Sashe 23
A Garin Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
'Yan mata ne guda uku suka shiga kowaccen su sanye take da kaya kamar mai shirin fita yaqi,a cikin matan da ke wajen, su aka bawa horon fita da mazan in za a je cikin gari sato mutane ko wani fada ko wata hatsaniya dai.
Daya daga cikin su sai rawar jiki take, hankalin ta a tashe, lokaci zuwa lokaci ta na daga kai ta kalli No 1, da alama ta na neman agaji ne a wajen shi, shi kuwa kauda kai ya yi kamar bai taba ganin ta ba.
Su na qarasa shiga Lawwali ya yi ido hudu da budurwar da ke rawar jiki, ya ce,
"Yaseerah kin bata wayon ki, shin kin manta million nawa Excellency ya ce mu karba wajen mutenen ga? Kudi na hwa masu yawa, me ya sa zaki zagaya ki aikata haka?"
"Oga.... Dama...."
Cikin sauri No 1 ya kalle ta, ya ce,
"Oga butulci ne irin na mata, bai kamata a barta ba, ya kamata a hukunta ta saboda ya zama izina ga na baya"
Kafin Lawwali ya bada umarni, ko ya yi magana, No 1 ya harbi Yaseerah, qarar bindigar da qarar ta kusan a tare suka karade wajen, gaba daya kallo kan No 1 ya koma, shi kuma ya fara wani murmushin jin dadi ya ce,
"Oga a min afuwa, irin haka ba za ta qara faruwa ba, zan sa ido sosai, ba a koma samun maci amana wajen ga na yi ma alqawari"
"Wa ya ba ka izinin yin halbi?"
"Oga a min afuwa, na zaci za ka yi hwarin ciki na kawar da maci amana, duk da ina son Yaseerah ba zan taba bari ta ci amanar mu ba,"
Yanda ya yi maganar ya sa Lawwali zaton ko No 1 na jin haushin cin amanar da Yaseerah ta yi ne, shi ya sa ya harbe ta.
Umarni ya bada akan a ɗauke ta, a binne ta a daren, sannan ya miqe kamar zai tafi ya saita Tsohon Gwamna ya saki kunamar bindigar a qirjin shi, sannan ya fice, No 2 na biye da shi a baya,
"Oga ka sani fa dangin shi ba su aiko kudin nan ba, sun ce su na nan suna haɗawa ne, yanzu da aka kashe shi ya za a yi?"
"Ko sun kawo, ko basu kawo ba dama ba komawa wajen su zai yi ba,"
Motar shi ya fada, sannan ya wurga ma No2 bindigar shi, ya ja motar shi ya bar wajen.
Ko da ya isa gida wanka ya yi, ya nemi abinci ya ci, ya kwanta, nan da nan bacci mai dadi ya dauke shi.
***********************
Sultana ta kasa rintsawa, tunanin fuskar Lawwali ta hana ta sukuni, duk wani motsi da za ta yi ganin shi take, har a yanayin ma da bai taba zuwa mata ba, fuskar shi ta ke gani daf da ta ta in ta rufe ido, da ta bude se ta ga kamar da gaske shi ne a tsaye .
Miqewa ta yi ta shiga bayi, ta daura alwala, ta tada sallah, raka'a biyu ta yi, ta hau addu'a.
"Ya Allah ina roqon ka, dan kyawawan sunayen ka tsarkaka, ya rabbi, ka tausaya min a cikin halin da zuciya ta ke ciki, ban san me ne ne hakan ba, Allah ka bayyanar min da ma'anar abinda nake ji,ya Allah ka sanya ya zama alkhairi ne, Allah ka kawar da sharrin abinda ke cikin rai na"
Salatin Annabi ta yi, daga qarshe ta miqe, ta nade carpet din sallah ta kwanta, addu'ar bacci ta yi, ta shafe jikin ta, sannan ta kwanta da bangaren hannun ta na dama bakin ta dauke da tasbihi.
Lumshe ido ta fara yi, cikin ikon Allah kuwa bacci mai dadi ya dauke ta.
