Sashe 48
A Garin Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Duk jikin Lamishi ya yi laushi, bata da burin da ya wuce na ta san a wanne hali Mubaraka take yanzu, shin Lawwali gidan shi ya maida ta ? Ko itama ya tsunduma ta harkar shi?
Bata da amsar tambayar nan, gashi 'yan gulma har sun yad'a komawar Mubaraka, ana ta zuwa barka, da kuma son ganin ta, amma sai dai su yi qarya su ce ta fita da yayan ta wajen 'yan sanda, dan a ji su waye suka sace ta.
Kwana hudu mutane basu daina zuwa jaje ba, har iyayen su Murjanatu sun je, dan a tambayi Mubaraka su waye suka sace su, tunda su sun qi fadi, ko da suka je suma aka ce musu har yau Yayan ta bai maida ta ba.
Labari ya fara sauya salo, wasu na ganin ko yayan ta ya aurar da ita ne? Wasu na ganin qarya ne dama ba a gan ta ba, aka ce an gan ta,wasu na ganin tsoro ne ya sanya aka boye ta, kowa dai da abinda ya dasa a zuciyar shi, yake gani kuma shi ne daidai(haka halin dan Adam yake, sai ya sa maka maganar da ba ita ce a zuciyar ka ba a bakin shi)
Mai Buruji ta shawarci Lamishi da komawa wajen aiki, tunda dai an ga Mubaraka, yanzu zama shirun zai sa mata kadaici.
Haka kuwa aka yi, wata ranar Litinin da sassafe, suka shirya, suka dauki hanyar gidan gwamna Halliru, adaidaita na aje su, suka hango Lawwali tafe, zai je gidan shi ma.
Lamishi bata taɓa tsayawa ta masa irin wannan kallon ba, kallon uwa da d'a, kullum kallon wani abu mara daraja da amfani, take masa, da ace tun sanda ya na da halin kirki take masa kalar wannan kallon, wataqila da Allah ya tallafa mata sun zama kamar sauran yara na gari.
Ciki suka shiga suka jira zuwan shi.
Ko da ya zo yi ya yi kamar bai gan su ba, Mai Buruji ce ta ce,
"Lawwali Barka da swahiya,"
Ko kallon inda take bai ba, ya je ya jingina da motar Sultana, Lamishi kuwa bata yi fushi ba, bin shi tayi, ta hade hannayen ta ta na wasa da su, ta ce,
"Yayan Mub...."
"Kar ki sake ki ambaci sunan ta abakin ki, zan manta ba a gida muke ba na karta Maki rashin mutunci,me ki ke so? Kuddi na ki ka bida?"
Wasu hawaye ne masu dumin gaske suka zuba mata, da hanzarin ta sa hannu ta share su,
"Uhmm dama cewa na yi, ku na tare da ita ne? Na ga baka maishe ta gida ba tun sanda ka kawo ta mun ka gane ta"
"Ban yi niyyar maishe ta gidan ba, kuma ba amfanin ki san inda take, ko akwai? Ke dai san ni ba zan cutar da ita ba, ke kuma fa? Duk duniya ta shaida ke ki na iya kashe ta ma da hannun ki, tunda kin ka kashe ta da bakin ki"
Ita kan ta ta na mamakin yanda maganganun Lawwali ke qona zuciyar ta, ta ya uwa za ta kashe dan ta? Duk da ta sani bata kyauta ba matuqa, amma ba za ta iya kashe Mubaraka ba, jinin ta ce.
Murmushin mugunta Hajiya Ikee ta yi, a daidai lokacin da ta saki labulen d'akin ta, ta d'auki dan kwalin ta ta d'aure kan ta da kyau, ta fita daga d'akin ta, sauka take a matattakalar benen, cikin sauri, dan bata son Lamishi ta bar wajen, bata isa ba.
Ta na fita kuwa Lamishi na isa bakin qofar shiga cikin gidan, dan gudanar da aikin ta, Mai Buruji ma ta wuce nata aikin.
Da sauri Lamishi ta yi baya, tare da duqar da kan ta, ta hau gaishe da Hajiya Ikee, cikin tsawa da hargowa Hajiya Ikee ta bangaje Lamishi ta fadi qasa, sannan ta ce,
"Keeee! Mahaukaciya, daqiqiya, mai warin talauci, halan baki gani ne? Ko kuwa hayaqin icce ya makantar maki da ijiya? (Idanu)"
Mamaki ne mai girma a zuciyar Lamishi, ta san Hajiya Ikee bata da mutunci, amma haka bai taba shiga tsakanin su ba, duk kalar rashin mutuncin da take musu baya wuce akan aikin su, su na gyarawa ta bata, ko in Sultana na musu magana ta yi ta hantarar Sultanan ta na hana ta magana da masu aiki, amma wannan bangazar da zagin rashin mutuncin daga ina?
