zakasan ka mareni ta fad'a tana tunkarar Inda Zarah ta durkushe ta na Maida numfashi sosai kalaman Amera ke dakar mata zuciya ganin tayo Wajenta ne ya sanyata saurin tashi ta boye Bayan MD sai Lokacin ta samu damar fashewa da kuka "Wlh Amera kika k'ara tab'ata zakiga b'acin raina yanda bakiyi tunaniba wai hauka ne kike kome me kike shirin aikatawa saboda kishi ya rufe maki ido" Cikin kuka Amera ta ce "zakaga hauka Mustapha zakasan ka taboni ka jira fitowa ta ta fad'a kamar wata mahaukaciya tare da Yin hanyar Ciki ganin haka ya sanya Zarah rudewa cikin kuka ta ce " Dan Allah ka fitar dani daga gidannan na shiga ukku "MD Yama rasa yanda zanyi Cikin Sauri ya nufi parking space tare da dauko mota Zarah hada tuntub'enta wajen shiga tana shiga sukaga fitowar Amera hannu d'aya da tabarya hannu d'aya kuma lafceciyar wuk'a mai kamar Adda iya rudewa Zarah ta rude Duk Addu'ar da tazo bakinta yi take cikin kuka ta ce " Kayi Sauri karta karaso na shiga ukku ni Fatima Wannan wace irin masifa ce "ta fad'a tana fashewa da kuka da karfi yaja motar Horn D'aya yayi mai gadi ya bud'e masa da gudu Amera ta nufo su tana ihu tabarya da wuk'a a hannunta ta ce " ka bud'e musu get suka Fita wlh a bakin aikinka"lokacin har motarsu ta fita Wata nauyayyar Ajiyar zuciya Zarah ta sauke amma dukda haka gabanta fad'uwa yake MD ko mamaki ne cike a ranshi bai tab'a tunanin haukan kishin Amera yakai haka ba wata irin zufa ce Ke keto masa Har suka isa Zaria cikinsu ba Wanda yace uffan daidai kofar A B U yayi parking Tare da ciro bandir din y'an Dubu dubu ya mik'a Mata girgiza kai tayi har lokacin gabanta fad'uwa yake ta ce "a a nagode " wani irin kallo yayi mata tare da cewa "Bana bada Abu a a mayarmun doka ta ce wannan ki kiyaye kinga damar ki yaddasu ko kiyi sadaka wannan ba damuwata ba ce " Amsa Zarah tayi harzata fita Ya riko hannunta Wanda dukda suna cikin tashin hankali bai hanashi jin shock ba makulli ya damka mata ya ce "Ki kwashe kayanki ki koma Gidana dake nan karna dawo na iske baki koma ba" Tana shirin fashewa da kuka ta ce "Dan Allah karkace saina koma wlh banajin dad'in zaman Chan" Umarni na baki ba shawara ba sannan karki koma kiga Abunda zai faru"hawaye na zuba a idonta ta ce "To taya zan iya zama a wannan gidan ni d'aya wlh ni bazan iya zama ba " wani tunani ne yazo masa kuma hakane bazata iya zama gidan nanba ita daya Dagowa yayi da Kalleta Da har lokaci hawaye basubar zarya a idonta ba ya ce "Gobe zanshigo Garin Around 4 Idan na tafi saiki koma hostel din hakan yayi miki ai ko?saita samu kanta da daga masa kai " A hankali ta fita daga motar harta bace masa gani baibar kallonta ba kafin ya sauke ajiyar zuciya kanshi ya had'a da sitiyarin mota yayi minti goma batare da ya dago ba ya rasa abunda yake masa dadi Dak'yal ya iya tashi yayi driving ya juya Kd tun a hanya yakejin ringing wayarsa bai dagaba ganin missed call d'in yayi yawa ya sanyashi dubawa yana ganin Number Ammy ce saida gabanshi ya fad'i a sanyaye ya d'aga sabon kiran d'aya shigo "Duk Inda kake kazo ka sameni a gida yanzunnan " Yanayin yanda Ammy tayi maganar ya tabbatar masa da tana cikin fushi a sanyaye ya ce "Gani nan zuwa ammy'" Bata amsa ba ta katse kiran "numfashi mai zafi ya fesar kafin yaci gaba da driving cikin Rashin nutsuwa Koda ya isa kd kai tsaye gidansu ya nufa A palour ya tarar da Ammy sai Chuchu gefenta tana Danna waya Amera na Kan sopa itama ta hade kai da gwuiwa tana kuka girgiza kai kawai yayi Dan yanzu kam ya tabbatar da kishin Amera ya wuce yanda yake Tunani Kennan Ammy tazo ta sanarwa " waje ya samu a palourn ya zauna Ba yabo ba fallasa Ammy ta amsa gaisuwar da yayi mata sannan Chuchu ta gaisheshi kamar ko yaushe yanda take gaisheshi Ajiyar zuciya Ammy ta sauke tare da Kallon MD ta ce "Yanzu Amera take zomun da wata magana wacce ta kusan girman tunani na hakane gaske ne koko?Batare da nuna alamun damuwa ba ya ce " wace magana kenan Ammy"Kallon Amera Dake kuka har lokacin Ammy tayi ta ce "maimaita abunda kika fad'amun " Kamar mai jira cikin kuka Amera ta ce "da Mace na kama su a gida na " Da mamaki MD yake kallonta Cike da mamaki ya ce "Kika kamamu Amera fa kikace zaki iya rantsewa da Qur'an Akan kin kamani da wata mace " Tana kuka ta ce "ba kamawa na iskanci ba Ai kamawa na bahaushe kun fito tare kaida ita daga pournmu"Kallon mamaki Ammy da Chuchu suka dinga binta da su Chuchu ta ja dogon tsuka ta ce " Daman ba na fad'a maki ba Ammy saikace dai bakisan halin yaya ba nasan wallahi yaya bazai tab'a aikata abunda tazo ta fad'a ba sharri ne kawai take neman K'ulla masa dan munafurci Mtwsss "daga mata hannu Ammy tayi ta ce " Karna karajin bakinki a nan Auta Amera sa'arkice karna kumajin bakinki a maganar nan "Tana turo baki Chuchu ta tashi tare da gallawa Amera harara da itama Amerar hararartata ta ke Dan daman Chan basa jituwa tabar palourn tana Jan tsoka maida hankalinta wajen Amera ammy tayi ta ce " Fad'amun gaskiyar abunda ya faru"Har lokacin kuka ta ke....nan ta labartawa Ammy komai da ta gani iya gaskiyarta har tafiyar da yayi da ita da shakar da tayiwa yarinyar.Kallon MD Ammy tayi ta ce "Hakane babana" Batare da tsoro ko shakku ba ya ce "Hakane Ammy" Me ya hadaka da mace babana har cikin gidanka kuma Alhalin ba kowa a gidan"?Tambayar da tun farko ya kamata tayi Amma ta kasa"ya fad'a ya na Hararar Amera "To yanzu fad'a mana meye alakarta da ita "Numfashi yaja kamar bazai magana ba saikuma.ya d'ago ya ce " Kanwar Jaber ce Tare suka zo bata da lafiya ya dawo da ita daga Asibiti sai akayi mashi kiran gaggawa Compony kasancewar gidana ne Inda yafi kusa da Inda yake shine ya nufo gidana da ita ya tafi kasancewar bata lafiya Saiyace ta jirashi anan kafin ya dawo ganin ya jima ne ya sanya nace bari mu fito Kawai na sanya driver ya kaita gida shine fa "Salati Ammy tayi ta na kallon Amera ta ce " Tofa kinji Kike tada jijiyoyin wuya yanzu Dan Allah wannan dame yayi kama Wannan wani irin zafin kishi ne gareki Amera ba bincike ba komai kin kama y'ar mutane da Duka bama lafiya gareta ba yanzu Dan Allah iyayenta muna mutunci dasu sukaji zasuji dadi kuwa?Goge hawayenta Amera tayi ta ce "Kiyi hakuri ammy bankawo komai a raina bane sharrin shaidan ne " tab'e baki Ammy tayi ta ce Allah kiyaye "ta Mike tabar palourn cike da jin Haushi Matsowa tayi kusa da MD da ya lumshe idonshi tayi cikin sigar Ban hakuri ta ce " Kayi hakuri honey Dan Allah"Bai tanka mata ba haka bai bata amsa ba "Tana shirin fashewa da kuka ta ce " Please honey Dan Allah ka yafemun kasan kome nayi nayishine saboda sonda nake maka tsananin kishin Kane ya sa na aikata komai "Dagowa yayi lokaci guda d'aya Kalleta yaga irin yanda idonta yayi ja " girgiza kai yayi ya ce "kishi hauka ne Amera?haka ake kishi?yanxu da kin Kashe y'ar mutane ki ce me ?So kike ki ja mana bala'i ,sannan ji maganganun batancin da kika dinga fad'amun matsayina na mijinki hakan da kikayi tarbiya ce,Ko angaya maki haka ake kishi" kama hannunshi Tayi tana kuka ta ce "Kayi hakuri honey bana iya control d'in Kaine ne akan kishin da nake maka " tab'e baki yayi baice Mata komai ba "Kayi hakuri Dan Allah Karkayi fushi?Dagowa yayi yaga yanda tayi kalar tausayi lokaci guda saiya sakar mata murmushi ya ce " ya wuce my merah"Ajiyar zuciya ta sauke tare da kwancewa jikinshi ta Ce"Thnks mijin da yafi na kowa "a hankali ya zame jikinshi da nata Dan kar Ammy ta fito a tare sukaje sukayiwa Ammy bankwana sannan suka kama hanyar gidansa a hanya MD sai mamaki yake yanda ya iya
Chapter 45 · 0% Book details