Sashe 28
A Garin Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yar dariya suka yi a tare, Lawwali ya shagala da kallon ta suka ji an rangada salati, da sauri sultana ta miqe ta na zare ido, cikin in ina ta hau yi wa Hajiya Ikee Barka da zuwa, wani mugun kallo take bin Lawwali da shi, daga sama har qasa, babban abinda zai ba mai karatu mamaki shi ne, Lawwali dai ba a talauce ya je ba, kayan jikin shi kawai sun tasamma dubu dari,ga tsarabar daya kawo ma Sultana ya kashe 50k, wayar hannun shi abar kallo ce, ga motar shi can a waje, ko wani dan attajirin sai haka, amma Hajiya Ikee ke masa maqasqancin kallo,
"Ran ki shi dade Barka da War haka,"
Cikin tsawa ta ce
"Dakata min diyan tallaka! Me ya kawo ka har parlourn manyan baqi? Ke Sultana wacce wanga diyan tallakan ya shigo min har nan?"
Cikin kame kame da tura baki Sultana ta ce,
"Hajiya ke san hwa mai tsaron lahiya ta shike, Daddy ne yacce duk inda ni aje qawahu na shi sa na shi, tau yau na ce masa ban zuwa ko ina ban da lahiya, shi ne yazo diba ni, in baki yarda ba ki tambayi daddy shi ne yacce duk inda niyyi shi ma shi yi"
"Akan wanne dalili za a hada ki da wanga gola golan qato? Tau ban yarda ba, ke da gani nai ke san shi na shan wani abu, kuma...."
Cikin jin kunyar kalaman Hajiya Ikee Sultana ta katse ta, dan cin fuska ba shi da dad'i ,tsabar kunyar Lawwali Sultana ta kasa kallon shi.
Lawwali kuwa kawai ayyana irin azabar da zai ganawa Hajiya Ikee yake a duk ranar da tsautsayi ya had'a su, a fuskar shi kuwa murmushi ne bayyane, wanda ba me gane ma'anar shi in ba yaran shi ba, da ace a daji ne yake wannan murmushin to fa tabbas sai ya kai harbi, kad'a kai ya yi, ya ajiye ma Sultana tsarabar ta a gaban ta da kyau da kyau,ya kalle ta ya ga yanda take jin kunyar hada ido da shi, qoqari ya yi suka kalli juna, kashe mata ido daya ya yi, ta kuwa sanya murmushi, tare da rufe fuska, Hajiya Ikee salati ta saki, ta na tafa hannaye, Lawwali kuwa wucewa ya yi tare da fadin,
"Na bar ku Lahiya, Ran ki shi dade "
Ya na fita Hajiya Ikee ta ja Sultana, ta na masifa, tare da fadin, dole a sauya mata driver, bari Daddyn ta ya dawo, kuka kawai Sultana take, ta na bada hakuri, amma haka Hajiya Ikee ta murje idon ta, ta ce sai an sauya mata Lawwali.
************************
Da asuba Mai unguwa ya fita Masallaci, an yi sallah, aka hadu da mutanen unguwa aka sauke qur'ani, aka roqi Allah, akan Allah ya kawo qarshen wannan tashin hankulan da ake ta yi, sannan aka roqi Allah akan ya bayyana Isyaka, Mai Unguwa fadi yake, ya na kumawa,
"Ya Allah ko gawar shi ne Allah ka gwadi mana, mu san ya mutu ne, ya Allah ka bayyana muna da shi lahiya"
Bayan kammala addu'a kowa na tafiya gida ne, wasu da basu samu zuwa har gida jajanta masa ba, suka jajanta masa a nan.
Sai da gari ya dan fara wayewa ya yi sallama da mutane ya dau hanyar gida, a hanya ya gamu da wani daga cikin yaran shi ya na ta gudu, ya na haki, tare da murna, ya na hango baban nasu yaci burki a gaban shi, ya ce,
"Baba ! Baba !! an ga Isyaka, ga shi can gida, kwance jikin Baabaa"
"Alhamdu lilLAAH, Hamdan katheeran, Allah na gode maka,"
'Dan dandamalin wani gida ya hau a gefen hanyar, ya yi sujjadar godiya ga Allah, sannan suka kama hanya, suka nufi gida.
Ko da suka je, ga Isyaka nan, ya yi fururu, kayan shi duqun duqun, jikin shi alamar ya ci duka ya gaji.