"Ran ki shi dade ki yi min ahuwa, ban gan ki ba"
Sai da Hajiya Ikee ta kalli inda Lawwali ke tsaye, sannan ta ce,
"Ina hwa zaki ganni ana Allah Allah a shigo AC, a yi aiki a saci abinda aka sata a tai gida, tau bari ki jiya, daga yau, duk na qara diba abu ban gani ba, sai nasa an daure min keyya, da shegiyar kishiyar can taki, da duk wani dangi naki, barauniyar banza barauniyar yohi"
Wani irin tashin hankali ne ya shiga Lamishi, a barta da rashin mutunci, da rashin ragawa kowa, gulma da munahurci,amma banda sata, sataa, ita Lamishi ake zargi da Sata? Wai me ke faruwa ne yau? Ko dan dai ta jima bata zo bane?
"Ran ki shi dad'e ki yi min ahuwa, diya ta ce ta bace, ba mu gane ta ba, sai kwanan nan, shi yasa bana zuwa, na aiko Mai Buruji ta sanar da ku,"
Sultana da ta fito ta ga Lamishi a qasa, a wulaqance, sai ta ji ran ta ya ɓaci, ko da ba mahaifiyar Auwal bace, bai kamata a yi wa mace mai shekaru haka ba,da hanzari, ta d'aga Lamishi ta na kad'e mata jiki, kallon motar ta tayi, ta ga Lawwali na tsaye ya na jiran ta, ko kallon wajen ma baya yi, alamu sun nuna kamar ma baya wajen, ballantana ya san me ake aikatawa, daidai da kwayar zarra ba bu digon baqin ciki a fuskar shi.
Ran Sultana ya baci da hakan kuwa matuqa, ya na tsaye ake wulaqanta mahaifiyar shi? Wane irin yaro ne shi? Kafin ta gama tunanin ta taji Muryar mahaifiyar ta na fadin,
"Aka neme ta anka rasa ko ta bi duniya? Zamani ne na in talauci ya wa mutum yawa shi hwara biyar samari, dan su samu kuddi"
Kusan a tare suka kalli Lawwali, kowannen su da abinda yake saqawa a cikin zuciyar shi, Hajiya Ikee ba karamin kaduwa hanjin cikin ta suka yi ba, da ganin yanayin fuskar shi, wani irin gurnani ya saki kamar wani zaki, da sauri ya zagaya ya bude mota, tare da yi wa sultana alama da su tafi.
Kamar wadda ya yi wa magani, haka ta bi umarnin shi zungui zungui ta fada mota, da wani irin gudu ya bar gidan,tsoro ne da tashin hankali a bayyane a fuskar Sultana, wannan wanne irin gudu yake da ita.
Bangaren Lamishi kuwa sai ta ji wani sanyi ya mamaye ta, ta tabbata Hajiya Ikee bata zagi banza ba, ko bai rama dan ita ba, sai ya dau mataki dan qanwar shi, qarasa miqewa ta yi ta na murmushi, ta tsaya sosai, ta na jiran Hajiya ta matsa, ta shiga ta hau aikin ta.
Hajiya Ikee kuwa, ji ta yi qirjin ta na bugawa da sauri da sauri, idanun Lawwali kawai take hangowa, tafe take zuwa daki, ba tare da ta san sanda ta fara tafiyar ba.
Tunani take mai zurfi, game da abinda ya faru, zama ta yi a bakin gado, ta na nazari, cikin murmushi ta miqe, ta ce,
"Wato duk wanda ka son ya sami nasara akan ka Lawwali, shi tabi qaunar ka, da kyau"
Hannayen ta biyu ta tafa, cikin jin dadi, tare da ganin ta samo babbar hanyar da za ta yi maganin Lawwali.
