Sashe 4
A Garin Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ɗaukan wankin ta yi a ka ta yi shago, ta auni wake, dan ya fi arha, kuma in ta dafa za su jima suna shan ruwa in an ci, ta sai man ja ta sai maggi, ta sai omo da sabulu, sanan ta yi gida.
A hanyar ta ta komawa gida, ta ga dandalin su Lamishi suna nan suna hira, kafin ta qarasa ta ji Lamishi na basu labari taimakon da ta mata, ran ta ya baci, amma ba yanda ta iya, wanda ya ajiye ta shi ya ja mata komai, ta na yin kusa da su sukai shiru, kamar ba su ke magana ba.
Gidan ta ta shige, ta ɗora tukunya ta wanke wake ta jiqa tokar murhu kadan ta zuba dan ya dahu da wuri, itacen ba yawa, fatan ta Allah ya sa ya dahu da wuri, ba dan yaran sun kusan dawowa ba da jiqa waken zata fara, ta rage asarar ice.
Bokiti ta dauka ta je ta roqi Yabbuga akan za ta debi ruwa a rijiyar gidan ta, cikin daure fuska ta ce ta je ta diba, godiya ta yi, ta shiga ta dinga jidar ruwa, qirjin ta na matsanancin ciwo, amma ba yanda za ta yi, dole hakuri za ta yi, ta nemawa yaran ta abin da za su ci.
Ta na fitowa daga gidan Yabbuga ta ji ta na fadin.
"Kuuu ban baku labari ba, kun kuwa san an yi baquwa a shiyyar ga tamu? Humm in kun gane(in kun ganta) ta baqa awab-baqar talle (kamar baqar tukunyar miya) , mijin ta ko kyakkyawa, nicce wanga mi yaggani da ya kwaso mace hakan ga awak-kuddi (kamar kudin shi basu cika ba) nai basu cika ba"
Dariya suka sanya da shewa , suka tafa,
"Yabbuga idon duniya, ta wanne bangare gidan yake gobe in su Lamishi sun taso aiki mu tai ganin gida ?"
"Can bayan gidan su Lamishin ne ai, sai kun ga gidan , wayyooo aljannar duniya kenan, gidan da nika mahwalkin samu Allah yabbatar, babu komi, su ci anan, mu ci a can"
"Ke haba na gane gidan, gidan nan me dan banzan kyau, ashe an tare"
"Shi hwa ni ka batu"
Lamishi na qoqarin magana Yabbuga ta jiyo qarar machine din Dan Jumma, da wata iriyar alkafura ta hantsila ta fada gidan ta, dariya suka fara yi, suna fadin ,
"Shegiyar za ta yi tsiya kenan,duk ka ga Yabbuga ta shiga gida bata son Dan Jumma ya gan ta nan, to akwai tsiya"
"Ina yini Dan Jumma ?"
Cikin daure fuska ya amsa ya shige, bai jira jin me za su fada ba, cikin qunar rai, dan ya san dole Yabbuga ma na wajen, sai dai guduwa ta yi da ta ji shi.
Sallama ya rangada, tare da jingine machine din shi, ya cire yar ledar da ke jikin hannun machine din, ya taka zuwa bakin qofar dakin nasu, kwance take abun ta, ta na jin shi ya na sallama ta qi amsawa.
Murmushi ya Yi, dan kuwa ya san halin kayan shi, ajiye ledar ya yi, ya zauna tare da bude kwanon abincin da ke gaban shi, shinkafar ce dai da miya, kullum abincin kenan, in an sauya kuwa to tuwo ne, in ya kawo taliya ko wani kalar abincin sai ta dafe lokaci daya ta raba wa qawaye ta nuna masu itama ana cin dadi gidan ta, ba wai dan ta samu lada ba.
Budewa ya yi ya fara ci bayan ya yi Bismillah,
"Au ka na gani ina hushi ba za ka kula Ni ba ko? Tauu ya yi, ci abincin ka ka qoshi da kyau, ya yi" ta juya baya ta na zumbura baki, ita a dole fushi take.
Dan Jumma bai kula ta ba, sai da ya ci abincin shi sanan ya tattara hankalin shi zuwa gare ta......
A GARIN MU
WRITTEN BY HAERMEEBRAERH
PAGE 5:
"Ina sauraron ki sarauniyar mata, mi am-matsalar ki yau Kuma?"