(Wannan shi ne amfanin addu'a, ka roki Allah mai duka, sannan ka yi imani, da yaqin cewa Allah ya ji, kuma ya amsa, lokaci kawai kk jira komai ya daidaita. Ba wai ka yi addu'a ba kuma ka ci gaba da damuwa, ya zama da kai da wanda bai yi addu'a ba baku da maraba)
***********************
Washe gari da safe mutanen Tsohon gwamna suka aika da 300m cash, suka aika Zuby ta karba, No 2 da No 3 na can nesa sun yi ready ko da an zo da 'yan sanda, Zuby kuwa sanye take da hijabi da niqabi, ta yanda ba mai iya gane ko ita wace ce, ta na karba motar su No 2 mai baqin gilashi ta tsaya a gaban ta, ta fada suka wuce a guje suka tada qura.
Dan Tsohon Gwamna da qanin Tsohon gwamna na ganin an wuce ba a fiddo masu da shi ba suka bi motar da gudu su na ihun kiran su, motar tini ta bace kamar walqiya, yaron durqusawa ya yi ya fashe da matsanancin kuka, baffan shi ne ya dafa shi shima idanun shi na zubar da hawaye, kusan wata daya kenan rabon su da yayan na shi,suna cikin wanan mummunan halin wayar Qanin Gwamnan tai qara ya duba kiran.
Hannu na rawa ya dauka, cike da jimami da tsoro,
"Ka duba bayan dutsen nan za ku ga dan uwan ku"
Ai be gama jin me za a ce ba ya yar da wayar ya kwasa da gudu bayan dutsen, gawar tsohon gwamna ce ta masa maraba, salati ya saka da qarfi y fadi a wajen, da gudu dan gidan tsohon gwamna ya isa dan tare shi amma inaa, kafin ya isa ya fadi qasa, gawar mahaifin shi da ya gani cikin jini ta kidimar da shi, ihu kawai ya fara, ya na kiran a taimaka musu, ga shi wajen daji ne ba mutane, in ya diba a guje dama, sai ya koma hagu da gudu, da kyar y samu natsuwa ta zo masa ya yi inda suka aje motar su, domin sun hana su shiga da mota, a guje ya ke keta dajin har ya isa wajen motar su, kunnawa ya yi ya koma wajen gawar da baffan shi, ya ɗebe su ya mayar motar sai gida.
Ranar wannan ahali sun shiga cikin matsanancin tashin hankali, masu kuka nayi, masu suma na yi, masu addu'a na yi, masu ihu da kururuwa na yi, nan da nan kuwa labari ya baza garin Zamfara da kewaye ,mutane sun shiga tashin hankali da firgici, Indai manyan qasa ba su tsira ba su kuma gama gari fa?
Direct gidan Lawwali suka nufa da qatuwar jakar kudin, ya shirya tsaf dan tafiya gidan gwamna Halliru, sai qamshi ya ke bugawa, zuciyar shi fess kamar ba abinda ya aikata mummuna, fatan shi ya cimma burin shi na sace zuciyar baiwar Allah Sultana.
Bugun gate din gidan sukai ta yi, shi kuma ya na tsaki da ihun fadin
"Wane na ya ka son balle min gambu?"(wane ne ke son karyan qofa)
"Oga"
Shi ne kawai abinda suka fadi, ya gane su waye, ya na bude qofa suka miqa masa jakar suka koma motar su suka wuce, shi kuma a motar shi ya saka jakar ya bude gate ya shiga mota, bayan ya fidda motar ne ya rufe gidan ya nufi gidan Gwamna Halliru.
Ko da ya isa time din 7:12am ne, ya sanar da gwamna zuwan shi, ya na isa ya tarar da gate bude, motar shi ya shigar ya aje ta a parking lot, ya bude ya dauki jakar, ya zaga ta baya, dakin da suke zama su tattauna mugayen abubuwan su, shi da gwamna, da sauran miyagun mutanen da suke harkokin banza tare.
Sultana ta yi mamakin ganin Lawwali da sassafe haka kuma ya zaga ta baya inda mahaifin su ne kaɗai ke zuwa da baqin shi,gashi dauke da qatuwar jaka, to ko gidan aka ce ya dawo da zama ne? Wataqila ya dawo gidan da zama ne.
Murmushi ta yi mai kyau, dan jin dadin hakan, tare da fatan Allah ya sa hasashen ta ya zama gaskiya.
Ta na mamakin yanda yanzu ta koyi leqe ta window, hakan ba halin ta bane, a baya ba ta tuna sanda ta taɓa bude labule ta kalli qasa ba, amma a yanzu kullum sai ta kalli qasa, musamman kafin ta fita, da kuma in sun dawo.
