Sashe 92
A Garin Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Miqewa ta yi ta bazama zuwa dakin, zaune ta gan su, da su Hajiya Ikee da Sultana, sai Mubaraka da ke kwance kusa da Sultanan, ta na ta sauke numfashi da kyar,ji take iskar shaqa ta mata kadan, amma haka take daurewa, ko dan kar Sultana ta sake samun wata damuwar.
"Sassanun mu da hankuri bayin Allah, Allah shi jiqan Lawwali, Allah shi gahwarta masa, sannun mu da hankuri, Hajiya Sannun mu da hankuri"
Amsa mata suka yi, tare da yi mata godiya.
Su na nan zaune mutanen unguwa aka fara kawo abincin sadaka, ai kuwa kafin kace me, masu zaman makoki an miqe an fara warwason abinci, kowa na son ya samu abinda zai kai bakin salati.
Sai a sannan ne Hajiya Ikee ta tuna Sultana ma bata karya ba, ga ciki, waya ta yi wa Sultan, ta ce ya samu ya ɗan siyo ko da kayan shayi ne me yawa da bread a kawo, saboda su karya, ai ba a zauna ba abinci ba.
Nan da nan kuwa ya aika su Jameelu, aka kawo kayan shayin da bread,bayan sun debi wanda za su yi amfani da shi, ta sa aka fidda sauran.
Duk yanda ta so ta matsa wa su Sultana su ci abinci qi sukai, dole ta hakura, ta ci ta bar su.
Haka akai ta zaman makoki, har kwana bakwai, sannan Hajiya Ikee ta tafi ta bar Sultana a gidan, ita da Mubaraka sun zama kamar hanta da jini, a koda yaushe su na tare da junan su, kowacce su na kallon 'yar uwar ta a matsayin Lawwali, domin su din masoyan shi ne, ya na ji da su.
Sultana bata bar gidan ba sai da aka yi arba'in a lokacin cikin ta ya shiga wata na tara, Mubaraka ke raka ta ganin likita, Sultan ya yi hakuri iya hakuri, domin ba zai iya bijiro da maganar kai masa amarya a wannan lokacin ba, amma tabbas ya na da buqatar matar shi.
Cikin Sultana har ya haura wata tara, ta wuce EDD din ta, haihuwa shiru, kuma ciki kullum aka je ganin likita zai ce lafiya qlou take.
Yau ma sun shirya tsaf dan zuwa asibiti ganin likita, Sultana ce ta ke ta yi wa Mubaraka magana akan ta hanzarta Sultan na jiran su a qofar gida.
Cikin sauri ta qarasa sanya hijabin ta ta sake yi wa Lamishi sallama suka fita, zaune yake a motar ya sha gayun shi da wata brown din shadda da baqar hula, hasken shi ya qara fita sosai, ya yi wani irin kyau,tunda suka shiga motar Suka gaishe shi, Mubaraka ta ja baki ta tsuke, lokaci zuwa lokaci ta na satar kallon shi ta madubi.
"B love ki kalle ni kan ki tsaye, ni din naki ne, ke kadai, ba sai kin yi ta satar kallo na ba kamar wani baqon saurayi a unguwa"
Kunya ce ta kama ta sosai, ta sa hannun ta ta kare fuskar ta, ta na kallon waje.
Sultana kuwa murmushi ta yi, tunawa da nata masoyin sai ya sanya kwalla taruwa a idon ta, har suka isa bata san wainar da su Sultan ke toyawa ba a motar.
Su na zaune a asibitin Mubaraka ta hango Hansatu riqe da Ahmad sai wani mutum a gefen ta, Hansatu ta yi shar da ita kamar ba Hansatun Isah da ta sani ba, ganin Ahmad ne ya sake tabbatar mata da cewa Hansatun ce dai.
Ta gaban su za ta wuce, har sun gota su ta koma baya,
"Ahhh Ahhh Mubaraka d'iyar albarka, kwana da yawa"
"Aunty Hansatu ina kwana, ya gida, ya su Ameenatu,"
"Lahiya qalou, ya bayan rabuwaaa? Ina mutanen shiyyar mu, ya su Lamishi, ya yayan ki, ina hwata kowa lahiya"
Cike da murmushi Mubaraka ta ce,
"Kowa lahiya lau Aunty Hansatu, Yayana ne dai Allah ya yi mai rasuwa har an yi arba'in ma, waccan matar shi ta, mun ka kawo ganin likita,"
Salati Hansatu ta yi, sanan ta ja Mubaraka su ka ɗan koma gefe,
"Allahu akbar, Allah ya jiqan shi, dan Allah ki gaishe min da su Lamishi, ina nan tahe, ban sani ba, ban da labari, dan tunda na tai ban koma ba da nayi aure ne ma Asshibi ta tai, dan mu na gaisawa ta waya da ita, jehi jehi, bata sanar da ni wannan babban rashi da an kai ba, Allah shi gahwarta mai"
Mubaraka na son Hansatu, saboda mace ce mai kirki, ta ji dadin yanda ta nuna kulawar ta, kallon mutumin dake mata ta'aziyya ta yi, sannan ta ce,
"Aunty Hansatu wanga na Yayan nawa?"