"Auuu ni ce matsalar ma ko? Tau ya yi"
"Kin dai san ba haka nika nuhi ba ko? Ina so na San damuwar ki, da har zan sallama ki qi amsa min ki na musulma"
"Suhwa nika so"(super na ke so.. Atampa)
"Me ne ne haka nan? (Me ne ne hakan)"
"Atanhwa suhwa nika so," (atampa super nake so)
"Ai ko aiki ya gane ki wallah, ni da nike qaramin ma'aikacin da rabo na da albashi yau wata biyu, haka d'ai sai ni kama sai maki wata super Dan dai ban da hankali ko? To mi za mu ci in kin Sanya super?"
Kuka Yabbuga ta saka, har da Kiran ta shiga uku, tsiyar auren talaka kenan, bata rai Dan Jumma ya yi sosai ya kalle ta,
"Ni ki ke kira da talaka yau Kuma Yabbuga? Lallai mace akwai ta da mance alkhairi, ke manta sanda nike da walwala, ke mance sanda nike da azziqin da kk Shan gatan da ba bu ya ke a cikin tsarar ki? Ke fa ba qaramar yarinya bace, karki manta bara waccan anka kai Kareema d'aki, yanzu haka ciki gare ta, kin kusa kai wa ga jika, shi na ki ke Wagga baqar tabi'a"
"Ni ke baqar d'abi'a ko kai? Yanzu ace yar super ga ba ka iya sai min? Shin ta Ina ka bi ka shigo gidan ga? Ba ka ga su Lamishi a waje bane?ko ba ka ga irin tuwahin da ke jikin su ba ne? Nan Nan Isa da yaggane su sai da ya tsaya ya yabe su, ni matar ka Kuma maqotan shi kallo ban ishe shi ba"
Wani irin zabura Dan Jumma ya yi, tare da kallon Yabbuga a yanayi na tashin hankali.
"Mi na na ki ka ce, Isa ya gane ku bai yaba tuwahin ki ba ,shi ka banna maki rayuwa hakan ga?(Isa ya gan ku be yaba kayan ki ba shi ke bata maki rai?) Ashe dama Isa ki ka aure ba Dan Jumma ba? To ki tai Isa shi sai maki super Yabbuga na Yi masallaci"
"Walle ba ka Isa ka juyan magana ka tafi ba, ka San ba haka nika nuhi ba, super ko sai ka siye ta gidan ga, kahin ka ga hwari na,"
"Irin wanga halin da ki ke shi Kareema ta koya, daga yin aure mijin ta ya kawo qara ya hi sau bakwai, kwanaki ba koro ta ya yi ba da ya gaji da bani bani da sai min? Da girman ki amma ki na wanga mummunan hali, ba lehin ki na ba, lehi na na, da a baya niyyi zamanin sai maki duk wani abu da aka yayi, maimakon yanzu da Banda shi ki hakura ki San na kyautata maki a baya, shi na kk hango na sama da ke, se ki fada min, da su Lamishin Basu aiki gidan Gwauna Ina na zasu samu kwancen tsohuwar super ma balle sabuwa? Sannan da ki ke gasa da Lamishi, ai Lamishi ta ciri tuta tunda ta iya zama da kishiya, me ya sa baki gasa da ita ta nan ba? Gashi can su na zaune lahiya kamar Yaya da qauna"
"Babbar batasin Nan, ni ka ke kalla ka yi min batun kishiya Dan Jumma? Ashe ka daina so na? Ka San ya akai Suka hwara zaman lahiyar ne ? Ai na dole ne, tunda Mai Buruji ta hwara rashin nasihwa(rashin mutunci) , ta ga bata diban komai jikin Lamishi, shi na aka zauna lahiya, Kuma indai batun suhwa ne Dan Jumma yassa ka min batun kishiya riqe suhwar ka, banni so, amma ka sani kai da ka samu kwaciyar hankali gidan ga sai na huce haushi na"
"Ga leda nan na shigo maki da ita, huce haushin ki saman ta"
Alwala ya fita waje ya yi, ya wuce masallaci, qofar gidan ba kowa dik su Lamishi sun tafi,bayan sun gama jin drama da akai a gidan, ko a gida ma labarin da sukai ta yi kenan.