Lamishi kuwa, ko da ta shiga dakin Sultana Dan gyarawa, sai ta ga babu datti, kuma Mai Buruji ta tabbatar mata da cewar ba mai zuwa gyaran dakin ta, tun bayan batan Mubaraka, da alama da kan ta take gyarawa,duk da cewa akwai masu aiki sosai a gidan, wanki ne dai gashi nan, ta tara mai mugun yawa, sake dan gyara abinda ba a gyara ba ta yi, ta debi wankin, ta tafi wajen yin wanki.
Sai da ta gama aikin cikin gidan sannan ta tafi wajen su Mai Buruji, nan ta labartawa Mai Buruji duk abinda ya faru, dariya Mai Buruji ta dinga yi, daga qarshe ta ce,
"Aiko yau ta kai qarshen iskanci, da wulaqanta tallaka, kee Yaya watarana ma haihuwar dan iska na da rana, dan ko walle na sani Lawwali ba shi barin wanda duk ya ɓaci (zagi) qauna tai, ko da ke ta kuwa, balle wata can,"
"Bari ke dai,shi ne na ka wa dariya nima, yo Allah na tuba zagi ko ga unguwa sha nai mukai kullum, abu d'aya ya yi min ciwo da ta ce muna mata sata,na san banda halin kwarai, amma hwa bana sata bana maita,"
Haka sukai ta hira a tsakanin su, su na aikin su.
Bangaren Lawwali da Sultana kuwa, duk yanda ta so ta yi magana, ko da kalmar bada hakuri ne kuwa, ya gagara, saboda yanda Oga ya daure fuska abun ba a cewa komai, banda tafasa ba abinda zuciyar shi take yi, har shi za a zagarwa qauna? Yarinyar da yake jin ta kamar tsoka daya a miya? Duk wanda ya zage ta, ko ya taba ta, ji yake kamar ya soka mishi kibiya a idanun shi, ya na matuqar jin ciwo ya ga wani na zaluntar Mubaraka.
Hajiya Ikee da ta san tanadin da yake mata da bata taba masa qanwa ba, abinda ya wa Lamishi ya bata ran shi, domin kuwa Uwa uwa ce, amma da ya tuna shegen kwadayi da son abin duniyar su ya ja musu walaqanci,dan ba shi da tabbas akan abinda Hajiya ikee ta fadi, na suna sata, duk wani mai son abun duniya in ya samu na wani, zai iya sata,dan haka sai ya dauke kai ya dena kallon su, amma duk abinda take fada a kunnen shi, kuma tabbas ta dauki bashin da ba zata iya biya ba.
Bata da amsar tambayar nan, gashi 'yan gulma har sun yad'a komawar Mubaraka, ana ta zuwa barka, da kuma son ganin ta, amma sai dai su yi qarya su ce ta fita da yayan ta wajen 'yan sanda, dan a ji su waye suka sace ta.
Kwana hudu mutane basu daina zuwa jaje ba, har iyayen su Murjanatu sun je, dan a tambayi Mubaraka su waye suka sace su, tunda su sun qi fadi, ko da suka je suma aka ce musu har yau Yayan ta bai maida ta ba.
Labari ya fara sauya salo, wasu na ganin ko yayan ta ya aurar da ita ne? Wasu na ganin qarya ne dama ba a gan ta ba, aka ce an gan ta,wasu na ganin tsoro ne ya sanya aka boye ta, kowa dai da abinda ya dasa a zuciyar shi, yake gani kuma shi ne daidai(haka halin dan Adam yake, sai ya sa maka maganar da ba ita ce a zuciyar ka ba a bakin shi)
Mai Buruji ta shawarci Lamishi da komawa wajen aiki, tunda dai an ga Mubaraka, yanzu zama shirun zai sa mata kadaici.
Haka kuwa aka yi, wata ranar Litinin da sassafe, suka shirya, suka dauki hanyar gidan gwamna Halliru, adaidaita na aje su, suka hango Lawwali tafe, zai je gidan shi ma.
Lamishi bata taɓa tsayawa ta masa irin wannan kallon ba, kallon uwa da d'a, kullum kallon wani abu mara daraja da amfani, take masa, da ace tun sanda ya na da halin kirki take masa kalar wannan kallon, wataqila da Allah ya tallafa mata sun zama kamar sauran yara na gari.
Ciki suka shiga suka jira zuwan shi.
Ko da ya zo yi ya yi kamar bai gan su ba, Mai Buruji ce ta ce,
"Lawwali Barka da swahiya,"
Ko kallon inda take bai ba, ya je ya jingina da motar Sultana, Lamishi kuwa bata yi fushi ba, bin shi tayi, ta hade hannayen ta ta na wasa da su, ta ce,
"Yayan Mub...."