Ya na ganin Mahaifin nasu kawai sai ya fashe da kuka, a da kuwa ko kukan ma ya kasa.
Mai Unguwa ma kukan ya fara yi, ya na sake godewa Allah tare da fadin,
"Ba abinda ya fi qarfin Allah, duk abinda Allah ya yi daidai ne, Allah mun gode maka, Allah ka qarawa Annabi daraja da wasila da fadhila, Allah mun gode maka, d'an baba, ya aka yi?"
Ya na cikin kukan ya saki murmushi, hawaye na zuba.
Kishiyar Baabaar Isyaka ce ta zo, ta ce,
"Tau ga ruwan wanka can na sauke taso ki je ki wanke shi ya ji dad'in jiki shi"
Godiya Baabaar Isyaka ta mata, ta kinkime shi ko nauyin shi bata ji,su ka nufi bayi, riga ta fara cire masa, ta fara qoqarin cire masa wando, ihu ya sanya, ya na fizge fizge, kamar mai jinnu, tare da fadin
"Ba na sooo, kar ka taba ni, ba na sooo wayyooo Allah na da zahi, zahi nika ji wallah, wayyoooo a taimaka min...."
Kuka sosai Baabaar shi ke yi, ta fita da gudu, zata kira taimako, ta tadda Mai unguwa da kishiyar ta da wasu daga yaran gidan a bakin qofar bayin, da kyar a ka samu ta nutsu, ta yi bayani, dakko shi akai waje, aka cire wandon, juya bayan shi Mai unguwa ya yi, wani wari ya ji ya na fita daga bayan yaron nashi, su na daga shi aka duba sosai, an fafake ma yaro baya, jini da wani ruwa mai danqo danqo ke zuba, ga wari, ihu da kururwar mata da yaran gidan ne ya cika ko ina na gidan, Mai unguwa kuwa suman tsaye ya yi, hawaye na bin kuncin shi, zuciyar shi ta yi mugun qunci, ta yi baqiqqirin,
"Wa ya yi maka wannan mummunan al'amari Isyaka? Wa ye ya bata maka rayuwa Isyaka? Wa ye ya zalunce mu? Ya aikata abinda Allah da Manzon shi ya yi hani da shi, ya tsine wa masu yi, da wanda aka musu, Allah ya na fushi da masu wannan mummunar dabi'ar da ko dabbobi ba sa aikata wannan alfashar,wa ye ya ci amanar mu? Waye shi ? Waye ya ci amanar mu?"
Babban dan Mai unguwa ne ya kama Isyaka daga hannun mahaifin nasu, ya aje saman tabarma, sannan ya ja hannun baban nasu suka koma gefe, ya zaunar da shi saman kujerar shi ta tsakar gida, ya na jin ya zauna, ya dafe goshin shi, ya fashe da wani irin kuka, mai ciwo.
Gaba daya gidan ya rikice, da sassafiyar har maqota sun ji koke koken sun shigo, kafin ka ce kwabo, labari ya baza unguwa.
Wasu da ke a social media kuwa har sun fara yadawa, tare da ɗaukan hoton Isyaka ba da izinin iyayen shi ba, ba da sanin shi ba.
Gani suka yi kukan ba zai kai su ba, uwar gidan Mai unguwa ce ta dauke shi, ta na kuka ya na kuka, ta wanke shi tass, ya suma ya kai sau uku kan a gama, saboda ciwon da ke jikin shi.
Ranar ahalin Mai unguwa ba mai maganar karyawar safe ma balle na rana, kowa hankalin shi a tashe yake, bayan sun gama shirya yaron, Liman ya yi sallama da Mai Unguwa.
Ko da ya je, suka gaisa ya jajanta abinda matan shi suka je suka bashi labari, sai ya bada shawara akai yaro asibiti, sannan a kai ma yan sanda rahoto.
Haka kuwa akayi ,a police station an yi ma Isyaka tambayar duniya bai san su waye suka dauke shi ba, bai ma san sanda aka dauke shi ba,sannan aka maida shi, (sharrin asiri,wasu masu aikata hakan su na sihiri,domin in b asihiri ba ba yanda za a yi wasu abubuwan su faru, se kuma son zuciya da rashin tsoron Allah, Allah ya ma na tsari da mugun ji mugun gani, mugun aiki)
Ba yanda suka iya, daga qarshe dai aka ce za a yi bincike, wanda zai wahala ayi din,cases irin wannan sun fi dari a wajen yan sandan,ba kan shi farau ba,an dad'e ana yi ba a bi ma mutane haqqin su, domin wasu masu bin haqqin ma suke kwace haqqin, asibitin aka wuce da shi, nan ma sai da aka sha fama kafin a samu bashi gado.