"Shi na Mubaraka, shi na wanda iyaye na sun ka so na aura tun kahin Isah, Allah be nufa ba sai yanzu"
"Allah Sarki, matar mutum kabarin shi,Allah shi sanya alkhairi aunty,"
"Ameeen na gode, Ahmad mun ka kawo ganin likitan yara ba shi da lahiya, bari mu tai, sai na shigo shiyyar"
"Allah shi bi da lahiya sai kin zo din, na gode"
Shafa kan Ahmad Mubaraka ta yi, ta ce ya gaida su Ameenatu, dan ya san ta sosai, Islamiyya daya suke zuwa, ita a babban aji take, murmushi ya yi, har da daga mata hannu ya tafi, Sultana ta shiga ganin likita, Sultan ya zo ya tsaya a gefen mubaraka, da ke kallon inda su Hansatu suka bi dauke da murmushi, dan dukan kafadar ta ya yi kadan, da tashi, sannan ya ce,
"Da ace za a kawon ke yau, kema nan da wata tara ko goma za ki haifa mana baby, nan da shekara bakwai ya zama kamar wancan yaron,"
Kunya ce ta bi ta lullube Mubaraka, ta rasa ina za ta sanya kan ta, su na nan tsaye suka ga an gunguro da gado, Sultana na kai, da sauri Mubaraka da Sultan suka yi kan ta, gani suka yi ta na ta yatsina fuska, kamar za ta yi kuka.
"Me ya hwaru?"
"Daga duba ta naquda ta taso, zamu kai ta dakin haihuwa, ku je ku kawo kayan haihuwa"
Cikin sauri kuwa Mubaraka ta duqa gaban Sultana ta ce,
"Sannu Aunty Sultana, Allah shi sauke ki lahiya, Allah shi kawo miki haihuwar da sauqi, bari mu tai mu doko kayan,"
Shafa kan Sultana, Sultan ya yi, Sannan suka tafi.
A dakin haihuwa kuwa banda kiran sunan Allah ba abinda sultana ke yi, irin azabar da take ji ba ta da misali.
Cikin ikon Allah kafin Mubaraka su je su dawo, ta samu haihuwar yaron ta namiji, sambalele, dan lukuti kamar OO.
Duk ya cika dakin da kuka, Midwife din da ta karbi haihuwar sai tsokanar shi take da kiran shi ragon maza, a ido gashi kamar namiji, amma sai kuka, Sultana kuwa kuka kawai take, zuciyar ta ta shiga wani irin yanayi wanda ba shi da misali,tun Nurses na ganin kamar kukan Murna ne, har abun ya basu mamaki,
"Boyar Allah kukan ga ya yi yawa, ke da zaki godewa Allah, sai ki zanka kuka haka?"
Mubaraka ce ta leqa kan ta dakin,riqe da kayan baby, kamar yanda aka buqata, Sultana na ganin ta, ta sake bare baki da kuka, Mubaraka ta fahimci kukan me take, kawai sai ta ji hawaye ya na gudu a nata kuncin, qarasawa ta yi, ta duqa ta rungume Sultanan, ita ma rungume ta tayi da duk wani qarfin da ya rage mata, kuka sukai ta yi, kamar ranar ne Lawwali ya tafi ya bar su.