Hansatu kuwa bayan ta gama dafa wake,ta soya man ba ko albasa, ta zuba ita da yaran, ta aje ma Isa na shi, da ruwan sha, a shimfidar shi da yake zama, a tare Suka ci da yaran ta, suka qoshi, kowa ya Sha ruwa, cikin hamdala, sai annashuwa da murna suke, ga wani Nan ta Dan rage da safe ta zafafa (dumama) musu su ci.
Ta na idar da sallah ta hau wankin Lamishi, bata tashi ba sai da ta gama shi tsaf.
Ta shanya, lokaci ne na iska, bata kwanta ba sai da ta ninke su ninkin guga ta daure ta ajiye, qarfe Sha d'aya saura, hamma ta ke ta dokawa, ta gaji matuqa, ga shi har wannn lokacin qirjin ta bai daina ciwo ba, ya dai rage ne kawai.
Dan kishingid'a ta yi a tsakiyar yaran ta da ke kwance a parlour , Nan da Nan kuwa bacci Mai dadi ya share ta.
Bata sani ba, shin ta jima ta na baccin ko kuwa? Kawai dai taji an take qafar ta ne, har sau biyu, tsabar mugunta, ba zai durqusa ya tashe ta ba, sai dai ya take qafar ta.
Da sauri ta janye qafar tare da miqewa ta na masa sannu da zuwa.
Amsawa ya yi ciki ciki, ya qaqalo murmushin dole, Wanda ya Sanya gaban Hansatu faduwa da qarfi, Dan ta San ma'anar shi, taba wuyan ta tayi, ta ji shi zafi rau, ta San ba komai ya ja ba sai aikin da ta Sha, ga ciwon qirji na damun ta, gashi ta yi aiki cikin iskar da ke kadawa me sanyi.
Kwallar ta ta mayar, ta raka shi waje tare da zuba masa ruwa ya wanke hannu, kamar wani qaramin yaro, abinci ya ci, ya qoshi, tare da zabga wata gyatsa me Dan banzan wari.
Kauda kai Hansatu ta Yi, Isa kuwa ko a jikin shi, ya na tashi ta tattare komai, sannan ta je ta wanke bakin ta da ruwa da dan gishiri, ta bi shi daki, (ita ta iya ta wanke bakin ta, saboda Kar a ji warin shi, Amma shi ya wuni zubur da baki bawanki, sannan ya ci abinci, ko kurkurewa bai ba, ya tafi ya kwanta a haka)
A hanyar ta ta komawa gida, ta ga dandalin su Lamishi suna nan suna hira, kafin ta qarasa ta ji Lamishi na basu labari taimakon da ta mata, ran ta ya baci, amma ba yanda ta iya, wanda ya ajiye ta shi ya ja mata komai, ta na yin kusa da su sukai shiru, kamar ba su ke magana ba.
Gidan ta ta shige, ta ɗora tukunya ta wanke wake ta jiqa tokar murhu kadan ta zuba dan ya dahu da wuri, itacen ba yawa, fatan ta Allah ya sa ya dahu da wuri, ba dan yaran sun kusan dawowa ba da jiqa waken zata fara, ta rage asarar ice.
Bokiti ta dauka ta je ta roqi Yabbuga akan za ta debi ruwa a rijiyar gidan ta, cikin daure fuska ta ce ta je ta diba, godiya ta yi, ta shiga ta dinga jidar ruwa, qirjin ta na matsanancin ciwo, amma ba yanda za ta yi, dole hakuri za ta yi, ta nemawa yaran ta abin da za su ci.
Ta na fitowa daga gidan Yabbuga ta ji ta na fadin.
"Kuuu ban baku labari ba, kun kuwa san an yi baquwa a shiyyar ga tamu? Humm in kun gane(in kun ganta) ta baqa awab-baqar talle (kamar baqar tukunyar miya) , mijin ta ko kyakkyawa, nicce wanga mi yaggani da ya kwaso mace hakan ga awak-kuddi (kamar kudin shi basu cika ba) nai basu cika ba"
Dariya suka sanya da shewa , suka tafa,
"Yabbuga idon duniya, ta wanne bangare gidan yake gobe in su Lamishi sun taso aiki mu tai ganin gida ?"