**********************
Lawwali na fita daga gidan su Sultana unguwar iyayen shi ya nufa, domin yanda ran shi ke tafasa da kalaman Hajiya Ikee, in bai dora sanyin idaniyar shi a idon shi ba ba zai ji salama ba, bai san me zai iya aikatawa ba.
Ko da ya isa gida kuwa, ya yi sallama Mai buruji da Kameelu ne suka amsa shi, Kameelu ya tafi da sauri ya na ma yayan nasu sannu da zuwa, ya ga ba walwala a tattare dashi, nan take ya ce,
"Yah Lawwali Mubaraka kuwa bata nan, tun da ta tafi makarantar boko bata dawo ba, wataqila ta wuce islamiyya daga can"
Idanun shi ne suka kada suka yi jawur, cikin d'aga murya yace,
"Miii ! Mi ka ce? Ina ta tai? Yanzu hwa mangariba ake kira, ina ta tsaya?"
Lamishi ce ta fito daga dakin ta, ta tsartar da yawu, ta na saka takalmi ta na daura zani ta ce,
"Ina ko ta tafi banda gantali, na ce kar ta tai makarantar wahalar ga amma sai da tassa qafa ta hita, in ma sace ta ank....."
Wani duka Lawwali ya kai wa randar da ke tsakiyar gidan, sai da ta tarwatse, ruwan cikin ta ya baje a wajen, ba Mai Buruji ba da ta riga ta fara tsorata da yanayin da ya shigo da shi ba, hatta ita 'yar taurin wato Lamishi sai da ta shiga taitayin ta, kameelu kuwa a guje ya bar gidan, cikin hargowa ya kalli Lamishi yace,
"Ina raga maki ne saboda Baraka na, duk wani abu ya same ta, sai na yi ajalin ki"
Yanayin yanda ya yi maganar ya kad'awa Lamishi hanji, a rayuwar ta kafff yau ce rana ta farko da ta ji tsoron d'an nata, ashe kyale ta yake saboda Mubaraka na hana shi, Dan Talo da ya so shiga gidan dan ganin motar Lawwali ne, ya ji ana tashin hankalin nan, ya koma cikin sanda ba tare da kowa ya ga shigar shi ba, balle fitar shi.
"Ran ki shi dade Barka da War haka,"
Cikin tsawa ta ce
"Dakata min diyan tallaka! Me ya kawo ka har parlourn manyan baqi? Ke Sultana wacce wanga diyan tallakan ya shigo min har nan?"
Cikin kame kame da tura baki Sultana ta ce,
"Hajiya ke san hwa mai tsaron lahiya ta shike, Daddy ne yacce duk inda ni aje qawahu na shi sa na shi, tau yau na ce masa ban zuwa ko ina ban da lahiya, shi ne yazo diba ni, in baki yarda ba ki tambayi daddy shi ne yacce duk inda niyyi shi ma shi yi"
"Akan wanne dalili za a hada ki da wanga gola golan qato? Tau ban yarda ba, ke da gani nai ke san shi na shan wani abu, kuma...."
Cikin jin kunyar kalaman Hajiya Ikee Sultana ta katse ta, dan cin fuska ba shi da dad'i ,tsabar kunyar Lawwali Sultana ta kasa kallon shi.
Lawwali kuwa kawai ayyana irin azabar da zai ganawa Hajiya Ikee yake a duk ranar da tsautsayi ya had'a su, a fuskar shi kuwa murmushi ne bayyane, wanda ba me gane ma'anar shi in ba yaran shi ba, da ace a daji ne yake wannan murmushin to fa tabbas sai ya kai harbi, kad'a kai ya yi, ya ajiye ma Sultana tsarabar ta a gaban ta da kyau da kyau,ya kalle ta ya ga yanda take jin kunyar hada ido da shi, qoqari ya yi suka kalli juna, kashe mata ido daya ya yi, ta kuwa sanya murmushi, tare da rufe fuska, Hajiya Ikee salati ta saki, ta na tafa hannaye, Lawwali kuwa wucewa ya yi tare da fadin,
"Na bar ku Lahiya, Ran ki shi dade "
Ya na fita Hajiya Ikee ta ja Sultana, ta na masifa, tare da fadin, dole a sauya mata driver, bari Daddyn ta ya dawo, kuka kawai Sultana take, ta na bada hakuri, amma haka Hajiya Ikee ta murje idon ta, ta ce sai an sauya mata Lawwali.