Da kyar Nurses din wajen suka raba su, cikin kuka Mubaraka ta ce,
"Ku yi hankuri dole mu yi kuka, mahaifin yaron ya rasu,tunawa da shi ne ya sa mu kokawa, da ace shi na nan da na tabbatar sai ya maku kyautar da za ku san kun karbi haihuwar matar so, na tabbatar da ya na nan da kun tabbata kun jima baku ga uban da ke son matar shi da d'an shi ba kamar shi,da za ku yi mamakin shin waya hi so a tsakanin mu ukun nan, matar shi? Dan shi? Ko qauna tai? Zuciyar shi cike take da soyayya, wadda in ya na wa mutum,sai mutum shi zaci shi kadai ya ke so,wannan dalili ne ya sa muke kuka, mun rasa wani bangare na jikin mu, kuma a yau mun samu wani bangare na jikin mu"
Wata midwife a wajen ce ta share hawayen ta ta ce,
"Allah Sarki, ku yi hankuri, Allah ba shi barin wani dan wani shi ji dad'i, Allah shi raya,"
"Ameeen"
An gyara jariri, da mahaifiyar shi, Sultan ya yi wa yaro huduba da suna Muhammad Auwal,Sultana kuwa qin bari ta yi a aje yaro nesa da ita, in ba Mubaraka ce ta dauke shi ba, kowa ya dauke shi za ta yi ta magana a miqa shi, ba kunya ba tsoron surutun mutane.
Kwanan su biyu a asibitin aka sallame ta, ta koma gidan Hajiya Ikee, nan fa Sultana ta ga gata, Mubaraka ba tare da wani tunani ba ta tattaro kayan su, ta taho gidan Hajiya Ikee, Sultan ya ji dadin hakan matuqa.
Ranar suna mutanen Tudun faila sun samu halartar sunan, an yi suna ba laifi, ba yabo ba fallasa.
Bayan Suna Lamishi ta tattara sauran kayan Mubaraka ta aiko mata da su, tare da yi mata aiken Fatan alkhairi daga wajen Jameelu, yana ta mata dariya yake bata saqon, ya ce,
"Mama 'Yabbuga ta ce dama haka ki ka so, ki koma gidan mijin ki, tunda ba su kai ki ba to gashi ke samu dama"
"Kaiiiii ya Salam, matar ga ta iya sheri wallah,"
Sultan ne da ya shiga dakin da Mubarakan ke da zama a gidan ya ce,
"Ai Jameelu na ke hwada maka harda roqo na ta yi wai na ce su Mama 'Yabbuga su maishe ta dakin ta"
"Innalillahi Yah Sultan yaushe mun kai haka da kai"
"Rannannn, ki tuna mana, rannan"
Dariya Jameelu ya dinga yi, ya na jin dadin ganin farin ciki a fuskar yayar tashi ,sallama ya musu ya koma gida, Sultan kuwa cewa ya yi,
"Tooo amarya ta, tunda yanzu kowa ya nutsu, mu ma ya kamata mu nutse cikin dausayin soyayyar mu ko? Yaushe za ki koma dakin ki? Nan dai dakin baqi na"
"Ba rana, ba dai ka yi min sheri ba?"
"Sassanun mu da hankuri bayin Allah, Allah shi jiqan Lawwali, Allah shi gahwarta masa, sannun mu da hankuri, Hajiya Sannun mu da hankuri"
Amsa mata suka yi, tare da yi mata godiya.
Su na nan zaune mutanen unguwa aka fara kawo abincin sadaka, ai kuwa kafin kace me, masu zaman makoki an miqe an fara warwason abinci, kowa na son ya samu abinda zai kai bakin salati.
Sai a sannan ne Hajiya Ikee ta tuna Sultana ma bata karya ba, ga ciki, waya ta yi wa Sultan, ta ce ya samu ya ɗan siyo ko da kayan shayi ne me yawa da bread a kawo, saboda su karya, ai ba a zauna ba abinci ba.
Nan da nan kuwa ya aika su Jameelu, aka kawo kayan shayin da bread,bayan sun debi wanda za su yi amfani da shi, ta sa aka fidda sauran.
Duk yanda ta so ta matsa wa su Sultana su ci abinci qi sukai, dole ta hakura, ta ci ta bar su.
Haka akai ta zaman makoki, har kwana bakwai, sannan Hajiya Ikee ta tafi ta bar Sultana a gidan, ita da Mubaraka sun zama kamar hanta da jini, a koda yaushe su na tare da junan su, kowacce su na kallon 'yar uwar ta a matsayin Lawwali, domin su din masoyan shi ne, ya na ji da su.
Sultana bata bar gidan ba sai da aka yi arba'in a lokacin cikin ta ya shiga wata na tara, Mubaraka ke raka ta ganin likita, Sultan ya yi hakuri iya hakuri, domin ba zai iya bijiro da maganar kai masa amarya a wannan lokacin ba, amma tabbas ya na da buqatar matar shi.
Cikin Sultana har ya haura wata tara, ta wuce EDD din ta, haihuwa shiru, kuma ciki kullum aka je ganin likita zai ce lafiya qlou take.
Yau ma sun shirya tsaf dan zuwa asibiti ganin likita, Sultana ce ta ke ta yi wa Mubaraka magana akan ta hanzarta Sultan na jiran su a qofar gida.
