Sashe 88
A Garin Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Sannu, sannu uwar gulai uwar munahurci, watakam waccan qandarabushe munahikar lungun ta dena zuwa, ke kin karbe ta ko? To ki kiyaye zuwa gidan ga ki na kawo gulmar mutanen unguwa, nan nan na wuce ta qofar gidan Malam Zakari, mata na ta zuwa makarantar Allah (islamiyya), su na daukan karatun da zai amfane su duniya da lahira, ke ki na nan ki na baza gulma,to daga yau na fada Maki, in ba alheri na zai kawo ki gidan ga ba, kar ki koma zuwa"
A yau ta hango abinda Yabbuga ke tsoro a idanun Lawwali, wani irin tsoro da nauyin shi ta ji ya baibaye ta, yaqen ma kasa shi ta yi,sai nishi take fiddawa,wanda ya sanya Mai Buruji dariya, ta rasa me ya sa in Lawwali ya ritsa matan unguwar su ke shiga tashin hankali haka, cikin zuciyar ta tace,
'Na raba ki da mutane irin su Lawwali Mai Buruji, bar ganin ya shiryu, yanzu zai juye ya tuna da,ku din ma ai tsoron shi kuke'
Kama bakin ta tayi dan kar dariyar ta ta fita fili, saboda hada ido da suka yi da Ta Yahai, idanun ta sun yi qanana qanana, sai zufar kan hanci ke tsattsafo mata, munafurci be ba a rayuwa .
Lawwali bayan ya gama wanke Ta Yahai, ya gaishe da iyayen shi, ya wa Mubaraka Sallama ya tafi gidan shi.
Bayan fitar shi ne Lamishi ta juya dan yi wa Ta Yahai magana ta ga wayam, Mai Buruji da dariya ta suqe ta har ta na zama a kujera,ta ce,
"Ai ya juya ku na gaisawa ta sa kai ta hice, ke ga idanun Ta Yahai? Ita da ka wa Yabbuga dariya akan tsoron Lawwali ita ma yau ta shiga layi,"
"Ke dai Allah shi yi miki sauqi, mi ne ne abun dariya to anan?"
"Yaya ke ma hwa dariyar ki ke,ke wallah zaman gida ya hi dadi akan shegen zaman gulmar nan da mu ke, haba, mi za ai da gulma da tsintse?"
"Walle kau, ke gani dai hankali kwance ba ruwan mu da damben unguwa, walle in ba qarya zan yi ba, har wani dan fari na ga muna yi,...ke wagga ke dawo ba mu ko gaisa ba, ya su Hajiya ?"
Mubaraka da ke ta gaishe su suna hira ce ta sake gyara zaman ta a tabarma ta ce,
"Su na lahiya, yau ma Hajiya tace Aunty sultana ta shirya, in Yah Auwal yamaishe ni gidaa ya bi ya dauki mata tai, ai dai an qare zaman makoki"
"Ai ko ta kyauta wallah, Allah dai shi jiqan gwamna,"
"Ameen, shin Umma da gaske ne abinda ya faru da Aunty Hansatun Isah?"
"Humm haka dai labari ke ta yawo, yanzu haka shi Laminu an yanke mai hakuncin zaman gidan maza shi na can, Asshibi kuwa ta murje ido, ta toshe kunne da tsintsen mutanen shiyya, tunda bata san mi ya ka aikatawa ba, shi da kan shi ya wanke ta,ita ko Hansatu an ce uwatta ce ta tafi har can qasa mai tsalki ta amso mata takardar saki (kun ji yanda mutane kan juya zance komai qanqantar shi ko? Su Yaya Musa ne suka amso takardar saki, amma an ce Hajiya ce, duk yanda labari yake mutanen duniya sai sun juya shi, shi ya sa dole ne mu godewa Sahabbai da duk wadan da suka yi sanadin hade mana Alqur'ani da hadisai har suka riske mu lafiya ba dad'i ba ragi, Allah ya yarda da su, ya shirya masu qirqirar hadisan qarya, da labaran qarya)"
"Ohhhh Allah shi kyauta, amma Ni Ko Umma ba dan kar a ce na ce ba, da sai in ce na wa Aunty Hansatu murnar rabuwa da Isah, mutumin nan azzalumi na wallah, Allah shi bata mafi alkhairi"
"Ameen ke dai diyar ga"
"Umma akwai tuwo? Na yi kewar cin abincin ki"
"Akwai, bari na debo miki, Allah ya yi da rabon ki, kahin su Jameelu su tai wajen koyon dunki da Yayan ku yassa su, sai da sun ka kusan canyewa suka bar kingi"
"Masha Allah, ashe sun sara zuwa, ya fadi min kuwa zai saka su, amma ban san sun fara zuwa ba, bana dinkin mu ba zai kwantai ba ashe, Allah ya taimaka"
"Ameeen ya Allah"
Mubaraka na zaune Lamishi ta kawo mata tuwon ta kuwa zauna ta gyare shi, dan kuwa Lamishi ba dai iya girki ba.