"Can bayan gidan su Lamishin ne ai, sai kun ga gidan , wayyooo aljannar duniya kenan, gidan da nika mahwalkin samu Allah yabbatar, babu komi, su ci anan, mu ci a can"
"Ke haba na gane gidan, gidan nan me dan banzan kyau, ashe an tare"
"Shi hwa ni ka batu"
Lamishi na qoqarin magana Yabbuga ta jiyo qarar machine din Dan Jumma, da wata iriyar alkafura ta hantsila ta fada gidan ta, dariya suka fara yi, suna fadin ,
"Shegiyar za ta yi tsiya kenan,duk ka ga Yabbuga ta shiga gida bata son Dan Jumma ya gan ta nan, to akwai tsiya"
"Ina yini Dan Jumma ?"
Cikin daure fuska ya amsa ya shige, bai jira jin me za su fada ba, cikin qunar rai, dan ya san dole Yabbuga ma na wajen, sai dai guduwa ta yi da ta ji shi.
Sallama ya rangada, tare da jingine machine din shi, ya cire yar ledar da ke jikin hannun machine din, ya taka zuwa bakin qofar dakin nasu, kwance take abun ta, ta na jin shi ya na sallama ta qi amsawa.
Murmushi ya Yi, dan kuwa ya san halin kayan shi, ajiye ledar ya yi, ya zauna tare da bude kwanon abincin da ke gaban shi, shinkafar ce dai da miya, kullum abincin kenan, in an sauya kuwa to tuwo ne, in ya kawo taliya ko wani kalar abincin sai ta dafe lokaci daya ta raba wa qawaye ta nuna masu itama ana cin dadi gidan ta, ba wai dan ta samu lada ba.
Budewa ya yi ya fara ci bayan ya yi Bismillah,
"Au ka na gani ina hushi ba za ka kula Ni ba ko? Tauu ya yi, ci abincin ka ka qoshi da kyau, ya yi" ta juya baya ta na zumbura baki, ita a dole fushi take.
Dan Jumma bai kula ta ba, sai da ya ci abincin shi sanan ya tattara hankalin shi zuwa gare ta......
A GARIN MU
WRITTEN BY HAERMEEBRAERH
PAGE 5:
"Ina sauraron ki sarauniyar mata, mi am-matsalar ki yau Kuma?"
"Auuu ni ce matsalar ma ko? Tau ya yi"
"Kin dai san ba haka nika nuhi ba ko? Ina so na San damuwar ki, da har zan sallama ki qi amsa min ki na musulma"
"Suhwa nika so"(super na ke so.. Atampa)
"Me ne ne haka nan? (Me ne ne hakan)"
"Atanhwa suhwa nika so," (atampa super nake so)
"Ai ko aiki ya gane ki wallah, ni da nike qaramin ma'aikacin da rabo na da albashi yau wata biyu, haka d'ai sai ni kama sai maki wata super Dan dai ban da hankali ko? To mi za mu ci in kin Sanya super?"
Kuka Yabbuga ta saka, har da Kiran ta shiga uku, tsiyar auren talaka kenan, bata rai Dan Jumma ya yi sosai ya kalle ta,
"Ni ki ke kira da talaka yau Kuma Yabbuga? Lallai mace akwai ta da mance alkhairi, ke manta sanda nike da walwala, ke mance sanda nike da azziqin da kk Shan gatan da ba bu ya ke a cikin tsarar ki? Ke fa ba qaramar yarinya bace, karki manta bara waccan anka kai Kareema d'aki, yanzu haka ciki gare ta, kin kusa kai wa ga jika, shi na ki ke Wagga baqar tabi'a"
"Ni ke baqar d'abi'a ko kai? Yanzu ace yar super ga ba ka iya sai min? Shin ta Ina ka bi ka shigo gidan ga? Ba ka ga su Lamishi a waje bane?ko ba ka ga irin tuwahin da ke jikin su ba ne? Nan Nan Isa da yaggane su sai da ya tsaya ya yabe su, ni matar ka Kuma maqotan shi kallo ban ishe shi ba"
Wani irin zabura Dan Jumma ya yi, tare da kallon Yabbuga a yanayi na tashin hankali.
"Mi na na ki ka ce, Isa ya gane ku bai yaba tuwahin ki ba ,shi ka banna maki rayuwa hakan ga?(Isa ya gan ku be yaba kayan ki ba shi ke bata maki rai?) Ashe dama Isa ki ka aure ba Dan Jumma ba? To ki tai Isa shi sai maki super Yabbuga na Yi masallaci"
"Walle ba ka Isa ka juyan magana ka tafi ba, ka San ba haka nika nuhi ba, super ko sai ka siye ta gidan ga, kahin ka ga hwari na,"
"Irin wanga halin da ki ke shi Kareema ta koya, daga yin aure mijin ta ya kawo qara ya hi sau bakwai, kwanaki ba koro ta ya yi ba da ya gaji da bani bani da sai min? Da girman ki amma ki na wanga mummunan hali, ba lehin ki na ba, lehi na na, da a baya niyyi zamanin sai maki duk wani abu da aka yayi, maimakon yanzu da Banda shi ki hakura ki San na kyautata maki a baya, shi na kk hango na sama da ke, se ki fada min, da su Lamishin Basu aiki gidan Gwauna Ina na zasu samu kwancen tsohuwar super ma balle sabuwa? Sannan da ki ke gasa da Lamishi, ai Lamishi ta ciri tuta tunda ta iya zama da kishiya, me ya sa baki gasa da ita ta nan ba? Gashi can su na zaune lahiya kamar Yaya da qauna"
"Babbar batasin Nan, ni ka ke kalla ka yi min batun kishiya Dan Jumma? Ashe ka daina so na? Ka San ya akai Suka hwara zaman lahiyar ne ? Ai na dole ne, tunda Mai Buruji ta hwara rashin nasihwa(rashin mutunci) , ta ga bata diban komai jikin Lamishi, shi na aka zauna lahiya, Kuma indai batun suhwa ne Dan Jumma yassa ka min batun kishiya riqe suhwar ka, banni so, amma ka sani kai da ka samu kwaciyar hankali gidan ga sai na huce haushi na"
"Ga leda nan na shigo maki da ita, huce haushin ki saman ta"
Alwala ya fita waje ya yi, ya wuce masallaci, qofar gidan ba kowa dik su Lamishi sun tafi,bayan sun gama jin drama da akai a gidan, ko a gida ma labarin da sukai ta yi kenan.
Hansatu kuwa bayan ta gama dafa wake,ta soya man ba ko albasa, ta zuba ita da yaran, ta aje ma Isa na shi, da ruwan sha, a shimfidar shi da yake zama, a tare Suka ci da yaran ta, suka qoshi, kowa ya Sha ruwa, cikin hamdala, sai annashuwa da murna suke, ga wani Nan ta Dan rage da safe ta zafafa (dumama) musu su ci.
Ta na idar da sallah ta hau wankin Lamishi, bata tashi ba sai da ta gama shi tsaf.
Ta shanya, lokaci ne na iska, bata kwanta ba sai da ta ninke su ninkin guga ta daure ta ajiye, qarfe Sha d'aya saura, hamma ta ke ta dokawa, ta gaji matuqa, ga shi har wannn lokacin qirjin ta bai daina ciwo ba, ya dai rage ne kawai.
Dan kishingid'a ta yi a tsakiyar yaran ta da ke kwance a parlour , Nan da Nan kuwa bacci Mai dadi ya share ta.
Bata sani ba, shin ta jima ta na baccin ko kuwa? Kawai dai taji an take qafar ta ne, har sau biyu, tsabar mugunta, ba zai durqusa ya tashe ta ba, sai dai ya take qafar ta.
Da sauri ta janye qafar tare da miqewa ta na masa sannu da zuwa.
Amsawa ya yi ciki ciki, ya qaqalo murmushin dole, Wanda ya Sanya gaban Hansatu faduwa da qarfi, Dan ta San ma'anar shi, taba wuyan ta tayi, ta ji shi zafi rau, ta San ba komai ya ja ba sai aikin da ta Sha, ga ciwon qirji na damun ta, gashi ta yi aiki cikin iskar da ke kadawa me sanyi.
Kwallar ta ta mayar, ta raka shi waje tare da zuba masa ruwa ya wanke hannu, kamar wani qaramin yaro, abinci ya ci, ya qoshi, tare da zabga wata gyatsa me Dan banzan wari.
Kauda kai Hansatu ta Yi, Isa kuwa ko a jikin shi, ya na tashi ta tattare komai, sannan ta je ta wanke bakin ta da ruwa da dan gishiri, ta bi shi daki, (ita ta iya ta wanke bakin ta, saboda Kar a ji warin shi, Amma shi ya wuni zubur da baki bawanki, sannan ya ci abinci, ko kurkurewa bai ba, ya tafi ya kwanta a haka)