Cikin sauri ta qarasa sanya hijabin ta ta sake yi wa Lamishi sallama suka fita, zaune yake a motar ya sha gayun shi da wata brown din shadda da baqar hula, hasken shi ya qara fita sosai, ya yi wani irin kyau,tunda suka shiga motar Suka gaishe shi, Mubaraka ta ja baki ta tsuke, lokaci zuwa lokaci ta na satar kallon shi ta madubi.
"B love ki kalle ni kan ki tsaye, ni din naki ne, ke kadai, ba sai kin yi ta satar kallo na ba kamar wani baqon saurayi a unguwa"
Kunya ce ta kama ta sosai, ta sa hannun ta ta kare fuskar ta, ta na kallon waje.
Sultana kuwa murmushi ta yi, tunawa da nata masoyin sai ya sanya kwalla taruwa a idon ta, har suka isa bata san wainar da su Sultan ke toyawa ba a motar.
Su na zaune a asibitin Mubaraka ta hango Hansatu riqe da Ahmad sai wani mutum a gefen ta, Hansatu ta yi shar da ita kamar ba Hansatun Isah da ta sani ba, ganin Ahmad ne ya sake tabbatar mata da cewa Hansatun ce dai.
Ta gaban su za ta wuce, har sun gota su ta koma baya,
"Ahhh Ahhh Mubaraka d'iyar albarka, kwana da yawa"
"Aunty Hansatu ina kwana, ya gida, ya su Ameenatu,"
"Lahiya qalou, ya bayan rabuwaaa? Ina mutanen shiyyar mu, ya su Lamishi, ya yayan ki, ina hwata kowa lahiya"
Cike da murmushi Mubaraka ta ce,
"Kowa lahiya lau Aunty Hansatu, Yayana ne dai Allah ya yi mai rasuwa har an yi arba'in ma, waccan matar shi ta, mun ka kawo ganin likita,"
Salati Hansatu ta yi, sanan ta ja Mubaraka su ka ɗan koma gefe,
"Allahu akbar, Allah ya jiqan shi, dan Allah ki gaishe min da su Lamishi, ina nan tahe, ban sani ba, ban da labari, dan tunda na tai ban koma ba da nayi aure ne ma Asshibi ta tai, dan mu na gaisawa ta waya da ita, jehi jehi, bata sanar da ni wannan babban rashi da an kai ba, Allah shi gahwarta mai"
Mubaraka na son Hansatu, saboda mace ce mai kirki, ta ji dadin yanda ta nuna kulawar ta, kallon mutumin dake mata ta'aziyya ta yi, sannan ta ce,
"Aunty Hansatu wanga na Yayan nawa?"
"Shi na Mubaraka, shi na wanda iyaye na sun ka so na aura tun kahin Isah, Allah be nufa ba sai yanzu"
"Allah Sarki, matar mutum kabarin shi,Allah shi sanya alkhairi aunty,"
"Ameeen na gode, Ahmad mun ka kawo ganin likitan yara ba shi da lahiya, bari mu tai, sai na shigo shiyyar"
"Allah shi bi da lahiya sai kin zo din, na gode"
Shafa kan Ahmad Mubaraka ta yi, ta ce ya gaida su Ameenatu, dan ya san ta sosai, Islamiyya daya suke zuwa, ita a babban aji take, murmushi ya yi, har da daga mata hannu ya tafi, Sultana ta shiga ganin likita, Sultan ya zo ya tsaya a gefen mubaraka, da ke kallon inda su Hansatu suka bi dauke da murmushi, dan dukan kafadar ta ya yi kadan, da tashi, sannan ya ce,
"Da ace za a kawon ke yau, kema nan da wata tara ko goma za ki haifa mana baby, nan da shekara bakwai ya zama kamar wancan yaron,"
Kunya ce ta bi ta lullube Mubaraka, ta rasa ina za ta sanya kan ta, su na nan tsaye suka ga an gunguro da gado, Sultana na kai, da sauri Mubaraka da Sultan suka yi kan ta, gani suka yi ta na ta yatsina fuska, kamar za ta yi kuka.
"Me ya hwaru?"
"Daga duba ta naquda ta taso, zamu kai ta dakin haihuwa, ku je ku kawo kayan haihuwa"
Cikin sauri kuwa Mubaraka ta duqa gaban Sultana ta ce,
"Sannu Aunty Sultana, Allah shi sauke ki lahiya, Allah shi kawo miki haihuwar da sauqi, bari mu tai mu doko kayan,"
Shafa kan Sultana, Sultan ya yi, Sannan suka tafi.