Fitowa ta yi daga wanka, daure da towel, ta shirya, cikin kwalliyar da ta fi ta jiya daukan hankali, ta sauka qasa, a gurguje ta ci abinci, sannan ta fita, tsaye ta gan shi jikin mota ya na waya, ya na ganin ta ya kashe wayar ya bude mata mota, idanun shi akan ta, bakin shi dauke da murmushi, Itan ma haka, tsayawa ya yi kafin ya rufe qofar su na kallon juna
"Shin ki na sane ki ke kwalliyar ga dan ki gusar da hankali na ga jiki na ko kuma ki na sane ki ke satar zuciya ta ba tare da jin tsoron zan rasa ta ba gaba daya?"
Cike da jin kunya Sultana ta kauda kai ta na jizar lips din ta na qasa, bai tsaya jiran amsar ta ba dama, Ita kuwa a zaton ta ya na nan tsaye ya na jiran ta amsa masa, sai kawai ji ta yi mota ta fara tafiya,kallon shi ta yi ta madubi, su na hada ido kuwa ya kashe mata ido daya, tare da d'aga gira daya, kunya ce ta kama ta sosai sai da ta rufe fuskar ta da tafukan hannun ta.
Sallama suka yi da mai gadi, mai gadi na gaishe da sultana ba ta ji ba ma, har suka hau kan babban titi ba ta dawo normal ba, tabbas ta gama yarda a yau ta kamu da matsanancin son Lawwali, ita da take kwalliya dan ta ja ra'ayin shi, shi ya ja ra'ayin ta da kallon shi da kalaman shi.
Har suka isa ba su sake magana da juna ba, sai da ya je bude mata mota zata fita ne ya ce,
"Ran sarauniyar kyawawan matan Africa gaba daya shi dade, ina neman izinin ki zanna, gida wajen qauna ta,"
"Dan Allah Auwal ka dena sani jin kunyar ka,...and zaka iya zuwa, in ka je ka ce ina gaishe ta, ina gaishe da....(shiru ta yi, dan ta na jin nauyin ce wa Lamishi kuma a gaban shi, daga baya ta ce,) ina gaishe da Umman Mubaraka"
Daya daga cikin su sai rawar jiki take, hankalin ta a tashe, lokaci zuwa lokaci ta na daga kai ta kalli No 1, da alama ta na neman agaji ne a wajen shi, shi kuwa kauda kai ya yi kamar bai taba ganin ta ba.
Su na qarasa shiga Lawwali ya yi ido hudu da budurwar da ke rawar jiki, ya ce,
"Yaseerah kin bata wayon ki, shin kin manta million nawa Excellency ya ce mu karba wajen mutenen ga? Kudi na hwa masu yawa, me ya sa zaki zagaya ki aikata haka?"
"Oga.... Dama...."
Cikin sauri No 1 ya kalle ta, ya ce,
"Oga butulci ne irin na mata, bai kamata a barta ba, ya kamata a hukunta ta saboda ya zama izina ga na baya"
Kafin Lawwali ya bada umarni, ko ya yi magana, No 1 ya harbi Yaseerah, qarar bindigar da qarar ta kusan a tare suka karade wajen, gaba daya kallo kan No 1 ya koma, shi kuma ya fara wani murmushin jin dadi ya ce,
"Oga a min afuwa, irin haka ba za ta qara faruwa ba, zan sa ido sosai, ba a koma samun maci amana wajen ga na yi ma alqawari"
"Wa ya ba ka izinin yin halbi?"
"Oga a min afuwa, na zaci za ka yi hwarin ciki na kawar da maci amana, duk da ina son Yaseerah ba zan taba bari ta ci amanar mu ba,"
Yanda ya yi maganar ya sa Lawwali zaton ko No 1 na jin haushin cin amanar da Yaseerah ta yi ne, shi ya sa ya harbe ta.
Umarni ya bada akan a ɗauke ta, a binne ta a daren, sannan ya miqe kamar zai tafi ya saita Tsohon Gwamna ya saki kunamar bindigar a qirjin shi, sannan ya fice, No 2 na biye da shi a baya,
"Oga ka sani fa dangin shi ba su aiko kudin nan ba, sun ce su na nan suna haɗawa ne, yanzu da aka kashe shi ya za a yi?"