"Kar ki sake ki ambaci sunan ta abakin ki, zan manta ba a gida muke ba na karta Maki rashin mutunci,me ki ke so? Kuddi na ki ka bida?"
Wasu hawaye ne masu dumin gaske suka zuba mata, da hanzarin ta sa hannu ta share su,
"Uhmm dama cewa na yi, ku na tare da ita ne? Na ga baka maishe ta gida ba tun sanda ka kawo ta mun ka gane ta"
"Ban yi niyyar maishe ta gidan ba, kuma ba amfanin ki san inda take, ko akwai? Ke dai san ni ba zan cutar da ita ba, ke kuma fa? Duk duniya ta shaida ke ki na iya kashe ta ma da hannun ki, tunda kin ka kashe ta da bakin ki"
Ita kan ta ta na mamakin yanda maganganun Lawwali ke qona zuciyar ta, ta ya uwa za ta kashe dan ta? Duk da ta sani bata kyauta ba matuqa, amma ba za ta iya kashe Mubaraka ba, jinin ta ce.
Murmushin mugunta Hajiya Ikee ta yi, a daidai lokacin da ta saki labulen d'akin ta, ta d'auki dan kwalin ta ta d'aure kan ta da kyau, ta fita daga d'akin ta, sauka take a matattakalar benen, cikin sauri, dan bata son Lamishi ta bar wajen, bata isa ba.
Ta na fita kuwa Lamishi na isa bakin qofar shiga cikin gidan, dan gudanar da aikin ta, Mai Buruji ma ta wuce nata aikin.
Da sauri Lamishi ta yi baya, tare da duqar da kan ta, ta hau gaishe da Hajiya Ikee, cikin tsawa da hargowa Hajiya Ikee ta bangaje Lamishi ta fadi qasa, sannan ta ce,
"Keeee! Mahaukaciya, daqiqiya, mai warin talauci, halan baki gani ne? Ko kuwa hayaqin icce ya makantar maki da ijiya? (Idanu)"
Mamaki ne mai girma a zuciyar Lamishi, ta san Hajiya Ikee bata da mutunci, amma haka bai taba shiga tsakanin su ba, duk kalar rashin mutuncin da take musu baya wuce akan aikin su, su na gyarawa ta bata, ko in Sultana na musu magana ta yi ta hantarar Sultanan ta na hana ta magana da masu aiki, amma wannan bangazar da zagin rashin mutuncin daga ina?
"Ran ki shi dade ki yi min ahuwa, ban gan ki ba"
Sai da Hajiya Ikee ta kalli inda Lawwali ke tsaye, sannan ta ce,
"Ina hwa zaki ganni ana Allah Allah a shigo AC, a yi aiki a saci abinda aka sata a tai gida, tau bari ki jiya, daga yau, duk na qara diba abu ban gani ba, sai nasa an daure min keyya, da shegiyar kishiyar can taki, da duk wani dangi naki, barauniyar banza barauniyar yohi"
Wani irin tashin hankali ne ya shiga Lamishi, a barta da rashin mutunci, da rashin ragawa kowa, gulma da munahurci,amma banda sata, sataa, ita Lamishi ake zargi da Sata? Wai me ke faruwa ne yau? Ko dan dai ta jima bata zo bane?
"Ran ki shi dad'e ki yi min ahuwa, diya ta ce ta bace, ba mu gane ta ba, sai kwanan nan, shi yasa bana zuwa, na aiko Mai Buruji ta sanar da ku,"
Sultana da ta fito ta ga Lamishi a qasa, a wulaqance, sai ta ji ran ta ya ɓaci, ko da ba mahaifiyar Auwal bace, bai kamata a yi wa mace mai shekaru haka ba,da hanzari, ta d'aga Lamishi ta na kad'e mata jiki, kallon motar ta tayi, ta ga Lawwali na tsaye ya na jiran ta, ko kallon wajen ma baya yi, alamu sun nuna kamar ma baya wajen, ballantana ya san me ake aikatawa, daidai da kwayar zarra ba bu digon baqin ciki a fuskar shi.