***************************
Wata biyar kenan da kai kayan lefe, da duk wani abu da ake kai wa na bidi'ar aure,na Mubaraka, duk da cewa Lawwali ya ce a taqaita bidi'a amma still kaya sun qayatar da kowa, ranar aure kuma na ta qaratowa, dan kuwa bai fi saura sati Uku ba.
Amarya Mubaraka ta ga gata wajen Iyayen ta biyu, wato Mai Buruji, da Lamishi, sai kuma qawar amana wato Mama 'Yabbuga kamar yanda Mubaraka ke kiran ta, duk wani sabani ya kau, an shirya, an dinke, Ta Yahai ma ba a barta a baya ba, wajen hidimar biki.
Yanzu matan unguwar sun hade kan su, duk da in gulmar su 'Yabbuga ta motsa sai sun tab'a amma an samu sassauci, mutane sun fahimci abun ya zame musu kamar wani ciwo ne, (Allah ka raba mu da ciwon gulma da munafurci).
Ango kuwa na can na hidimar biki, a bangare daya kuma ya na ta zuwa neman aiki, duk da gwamnati mai ci ta ce za ta taimaka masa, a matsayin shi na dan tsohon gwamna,amma shiru ka ke ji, ba wanda ya kira shi.
Ya aika takardun shi ko ta ina dan neman aiki, kuma ya na saka ran albarkacin addu'ar da yake, da kuma tawassuli da kyawawan ayyukan da ya ke a rayuwar shi, Allah ba zai bari su wulaqanta ba, shi da mahaifiyar shi, da qanwar shi.
Cikin ikon Allah kuwa ana sauran sati biyu auren shi, ya samu aiki, aikin da bai taba zaton samu ba kuwa, nan da nan kuwa ya bugawa Hajiya Ikee waya ya sanar da ita, murna ta dinga yi da sanya albarka, suna gama waya da Hajiya ya kira Mubaraka, ya na murna ya sanar da ita, sujjada ta yi ta godewa Allah, kafin daga baya ta dau wayar ta yi ta zuba masa addu'a ta kariya daga dukkan abun qi, da nema masa alkhairi da albarkar da aikin ke tattare da shi .
*************************
Cikin Sultana na da watanni bakwai cif cif yanzu, Hajiya Ikee kan ce bata taɓa ganin wadda ciki ya yi wa kyau ba sama da Sultanan ta, Ita kuwa sultana kan ce son kai ne kawai, amma akwai wanda suka fi ta kyau.
Lawwali ya gama aika sauran 'yan kudaden shi Kano, ya na so kafin ya isa Taheer ya buda masa shago ko qarami ne,Taheer kuwa ya dage sai dai Lawwali ya amshi babban shagon shi, shi ya nemi qarami ya ci gaba da kasuwancin,tun Lawwali na ahh ahh ahh, sai da Taheer ya ja ran Oga ya kai ga ɓaci har ya bada umarni, sannan ya dena jayayya da Lawwalin.
Sun gama tsara bayan bikin Mubaraka, za su dunguma gaba daya shi da Taheer su tafi Kano din.
************************
Lawwali na matuqar bawa Sultana kulawa, kulawar da duk wani miji na gari, kuma uba na gari ya kamata ya bawa matar shi, musamman ma mai juna biyu, har Sultana na mamakin inda ya san yanda ake kula da mace mai juna.
Ta na bincike a wayar shi ta gano, internet yake shiga ya yi ta research akan yanda zai kula da ita.