************************
Da asuba Mai unguwa ya fita Masallaci, an yi sallah, aka hadu da mutanen unguwa aka sauke qur'ani, aka roqi Allah, akan Allah ya kawo qarshen wannan tashin hankulan da ake ta yi, sannan aka roqi Allah akan ya bayyana Isyaka, Mai Unguwa fadi yake, ya na kumawa,
"Ya Allah ko gawar shi ne Allah ka gwadi mana, mu san ya mutu ne, ya Allah ka bayyana muna da shi lahiya"
Bayan kammala addu'a kowa na tafiya gida ne, wasu da basu samu zuwa har gida jajanta masa ba, suka jajanta masa a nan.
Sai da gari ya dan fara wayewa ya yi sallama da mutane ya dau hanyar gida, a hanya ya gamu da wani daga cikin yaran shi ya na ta gudu, ya na haki, tare da murna, ya na hango baban nasu yaci burki a gaban shi, ya ce,
"Baba ! Baba !! an ga Isyaka, ga shi can gida, kwance jikin Baabaa"
"Alhamdu lilLAAH, Hamdan katheeran, Allah na gode maka,"
'Dan dandamalin wani gida ya hau a gefen hanyar, ya yi sujjadar godiya ga Allah, sannan suka kama hanya, suka nufi gida.
Ko da suka je, ga Isyaka nan, ya yi fururu, kayan shi duqun duqun, jikin shi alamar ya ci duka ya gaji.
Ya na ganin Mahaifin nasu kawai sai ya fashe da kuka, a da kuwa ko kukan ma ya kasa.
Mai Unguwa ma kukan ya fara yi, ya na sake godewa Allah tare da fadin,
"Ba abinda ya fi qarfin Allah, duk abinda Allah ya yi daidai ne, Allah mun gode maka, Allah ka qarawa Annabi daraja da wasila da fadhila, Allah mun gode maka, d'an baba, ya aka yi?"
Ya na cikin kukan ya saki murmushi, hawaye na zuba.
Kishiyar Baabaar Isyaka ce ta zo, ta ce,
"Tau ga ruwan wanka can na sauke taso ki je ki wanke shi ya ji dad'in jiki shi"
Godiya Baabaar Isyaka ta mata, ta kinkime shi ko nauyin shi bata ji,su ka nufi bayi, riga ta fara cire masa, ta fara qoqarin cire masa wando, ihu ya sanya, ya na fizge fizge, kamar mai jinnu, tare da fadin
"Ba na sooo, kar ka taba ni, ba na sooo wayyooo Allah na da zahi, zahi nika ji wallah, wayyoooo a taimaka min...."
Kuka sosai Baabaar shi ke yi, ta fita da gudu, zata kira taimako, ta tadda Mai unguwa da kishiyar ta da wasu daga yaran gidan a bakin qofar bayin, da kyar a ka samu ta nutsu, ta yi bayani, dakko shi akai waje, aka cire wandon, juya bayan shi Mai unguwa ya yi, wani wari ya ji ya na fita daga bayan yaron nashi, su na daga shi aka duba sosai, an fafake ma yaro baya, jini da wani ruwa mai danqo danqo ke zuba, ga wari, ihu da kururwar mata da yaran gidan ne ya cika ko ina na gidan, Mai unguwa kuwa suman tsaye ya yi, hawaye na bin kuncin shi, zuciyar shi ta yi mugun qunci, ta yi baqiqqirin,
"Wa ya yi maka wannan mummunan al'amari Isyaka? Wa ye ya bata maka rayuwa Isyaka? Wa ye ya zalunce mu? Ya aikata abinda Allah da Manzon shi ya yi hani da shi, ya tsine wa masu yi, da wanda aka musu, Allah ya na fushi da masu wannan mummunar dabi'ar da ko dabbobi ba sa aikata wannan alfashar,wa ye ya ci amanar mu? Waye shi ? Waye ya ci amanar mu?"
Babban dan Mai unguwa ne ya kama Isyaka daga hannun mahaifin nasu, ya aje saman tabarma, sannan ya ja hannun baban nasu suka koma gefe, ya zaunar da shi saman kujerar shi ta tsakar gida, ya na jin ya zauna, ya dafe goshin shi, ya fashe da wani irin kuka, mai ciwo.
Gaba daya gidan ya rikice, da sassafiyar har maqota sun ji koke koken sun shigo, kafin ka ce kwabo, labari ya baza unguwa.
Wasu da ke a social media kuwa har sun fara yadawa, tare da ɗaukan hoton Isyaka ba da izinin iyayen shi ba, ba da sanin shi ba.
Gani suka yi kukan ba zai kai su ba, uwar gidan Mai unguwa ce ta dauke shi, ta na kuka ya na kuka, ta wanke shi tass, ya suma ya kai sau uku kan a gama, saboda ciwon da ke jikin shi.
Ranar ahalin Mai unguwa ba mai maganar karyawar safe ma balle na rana, kowa hankalin shi a tashe yake, bayan sun gama shirya yaron, Liman ya yi sallama da Mai Unguwa.
Ko da ya je, suka gaisa ya jajanta abinda matan shi suka je suka bashi labari, sai ya bada shawara akai yaro asibiti, sannan a kai ma yan sanda rahoto.
Haka kuwa akayi ,a police station an yi ma Isyaka tambayar duniya bai san su waye suka dauke shi ba, bai ma san sanda aka dauke shi ba,sannan aka maida shi, (sharrin asiri,wasu masu aikata hakan su na sihiri,domin in b asihiri ba ba yanda za a yi wasu abubuwan su faru, se kuma son zuciya da rashin tsoron Allah, Allah ya ma na tsari da mugun ji mugun gani, mugun aiki)
Ba yanda suka iya, daga qarshe dai aka ce za a yi bincike, wanda zai wahala ayi din,cases irin wannan sun fi dari a wajen yan sandan,ba kan shi farau ba,an dad'e ana yi ba a bi ma mutane haqqin su, domin wasu masu bin haqqin ma suke kwace haqqin, asibitin aka wuce da shi, nan ma sai da aka sha fama kafin a samu bashi gado.
**********************
Lawwali na fita daga gidan su Sultana unguwar iyayen shi ya nufa, domin yanda ran shi ke tafasa da kalaman Hajiya Ikee, in bai dora sanyin idaniyar shi a idon shi ba ba zai ji salama ba, bai san me zai iya aikatawa ba.
Ko da ya isa gida kuwa, ya yi sallama Mai buruji da Kameelu ne suka amsa shi, Kameelu ya tafi da sauri ya na ma yayan nasu sannu da zuwa, ya ga ba walwala a tattare dashi, nan take ya ce,
"Yah Lawwali Mubaraka kuwa bata nan, tun da ta tafi makarantar boko bata dawo ba, wataqila ta wuce islamiyya daga can"
Idanun shi ne suka kada suka yi jawur, cikin d'aga murya yace,
"Miii ! Mi ka ce? Ina ta tai? Yanzu hwa mangariba ake kira, ina ta tsaya?"
Lamishi ce ta fito daga dakin ta, ta tsartar da yawu, ta na saka takalmi ta na daura zani ta ce,
"Ina ko ta tafi banda gantali, na ce kar ta tai makarantar wahalar ga amma sai da tassa qafa ta hita, in ma sace ta ank....."
Wani duka Lawwali ya kai wa randar da ke tsakiyar gidan, sai da ta tarwatse, ruwan cikin ta ya baje a wajen, ba Mai Buruji ba da ta riga ta fara tsorata da yanayin da ya shigo da shi ba, hatta ita 'yar taurin wato Lamishi sai da ta shiga taitayin ta, kameelu kuwa a guje ya bar gidan, cikin hargowa ya kalli Lamishi yace,
"Ina raga maki ne saboda Baraka na, duk wani abu ya same ta, sai na yi ajalin ki"
Yanayin yanda ya yi maganar ya kad'awa Lamishi hanji, a rayuwar ta kafff yau ce rana ta farko da ta ji tsoron d'an nata, ashe kyale ta yake saboda Mubaraka na hana shi, Dan Talo da ya so shiga gidan dan ganin motar Lawwali ne, ya ji ana tashin hankalin nan, ya koma cikin sanda ba tare da kowa ya ga shigar shi ba, balle fitar shi.