Ran Sultana ya baci da hakan kuwa matuqa, ya na tsaye ake wulaqanta mahaifiyar shi? Wane irin yaro ne shi? Kafin ta gama tunanin ta taji Muryar mahaifiyar ta na fadin,
"Aka neme ta anka rasa ko ta bi duniya? Zamani ne na in talauci ya wa mutum yawa shi hwara biyar samari, dan su samu kuddi"
Kusan a tare suka kalli Lawwali, kowannen su da abinda yake saqawa a cikin zuciyar shi, Hajiya Ikee ba karamin kaduwa hanjin cikin ta suka yi ba, da ganin yanayin fuskar shi, wani irin gurnani ya saki kamar wani zaki, da sauri ya zagaya ya bude mota, tare da yi wa sultana alama da su tafi.
Kamar wadda ya yi wa magani, haka ta bi umarnin shi zungui zungui ta fada mota, da wani irin gudu ya bar gidan,tsoro ne da tashin hankali a bayyane a fuskar Sultana, wannan wanne irin gudu yake da ita.
Bangaren Lamishi kuwa sai ta ji wani sanyi ya mamaye ta, ta tabbata Hajiya Ikee bata zagi banza ba, ko bai rama dan ita ba, sai ya dau mataki dan qanwar shi, qarasa miqewa ta yi ta na murmushi, ta tsaya sosai, ta na jiran Hajiya ta matsa, ta shiga ta hau aikin ta.
Hajiya Ikee kuwa, ji ta yi qirjin ta na bugawa da sauri da sauri, idanun Lawwali kawai take hangowa, tafe take zuwa daki, ba tare da ta san sanda ta fara tafiyar ba.
Tunani take mai zurfi, game da abinda ya faru, zama ta yi a bakin gado, ta na nazari, cikin murmushi ta miqe, ta ce,
"Wato duk wanda ka son ya sami nasara akan ka Lawwali, shi tabi qaunar ka, da kyau"
Hannayen ta biyu ta tafa, cikin jin dadi, tare da ganin ta samo babbar hanyar da za ta yi maganin Lawwali.
Lamishi kuwa, ko da ta shiga dakin Sultana Dan gyarawa, sai ta ga babu datti, kuma Mai Buruji ta tabbatar mata da cewar ba mai zuwa gyaran dakin ta, tun bayan batan Mubaraka, da alama da kan ta take gyarawa,duk da cewa akwai masu aiki sosai a gidan, wanki ne dai gashi nan, ta tara mai mugun yawa, sake dan gyara abinda ba a gyara ba ta yi, ta debi wankin, ta tafi wajen yin wanki.
Sai da ta gama aikin cikin gidan sannan ta tafi wajen su Mai Buruji, nan ta labartawa Mai Buruji duk abinda ya faru, dariya Mai Buruji ta dinga yi, daga qarshe ta ce,
"Aiko yau ta kai qarshen iskanci, da wulaqanta tallaka, kee Yaya watarana ma haihuwar dan iska na da rana, dan ko walle na sani Lawwali ba shi barin wanda duk ya ɓaci (zagi) qauna tai, ko da ke ta kuwa, balle wata can,"
"Bari ke dai,shi ne na ka wa dariya nima, yo Allah na tuba zagi ko ga unguwa sha nai mukai kullum, abu d'aya ya yi min ciwo da ta ce muna mata sata,na san banda halin kwarai, amma hwa bana sata bana maita,"
Haka sukai ta hira a tsakanin su, su na aikin su.
Bangaren Lawwali da Sultana kuwa, duk yanda ta so ta yi magana, ko da kalmar bada hakuri ne kuwa, ya gagara, saboda yanda Oga ya daure fuska abun ba a cewa komai, banda tafasa ba abinda zuciyar shi take yi, har shi za a zagarwa qauna? Yarinyar da yake jin ta kamar tsoka daya a miya? Duk wanda ya zage ta, ko ya taba ta, ji yake kamar ya soka mishi kibiya a idanun shi, ya na matuqar jin ciwo ya ga wani na zaluntar Mubaraka.
Hajiya Ikee da ta san tanadin da yake mata da bata taba masa qanwa ba, abinda ya wa Lamishi ya bata ran shi, domin kuwa Uwa uwa ce, amma da ya tuna shegen kwadayi da son abin duniyar su ya ja musu walaqanci,dan ba shi da tabbas akan abinda Hajiya ikee ta fadi, na suna sata, duk wani mai son abun duniya in ya samu na wani, zai iya sata,dan haka sai ya dauke kai ya dena kallon su, amma duk abinda take fada a kunnen shi, kuma tabbas ta dauki bashin da ba zata iya biya ba.