Yau ma kamar kullum, ta na zaune ta ce da shi, Ita dai so take ta ci qosai, irin wanda ake saidawa a bakin hanya din nan, akwai wata mata akan hanyar shiga unguwar Tudun faila, ta na qosan to ita ta tuna, shi ne take ta rikici ita qosai take so, gashi bai jima da dawowa daga unguwar ba, ba ya so ya koma, amma haka ya hakura ya shirya, ya fita.
A bakin titin fita daga Unguwar su ne ya ga wannan tsohuwar da yanzu kusan kullum sai ya gan ta, dunqule a waje daya, da kwanon barar ta a gaban ta, matsawa ya yi da motar shi, ya aje mata 1k a kwanon ya yi gaba, ya tabbata duk yanda akai, matsafan unguwar ba irin ta suke so ba, shi ya sa har yanzu take a raye, basu sanqame ta ba.
Ko da ya je wajen mai qosai ya tarar ta kusan saidawa, qullin saura kad'an, cikin Hamdala ga Allah ya miqa kudin shi aka bashi, ya dau hanyar komawa gida.
Ko da ya bi ta inda tsohuwar take sai bai gan ta ba, shi ma qara gudun motar shi ya yi, ya isa gida.
Ko da ya je gimbiyar ta yi bacci,ya na ta tunani shin ya tashe ta neee, ko ya bar ta? Kar ya tashe ta ya yi laifi,Kuma ya karanta a internet ba a so ana tashin mai ciki, in ta yi bacci, ana barin ta har ta tashi da kanta, in ya bari kuma har qosan ya yi sanyi, ya san za ta masa rikici, dan haka yawo ya dinga yi, ya na buga abubuwa, har sai da qara ta ishe ta ta farka, nan fa ta ja qosai ta hau ci, ta na ta surutu, wanda ya riga ya san santi ne, shi kuwa ya na ta matsa mata qafar ta da ta kumbura.
(Maza hausawa a dinga tausayin masu ciki,matan hausawa a dinga gyarawa, dan ba me kama qafa duk baso da qauje da datti ya matsa, sai mai tsananin qaunar ki da tausayin ki)
************************
Makaranta kun dai san an ce rana bata qarya, sai dai uwar d'iya ta ji kunya, to na tabbata wannan uwar d'iyar ba zata ji kunya ba,domin kuwa a shirye take tsafff dan gudanar da biki bidirin autar ta wato Mubaraka......
*Kun shiryaaa??*
💅🏻 *A GARIN MU* 💅🏻
BY HAERMEEBRAERH
PAGE 64:
A yau ta hango abinda Yabbuga ke tsoro a idanun Lawwali, wani irin tsoro da nauyin shi ta ji ya baibaye ta, yaqen ma kasa shi ta yi,sai nishi take fiddawa,wanda ya sanya Mai Buruji dariya, ta rasa me ya sa in Lawwali ya ritsa matan unguwar su ke shiga tashin hankali haka, cikin zuciyar ta tace,
'Na raba ki da mutane irin su Lawwali Mai Buruji, bar ganin ya shiryu, yanzu zai juye ya tuna da,ku din ma ai tsoron shi kuke'
Kama bakin ta tayi dan kar dariyar ta ta fita fili, saboda hada ido da suka yi da Ta Yahai, idanun ta sun yi qanana qanana, sai zufar kan hanci ke tsattsafo mata, munafurci be ba a rayuwa .
Lawwali bayan ya gama wanke Ta Yahai, ya gaishe da iyayen shi, ya wa Mubaraka Sallama ya tafi gidan shi.
Bayan fitar shi ne Lamishi ta juya dan yi wa Ta Yahai magana ta ga wayam, Mai Buruji da dariya ta suqe ta har ta na zama a kujera,ta ce,
"Ai ya juya ku na gaisawa ta sa kai ta hice, ke ga idanun Ta Yahai? Ita da ka wa Yabbuga dariya akan tsoron Lawwali ita ma yau ta shiga layi,"
"Ke dai Allah shi yi miki sauqi, mi ne ne abun dariya to anan?"
"Yaya ke ma hwa dariyar ki ke,ke wallah zaman gida ya hi dadi akan shegen zaman gulmar nan da mu ke, haba, mi za ai da gulma da tsintse?"
"Walle kau, ke gani dai hankali kwance ba ruwan mu da damben unguwa, walle in ba qarya zan yi ba, har wani dan fari na ga muna yi,...ke wagga ke dawo ba mu ko gaisa ba, ya su Hajiya ?"