"Ko sun kawo, ko basu kawo ba dama ba komawa wajen su zai yi ba,"
Motar shi ya fada, sannan ya wurga ma No2 bindigar shi, ya ja motar shi ya bar wajen.
Ko da ya isa gida wanka ya yi, ya nemi abinci ya ci, ya kwanta, nan da nan bacci mai dadi ya dauke shi.
***********************
Sultana ta kasa rintsawa, tunanin fuskar Lawwali ta hana ta sukuni, duk wani motsi da za ta yi ganin shi take, har a yanayin ma da bai taba zuwa mata ba, fuskar shi ta ke gani daf da ta ta in ta rufe ido, da ta bude se ta ga kamar da gaske shi ne a tsaye .
Miqewa ta yi ta shiga bayi, ta daura alwala, ta tada sallah, raka'a biyu ta yi, ta hau addu'a.
"Ya Allah ina roqon ka, dan kyawawan sunayen ka tsarkaka, ya rabbi, ka tausaya min a cikin halin da zuciya ta ke ciki, ban san me ne ne hakan ba, Allah ka bayyanar min da ma'anar abinda nake ji,ya Allah ka sanya ya zama alkhairi ne, Allah ka kawar da sharrin abinda ke cikin rai na"
Salatin Annabi ta yi, daga qarshe ta miqe, ta nade carpet din sallah ta kwanta, addu'ar bacci ta yi, ta shafe jikin ta, sannan ta kwanta da bangaren hannun ta na dama bakin ta dauke da tasbihi.
Lumshe ido ta fara yi, cikin ikon Allah kuwa bacci mai dadi ya dauke ta.
(Wannan shi ne amfanin addu'a, ka roki Allah mai duka, sannan ka yi imani, da yaqin cewa Allah ya ji, kuma ya amsa, lokaci kawai kk jira komai ya daidaita. Ba wai ka yi addu'a ba kuma ka ci gaba da damuwa, ya zama da kai da wanda bai yi addu'a ba baku da maraba)
***********************
Washe gari da safe mutanen Tsohon gwamna suka aika da 300m cash, suka aika Zuby ta karba, No 2 da No 3 na can nesa sun yi ready ko da an zo da 'yan sanda, Zuby kuwa sanye take da hijabi da niqabi, ta yanda ba mai iya gane ko ita wace ce, ta na karba motar su No 2 mai baqin gilashi ta tsaya a gaban ta, ta fada suka wuce a guje suka tada qura.
Dan Tsohon Gwamna da qanin Tsohon gwamna na ganin an wuce ba a fiddo masu da shi ba suka bi motar da gudu su na ihun kiran su, motar tini ta bace kamar walqiya, yaron durqusawa ya yi ya fashe da matsanancin kuka, baffan shi ne ya dafa shi shima idanun shi na zubar da hawaye, kusan wata daya kenan rabon su da yayan na shi,suna cikin wanan mummunan halin wayar Qanin Gwamnan tai qara ya duba kiran.
Hannu na rawa ya dauka, cike da jimami da tsoro,
"Ka duba bayan dutsen nan za ku ga dan uwan ku"
Ai be gama jin me za a ce ba ya yar da wayar ya kwasa da gudu bayan dutsen, gawar tsohon gwamna ce ta masa maraba, salati ya saka da qarfi y fadi a wajen, da gudu dan gidan tsohon gwamna ya isa dan tare shi amma inaa, kafin ya isa ya fadi qasa, gawar mahaifin shi da ya gani cikin jini ta kidimar da shi, ihu kawai ya fara, ya na kiran a taimaka musu, ga shi wajen daji ne ba mutane, in ya diba a guje dama, sai ya koma hagu da gudu, da kyar y samu natsuwa ta zo masa ya yi inda suka aje motar su, domin sun hana su shiga da mota, a guje ya ke keta dajin har ya isa wajen motar su, kunnawa ya yi ya koma wajen gawar da baffan shi, ya ɗebe su ya mayar motar sai gida.
Ranar wannan ahali sun shiga cikin matsanancin tashin hankali, masu kuka nayi, masu suma na yi, masu addu'a na yi, masu ihu da kururuwa na yi, nan da nan kuwa labari ya baza garin Zamfara da kewaye ,mutane sun shiga tashin hankali da firgici, Indai manyan qasa ba su tsira ba su kuma gama gari fa?
Direct gidan Lawwali suka nufa da qatuwar jakar kudin, ya shirya tsaf dan tafiya gidan gwamna Halliru, sai qamshi ya ke bugawa, zuciyar shi fess kamar ba abinda ya aikata mummuna, fatan shi ya cimma burin shi na sace zuciyar baiwar Allah Sultana.
Bugun gate din gidan sukai ta yi, shi kuma ya na tsaki da ihun fadin
"Wane na ya ka son balle min gambu?"(wane ne ke son karyan qofa)
"Oga"
Shi ne kawai abinda suka fadi, ya gane su waye, ya na bude qofa suka miqa masa jakar suka koma motar su suka wuce, shi kuma a motar shi ya saka jakar ya bude gate ya shiga mota, bayan ya fidda motar ne ya rufe gidan ya nufi gidan Gwamna Halliru.
Ko da ya isa time din 7:12am ne, ya sanar da gwamna zuwan shi, ya na isa ya tarar da gate bude, motar shi ya shigar ya aje ta a parking lot, ya bude ya dauki jakar, ya zaga ta baya, dakin da suke zama su tattauna mugayen abubuwan su, shi da gwamna, da sauran miyagun mutanen da suke harkokin banza tare.
Sultana ta yi mamakin ganin Lawwali da sassafe haka kuma ya zaga ta baya inda mahaifin su ne kaɗai ke zuwa da baqin shi,gashi dauke da qatuwar jaka, to ko gidan aka ce ya dawo da zama ne? Wataqila ya dawo gidan da zama ne.
Murmushi ta yi mai kyau, dan jin dadin hakan, tare da fatan Allah ya sa hasashen ta ya zama gaskiya.
Ta na mamakin yanda yanzu ta koyi leqe ta window, hakan ba halin ta bane, a baya ba ta tuna sanda ta taɓa bude labule ta kalli qasa ba, amma a yanzu kullum sai ta kalli qasa, musamman kafin ta fita, da kuma in sun dawo.
Fitowa ta yi daga wanka, daure da towel, ta shirya, cikin kwalliyar da ta fi ta jiya daukan hankali, ta sauka qasa, a gurguje ta ci abinci, sannan ta fita, tsaye ta gan shi jikin mota ya na waya, ya na ganin ta ya kashe wayar ya bude mata mota, idanun shi akan ta, bakin shi dauke da murmushi, Itan ma haka, tsayawa ya yi kafin ya rufe qofar su na kallon juna
"Shin ki na sane ki ke kwalliyar ga dan ki gusar da hankali na ga jiki na ko kuma ki na sane ki ke satar zuciya ta ba tare da jin tsoron zan rasa ta ba gaba daya?"
Cike da jin kunya Sultana ta kauda kai ta na jizar lips din ta na qasa, bai tsaya jiran amsar ta ba dama, Ita kuwa a zaton ta ya na nan tsaye ya na jiran ta amsa masa, sai kawai ji ta yi mota ta fara tafiya,kallon shi ta yi ta madubi, su na hada ido kuwa ya kashe mata ido daya, tare da d'aga gira daya, kunya ce ta kama ta sosai sai da ta rufe fuskar ta da tafukan hannun ta.
Sallama suka yi da mai gadi, mai gadi na gaishe da sultana ba ta ji ba ma, har suka hau kan babban titi ba ta dawo normal ba, tabbas ta gama yarda a yau ta kamu da matsanancin son Lawwali, ita da take kwalliya dan ta ja ra'ayin shi, shi ya ja ra'ayin ta da kallon shi da kalaman shi.
Har suka isa ba su sake magana da juna ba, sai da ya je bude mata mota zata fita ne ya ce,
"Ran sarauniyar kyawawan matan Africa gaba daya shi dade, ina neman izinin ki zanna, gida wajen qauna ta,"
"Dan Allah Auwal ka dena sani jin kunyar ka,...and zaka iya zuwa, in ka je ka ce ina gaishe ta, ina gaishe da....(shiru ta yi, dan ta na jin nauyin ce wa Lamishi kuma a gaban shi, daga baya ta ce,) ina gaishe da Umman Mubaraka"