A dakin haihuwa kuwa banda kiran sunan Allah ba abinda sultana ke yi, irin azabar da take ji ba ta da misali.
Cikin ikon Allah kafin Mubaraka su je su dawo, ta samu haihuwar yaron ta namiji, sambalele, dan lukuti kamar OO.
Duk ya cika dakin da kuka, Midwife din da ta karbi haihuwar sai tsokanar shi take da kiran shi ragon maza, a ido gashi kamar namiji, amma sai kuka, Sultana kuwa kuka kawai take, zuciyar ta ta shiga wani irin yanayi wanda ba shi da misali,tun Nurses na ganin kamar kukan Murna ne, har abun ya basu mamaki,
"Boyar Allah kukan ga ya yi yawa, ke da zaki godewa Allah, sai ki zanka kuka haka?"
Mubaraka ce ta leqa kan ta dakin,riqe da kayan baby, kamar yanda aka buqata, Sultana na ganin ta, ta sake bare baki da kuka, Mubaraka ta fahimci kukan me take, kawai sai ta ji hawaye ya na gudu a nata kuncin, qarasawa ta yi, ta duqa ta rungume Sultanan, ita ma rungume ta tayi da duk wani qarfin da ya rage mata, kuka sukai ta yi, kamar ranar ne Lawwali ya tafi ya bar su.
Da kyar Nurses din wajen suka raba su, cikin kuka Mubaraka ta ce,
"Ku yi hankuri dole mu yi kuka, mahaifin yaron ya rasu,tunawa da shi ne ya sa mu kokawa, da ace shi na nan da na tabbatar sai ya maku kyautar da za ku san kun karbi haihuwar matar so, na tabbatar da ya na nan da kun tabbata kun jima baku ga uban da ke son matar shi da d'an shi ba kamar shi,da za ku yi mamakin shin waya hi so a tsakanin mu ukun nan, matar shi? Dan shi? Ko qauna tai? Zuciyar shi cike take da soyayya, wadda in ya na wa mutum,sai mutum shi zaci shi kadai ya ke so,wannan dalili ne ya sa muke kuka, mun rasa wani bangare na jikin mu, kuma a yau mun samu wani bangare na jikin mu"
Wata midwife a wajen ce ta share hawayen ta ta ce,
"Allah Sarki, ku yi hankuri, Allah ba shi barin wani dan wani shi ji dad'i, Allah shi raya,"
"Ameeen"
An gyara jariri, da mahaifiyar shi, Sultan ya yi wa yaro huduba da suna Muhammad Auwal,Sultana kuwa qin bari ta yi a aje yaro nesa da ita, in ba Mubaraka ce ta dauke shi ba, kowa ya dauke shi za ta yi ta magana a miqa shi, ba kunya ba tsoron surutun mutane.
Kwanan su biyu a asibitin aka sallame ta, ta koma gidan Hajiya Ikee, nan fa Sultana ta ga gata, Mubaraka ba tare da wani tunani ba ta tattaro kayan su, ta taho gidan Hajiya Ikee, Sultan ya ji dadin hakan matuqa.
Ranar suna mutanen Tudun faila sun samu halartar sunan, an yi suna ba laifi, ba yabo ba fallasa.
Bayan Suna Lamishi ta tattara sauran kayan Mubaraka ta aiko mata da su, tare da yi mata aiken Fatan alkhairi daga wajen Jameelu, yana ta mata dariya yake bata saqon, ya ce,
"Mama 'Yabbuga ta ce dama haka ki ka so, ki koma gidan mijin ki, tunda ba su kai ki ba to gashi ke samu dama"
"Kaiiiii ya Salam, matar ga ta iya sheri wallah,"
Sultan ne da ya shiga dakin da Mubarakan ke da zama a gidan ya ce,
"Ai Jameelu na ke hwada maka harda roqo na ta yi wai na ce su Mama 'Yabbuga su maishe ta dakin ta"
"Innalillahi Yah Sultan yaushe mun kai haka da kai"
"Rannannn, ki tuna mana, rannan"
Dariya Jameelu ya dinga yi, ya na jin dadin ganin farin ciki a fuskar yayar tashi ,sallama ya musu ya koma gida, Sultan kuwa cewa ya yi,
"Tooo amarya ta, tunda yanzu kowa ya nutsu, mu ma ya kamata mu nutse cikin dausayin soyayyar mu ko? Yaushe za ki koma dakin ki? Nan dai dakin baqi na"
"Ba rana, ba dai ka yi min sheri ba?"