Mubaraka da ke ta gaishe su suna hira ce ta sake gyara zaman ta a tabarma ta ce,
"Su na lahiya, yau ma Hajiya tace Aunty sultana ta shirya, in Yah Auwal yamaishe ni gidaa ya bi ya dauki mata tai, ai dai an qare zaman makoki"
"Ai ko ta kyauta wallah, Allah dai shi jiqan gwamna,"
"Ameen, shin Umma da gaske ne abinda ya faru da Aunty Hansatun Isah?"
"Humm haka dai labari ke ta yawo, yanzu haka shi Laminu an yanke mai hakuncin zaman gidan maza shi na can, Asshibi kuwa ta murje ido, ta toshe kunne da tsintsen mutanen shiyya, tunda bata san mi ya ka aikatawa ba, shi da kan shi ya wanke ta,ita ko Hansatu an ce uwatta ce ta tafi har can qasa mai tsalki ta amso mata takardar saki (kun ji yanda mutane kan juya zance komai qanqantar shi ko? Su Yaya Musa ne suka amso takardar saki, amma an ce Hajiya ce, duk yanda labari yake mutanen duniya sai sun juya shi, shi ya sa dole ne mu godewa Sahabbai da duk wadan da suka yi sanadin hade mana Alqur'ani da hadisai har suka riske mu lafiya ba dad'i ba ragi, Allah ya yarda da su, ya shirya masu qirqirar hadisan qarya, da labaran qarya)"
"Ohhhh Allah shi kyauta, amma Ni Ko Umma ba dan kar a ce na ce ba, da sai in ce na wa Aunty Hansatu murnar rabuwa da Isah, mutumin nan azzalumi na wallah, Allah shi bata mafi alkhairi"
"Ameen ke dai diyar ga"
"Umma akwai tuwo? Na yi kewar cin abincin ki"
"Akwai, bari na debo miki, Allah ya yi da rabon ki, kahin su Jameelu su tai wajen koyon dunki da Yayan ku yassa su, sai da sun ka kusan canyewa suka bar kingi"
"Masha Allah, ashe sun sara zuwa, ya fadi min kuwa zai saka su, amma ban san sun fara zuwa ba, bana dinkin mu ba zai kwantai ba ashe, Allah ya taimaka"
"Ameeen ya Allah"
Mubaraka na zaune Lamishi ta kawo mata tuwon ta kuwa zauna ta gyare shi, dan kuwa Lamishi ba dai iya girki ba.
***************************
Wata biyar kenan da kai kayan lefe, da duk wani abu da ake kai wa na bidi'ar aure,na Mubaraka, duk da cewa Lawwali ya ce a taqaita bidi'a amma still kaya sun qayatar da kowa, ranar aure kuma na ta qaratowa, dan kuwa bai fi saura sati Uku ba.
Amarya Mubaraka ta ga gata wajen Iyayen ta biyu, wato Mai Buruji, da Lamishi, sai kuma qawar amana wato Mama 'Yabbuga kamar yanda Mubaraka ke kiran ta, duk wani sabani ya kau, an shirya, an dinke, Ta Yahai ma ba a barta a baya ba, wajen hidimar biki.
Yanzu matan unguwar sun hade kan su, duk da in gulmar su 'Yabbuga ta motsa sai sun tab'a amma an samu sassauci, mutane sun fahimci abun ya zame musu kamar wani ciwo ne, (Allah ka raba mu da ciwon gulma da munafurci).
Ango kuwa na can na hidimar biki, a bangare daya kuma ya na ta zuwa neman aiki, duk da gwamnati mai ci ta ce za ta taimaka masa, a matsayin shi na dan tsohon gwamna,amma shiru ka ke ji, ba wanda ya kira shi.
Ya aika takardun shi ko ta ina dan neman aiki, kuma ya na saka ran albarkacin addu'ar da yake, da kuma tawassuli da kyawawan ayyukan da ya ke a rayuwar shi, Allah ba zai bari su wulaqanta ba, shi da mahaifiyar shi, da qanwar shi.
Cikin ikon Allah kuwa ana sauran sati biyu auren shi, ya samu aiki, aikin da bai taba zaton samu ba kuwa, nan da nan kuwa ya bugawa Hajiya Ikee waya ya sanar da ita, murna ta dinga yi da sanya albarka, suna gama waya da Hajiya ya kira Mubaraka, ya na murna ya sanar da ita, sujjada ta yi ta godewa Allah, kafin daga baya ta dau wayar ta yi ta zuba masa addu'a ta kariya daga dukkan abun qi, da nema masa alkhairi da albarkar da aikin ke tattare da shi .
*************************
Cikin Sultana na da watanni bakwai cif cif yanzu, Hajiya Ikee kan ce bata taɓa ganin wadda ciki ya yi wa kyau ba sama da Sultanan ta, Ita kuwa sultana kan ce son kai ne kawai, amma akwai wanda suka fi ta kyau.
Lawwali ya gama aika sauran 'yan kudaden shi Kano, ya na so kafin ya isa Taheer ya buda masa shago ko qarami ne,Taheer kuwa ya dage sai dai Lawwali ya amshi babban shagon shi, shi ya nemi qarami ya ci gaba da kasuwancin,tun Lawwali na ahh ahh ahh, sai da Taheer ya ja ran Oga ya kai ga ɓaci har ya bada umarni, sannan ya dena jayayya da Lawwalin.
Sun gama tsara bayan bikin Mubaraka, za su dunguma gaba daya shi da Taheer su tafi Kano din.
************************
Lawwali na matuqar bawa Sultana kulawa, kulawar da duk wani miji na gari, kuma uba na gari ya kamata ya bawa matar shi, musamman ma mai juna biyu, har Sultana na mamakin inda ya san yanda ake kula da mace mai juna.
Ta na bincike a wayar shi ta gano, internet yake shiga ya yi ta research akan yanda zai kula da ita.
Yau ma kamar kullum, ta na zaune ta ce da shi, Ita dai so take ta ci qosai, irin wanda ake saidawa a bakin hanya din nan, akwai wata mata akan hanyar shiga unguwar Tudun faila, ta na qosan to ita ta tuna, shi ne take ta rikici ita qosai take so, gashi bai jima da dawowa daga unguwar ba, ba ya so ya koma, amma haka ya hakura ya shirya, ya fita.
A bakin titin fita daga Unguwar su ne ya ga wannan tsohuwar da yanzu kusan kullum sai ya gan ta, dunqule a waje daya, da kwanon barar ta a gaban ta, matsawa ya yi da motar shi, ya aje mata 1k a kwanon ya yi gaba, ya tabbata duk yanda akai, matsafan unguwar ba irin ta suke so ba, shi ya sa har yanzu take a raye, basu sanqame ta ba.
Ko da ya je wajen mai qosai ya tarar ta kusan saidawa, qullin saura kad'an, cikin Hamdala ga Allah ya miqa kudin shi aka bashi, ya dau hanyar komawa gida.
Ko da ya bi ta inda tsohuwar take sai bai gan ta ba, shi ma qara gudun motar shi ya yi, ya isa gida.
Ko da ya je gimbiyar ta yi bacci,ya na ta tunani shin ya tashe ta neee, ko ya bar ta? Kar ya tashe ta ya yi laifi,Kuma ya karanta a internet ba a so ana tashin mai ciki, in ta yi bacci, ana barin ta har ta tashi da kanta, in ya bari kuma har qosan ya yi sanyi, ya san za ta masa rikici, dan haka yawo ya dinga yi, ya na buga abubuwa, har sai da qara ta ishe ta ta farka, nan fa ta ja qosai ta hau ci, ta na ta surutu, wanda ya riga ya san santi ne, shi kuwa ya na ta matsa mata qafar ta da ta kumbura.
(Maza hausawa a dinga tausayin masu ciki,matan hausawa a dinga gyarawa, dan ba me kama qafa duk baso da qauje da datti ya matsa, sai mai tsananin qaunar ki da tausayin ki)
************************
Makaranta kun dai san an ce rana bata qarya, sai dai uwar d'iya ta ji kunya, to na tabbata wannan uwar d'iyar ba zata ji kunya ba,domin kuwa a shirye take tsafff dan gudanar da biki bidirin autar ta wato Mubaraka......
*Kun shiryaaa??*
💅🏻 *A GARIN MU* 💅🏻
BY HAERMEEBRAERH
PAGE 64: