Sashe 82
A Garin Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Abdullahi ne ya kalli Hansatu da sauri, a zuciyar shi ya na ayyana abubuwa da dama, babban abinda ya sani shi ne, wannan karon ba me auren ta sai shi, ba zai bari ta sake kufce masa ba.
An tsaida magana a cikin sati na sama za su tafi zuwa saudiya, Hansatu kuwa ta ce ba za ta koma unguwar su ba, unguwar gulma, dan ta san yanzu magana ta karade unguwar, za a yi ta nuna ta da baki da ido ne.
Hajiya ma cewa ta yi ta yi zaman ta, ai kuwa ita da yara nan suka samu wajen zama abun su, tun daga ranar Hansatu ta samu abokiyar hira, haka zata zauna ta yi ta bawa Hajiya labarin abubuwan da Isah ke mata, Hajiya kuwa ta ce,
"Ke ko gama zama da baqin mugu,dan neman sallamamme kawai"
****************************
Da isar su asibiti, Hajiya Ikee ta ɗora idon ta akan yaran nata, sai ta fashe da kukan murna, fess ta gan su, wanda ba haka suka zata ba gaba dayan su, wani haske da sheqi ma taga su nayi, musamman Sultana.
Bayan sun gaisa ne, ta ja su har gaban gadon da gwamna yake kai, duk ya fada ya rame,sai gulu gulun idanuwa, bakin shi ya karkace hannu da qafar shi kamar wanda Inna ta taba,asibiti sun tabbatar da cewa ba shi da wani ciwo da ya danganci asibiti a yanzu,sai qarancin jini da yake fama da shi,kullum ana qara masa jini leda biyu zuwa uku, hawan jinin da ya kama shi ma ya sauka, tun da jimawa, sun yi gwaje gwaje sun rasa dalilin da ya sa yake a shanye haka, kuma jinin shi ke yawan qarewa.
Hajiya Ikee na gama basu labarin rashin lafiyar mahaifin nasu Sultan ya ce,
"Hajiya ai da wahala Daddy ya warke,ko da zai warke din ma, domin kuwa mutane irin shi na fama da cututtukan da ake rasa gane kan su ne sakamakon Allah ya isa da mutane ke yi musu, da za a ce za a tara duk mutanen da ya zalunta, su yahe masa, na miki alqawalin sai ya miqe, amma in basu yahe masa ba, zai wahala ya tashi "
"Innalillahi, na shiga uku ni Ikilima, ina zan saka rayuwa ta? Yanzu fissbillahi haka ka ke ganin ba zai tashi ba sai mutane sun yahe masa? To mu yanzu ina mun ka san adadin wanda ya zalunta?"
"Ba lallai bane kuma, ta yu Allah shi bashi lafiya, amma fa zai karbi hukuncin da ya aikata a ranar gobe, in dai be tuba ba"
"Yau na shiga uku na lalace ni ikilima"
Kuka sosai Hajiya Ikee ke yi, shawara Sultana ta kawo, akan su maida Gwamna gida a na maganin Islamic, saboda yanzu kusan watan shi biyu a kwance, komai sai an masa, Hajiya duk ta rame,
"Ai dole gida zamu kai shi, in kunka ji kuddin da asibitin ga ke karba duk kwana guda sai tsoron Allah ya kama mutum, gwamnan da an ka mayar yanzu so guda ya taho da tawagar shi sun ka duba Daddyn ku, da 'yan jarida, akai ta hotuna da video, ko sisi basu bamu ba, amma sun ce sun basuwa kuddin jinya har ya ji sauqi, kuma ga shi asibiti kullum ni ka biyan kuddi"
"Hummm Mum kenan, a bar tone tone, mu samu yanzu a kama muna shi mu tai gida"
Bayan komawar su gida ne suka sha kallon ikon Allah, gwamna banda ihu da shure shure ba abinda yake, abun ya yi matuqar basu mamaki,Sultan ne ya ce su fitar da shi waje, ai kuwa ana fita waje ya dena ihun, sai zare ido kawai yake, da jin tsoron kar a maida shi ciki.
"Sultan mu tai gidan mu na can titin zanna, wataqilan nan ne bashi so"
"Bamu da wani gida da ya yi saura sai wanga, dan kuwa duk na bayar, anjima ma za a taho amsar makullai,nan din dai zamu koma, dole ya yi hankuri,"
"Yau na shiga uku na lalace ni Ikillma, kai wa Allah ku bamu makullin guda, wanda ka bawa wancan su amshi wanga"
"Muka san menene acikin gidan da za mu ba wa wasu shi? Mu din dai mu za mu shiga,koma menene ku ne kun ka jawo muna, dole a haka zamu shiga mu zauna da koma me ne ne a ciki"
Sultana ta kula da cewa ran Sultan ya fara ɓaci, abinda bai taba yi da iyayen su ba kenan, bayyanar da bacin ran shi irin haka, su kafe ya kafe, dan haka shiga maganar ta yi,
"Hajiya mu shiga sai a nemo mallammai masu ruqiyya su taho su taimaka muna, ko ya ka ce Yah Sultan"
Dauke kan shi ya yi, sannan ya ce,
"Ku shiga ciki, bari na shiga gari na samo malamin da zai zo a hwara tun yanzu, makullan gidan su na cikin safe din Daddy, ki bude ki basuwa in an zo amsa"
"Toh sai ka dawo"
*Ku taimakawa gwamna Halliru da malami me ruqyaaa*
💅🏻 *A GARIN MU* 💅🏻
BY HAERMEEBRAERH
PAGE 60:
Sultan ya yi yawo, iya yawo amma bai samu dacewa da malami ko guda d'aya da zai taimake su ya je ya yi wa Gwamna Halliru ruqiyya ba, wanda suka amince za su je kuma bai gamsu da kalar tasu ruqiyyar ba, dan kuwa cewa suke aljanun yanka suke so a musu su sha jini, za su rabu da shi, (da damar masu cewa su na cire aljanu da yanka, ko kuma aljani ya fadi buqatar shi a masa sanan ya fita, ba rugiyya suke ba, domin ba haka ake ruqiyya ba a sunnar Annabi Muhammad ,bai bamu umarnin yi wa aljani hidima ba, kar fa mu manta Allah ya daukaka mu sama da su, kuma cutar da mu suke saboda ba ma ganin su, amma kuma a dinga musu hidima? Ko a je wajen su neman taimako? Duk wanda yake haka ya sabawa Allah, in bai tuba ba Allah zai kama shi, ko ya azabtar da shi kamar yanda gwamna halliru ke shan wahala a hannun su, ya nemi taimakon su ba na Allah ba, su kuma a yanzu suna azabtar da shi, saboda abinda ya kasance ya na aikatawa).
Da kyar ya samu wani malami guda ɗaya da ya amince zai je ya ga Gwamnan, amma sai da yamma, bayan ya sallami d'aliban shi da ke d'aukan karatu a wajen shi.
Sultan ya koma gida a gajiye, tun daga gate ya ke jiyo kururuwa da ihun gwamnan, gidan shiru, ba wata hayaniya, dan kuwa duk ma'aikatan sun gudu, mai gadi ne guda d'aya kawai ya rage, shi ma dan bashi da wajen zuwa ne, ya sa ya ke zaune a nan din.
Da shigar Sultan gidan, Sultana ta tunkare shi, idanun ta sun yi luhu luhu, saboda kukan da ta sha ta qoshi, ganin mahaifin nasu a cikin mawuyacin halin nan ba qaramin tashin hankali bane a gare ta, ko ba komai, ya gwada masu soyayyar da bata da misali.
"Yah Sultan ya na gan ka kai d'ai? Suman Daddy uku bayan tahiyar ka, na rasa me zan masa ya samu sauqin abinda yake ji"
Kuka ta fashe da shi, saboda tsananin tausayin mahaifin nasu, sultan ne ya kama hannun ta, idanun shi sun yi jajawur, ya ce,
"Mu je ciki, ki dena kukan haka nan, kukan ki ba shi zai bashi lahiya ba,daddy addu'a shi ke buqata, mu tai a samu a kunna karatun Alkur'ani kahin mallam ya taho, dan ba yanzu ne zai taho ba, sai yamma"
Cikin ikon Allah kuwa ana kunna masa karatun Alkur'ani bacci mai dadi ya dauke shi, zama suka yi jingum jingum su na kallon shi, kowannen su da abinda yake saqawa a zuciyar shi.
Hayaniya suka jiyo sosai, daga wajen gate din gidan, a tare suka tashi suka nufi waje, Hajiya babu ko mayafi, daga ita sai leshin jikin ta da d'ankwali, Sultana kuwa tun da suka je bata cire mayafin ta ba, haka suka fita.
'Yan jarida ne sun kai su takwas a qofar gidan, sai roqon mai gadin suke ya bar su su shiga daukan rahoto.
Su na ganin iyalin gwamnan kuwa suka hau daukan su hoto, tare da qoqarin yi musu tambayoyi, tambayoyin kuwa sun matuqar sanya Sultan da Sultana jin nauyi da kunyar amsa su, tambayoyi ne wanda da suke tattare da gaskiya, amma kuma ba za su iya amsa su ba kai tsaye.
Dan haka Sultan ya musu izinin shiga,kamar jira suke, cikin turereniya da rige rige suka shige gidan.
Zama Sultan ya yi a saman kujera da ke a farfajiyar gidan, sannan ya ce,
"Tambayoyin duk da kun ka yi muna, sun nuna cewa wasu daga cikin 'yan jarida musulmai ba su san amfanin aikin jarida ba ga rayuwar su, ta duniya da lahira, domin kuwa da damar su su yad'a labarin da zai jawo su yi suna, ko su samu wata daukaka ta duniya, ko arziqi shi d'ai suke bid'a, ba labaran da za su gyara, kuma su taimaki al'umma ba,misali, yanzu kun taho ku na so ku ji mi na na ya sami tsohon Gwamna, kun taho da list din zargin da mutane ka yi akan shi, me ya sa sanda shi na kan mulki, ba ku zuwa dan taimaka masa wajen yi mishi tambayoyin da za su sa ya yi aiki dole? Ko ku na nufin ba ku da wadannan tambayoyin tun gabanin ciwon shi?
To Bari na baku amsa, amsar da na ke so ku yad'a ta a duniya kowa ya ji, da farko dai dole ne mu san cewa duk abinda ya ke faruwa gare mu a wannan qasa, da wannan yanki,na harikar kidnapping, da kashe kashen rayuka, da sace dukiyoyin al'umma, ba komai ya jawo mana ba, sai sab'awa Allah, daga mu har shugabannin mu, domin kuwa Allah ya ce,
"Wancan ne, haka abin yake, lallai Allah bai kasance yana canza wata ni’ima da ya ni’imta akan wasu mutane ba face har sai sun canza abin da yake cikin rayukansu, kuma lallai Allah mai ji ne, kuma masani.”
(Suratul Anfal: 53)
An tsaida magana a cikin sati na sama za su tafi zuwa saudiya, Hansatu kuwa ta ce ba za ta koma unguwar su ba, unguwar gulma, dan ta san yanzu magana ta karade unguwar, za a yi ta nuna ta da baki da ido ne.
Hajiya ma cewa ta yi ta yi zaman ta, ai kuwa ita da yara nan suka samu wajen zama abun su, tun daga ranar Hansatu ta samu abokiyar hira, haka zata zauna ta yi ta bawa Hajiya labarin abubuwan da Isah ke mata, Hajiya kuwa ta ce,
"Ke ko gama zama da baqin mugu,dan neman sallamamme kawai"
****************************
Da isar su asibiti, Hajiya Ikee ta ɗora idon ta akan yaran nata, sai ta fashe da kukan murna, fess ta gan su, wanda ba haka suka zata ba gaba dayan su, wani haske da sheqi ma taga su nayi, musamman Sultana.
Bayan sun gaisa ne, ta ja su har gaban gadon da gwamna yake kai, duk ya fada ya rame,sai gulu gulun idanuwa, bakin shi ya karkace hannu da qafar shi kamar wanda Inna ta taba,asibiti sun tabbatar da cewa ba shi da wani ciwo da ya danganci asibiti a yanzu,sai qarancin jini da yake fama da shi,kullum ana qara masa jini leda biyu zuwa uku, hawan jinin da ya kama shi ma ya sauka, tun da jimawa, sun yi gwaje gwaje sun rasa dalilin da ya sa yake a shanye haka, kuma jinin shi ke yawan qarewa.
Hajiya Ikee na gama basu labarin rashin lafiyar mahaifin nasu Sultan ya ce,
"Hajiya ai da wahala Daddy ya warke,ko da zai warke din ma, domin kuwa mutane irin shi na fama da cututtukan da ake rasa gane kan su ne sakamakon Allah ya isa da mutane ke yi musu, da za a ce za a tara duk mutanen da ya zalunta, su yahe masa, na miki alqawalin sai ya miqe, amma in basu yahe masa ba, zai wahala ya tashi "
"Innalillahi, na shiga uku ni Ikilima, ina zan saka rayuwa ta? Yanzu fissbillahi haka ka ke ganin ba zai tashi ba sai mutane sun yahe masa? To mu yanzu ina mun ka san adadin wanda ya zalunta?"
"Ba lallai bane kuma, ta yu Allah shi bashi lafiya, amma fa zai karbi hukuncin da ya aikata a ranar gobe, in dai be tuba ba"
"Yau na shiga uku na lalace ni ikilima"
Kuka sosai Hajiya Ikee ke yi, shawara Sultana ta kawo, akan su maida Gwamna gida a na maganin Islamic, saboda yanzu kusan watan shi biyu a kwance, komai sai an masa, Hajiya duk ta rame,
"Ai dole gida zamu kai shi, in kunka ji kuddin da asibitin ga ke karba duk kwana guda sai tsoron Allah ya kama mutum, gwamnan da an ka mayar yanzu so guda ya taho da tawagar shi sun ka duba Daddyn ku, da 'yan jarida, akai ta hotuna da video, ko sisi basu bamu ba, amma sun ce sun basuwa kuddin jinya har ya ji sauqi, kuma ga shi asibiti kullum ni ka biyan kuddi"
"Hummm Mum kenan, a bar tone tone, mu samu yanzu a kama muna shi mu tai gida"
Bayan komawar su gida ne suka sha kallon ikon Allah, gwamna banda ihu da shure shure ba abinda yake, abun ya yi matuqar basu mamaki,Sultan ne ya ce su fitar da shi waje, ai kuwa ana fita waje ya dena ihun, sai zare ido kawai yake, da jin tsoron kar a maida shi ciki.
"Sultan mu tai gidan mu na can titin zanna, wataqilan nan ne bashi so"
"Bamu da wani gida da ya yi saura sai wanga, dan kuwa duk na bayar, anjima ma za a taho amsar makullai,nan din dai zamu koma, dole ya yi hankuri,"
"Yau na shiga uku na lalace ni Ikillma, kai wa Allah ku bamu makullin guda, wanda ka bawa wancan su amshi wanga"
"Muka san menene acikin gidan da za mu ba wa wasu shi? Mu din dai mu za mu shiga,koma menene ku ne kun ka jawo muna, dole a haka zamu shiga mu zauna da koma me ne ne a ciki"
Sultana ta kula da cewa ran Sultan ya fara ɓaci, abinda bai taba yi da iyayen su ba kenan, bayyanar da bacin ran shi irin haka, su kafe ya kafe, dan haka shiga maganar ta yi,
"Hajiya mu shiga sai a nemo mallammai masu ruqiyya su taho su taimaka muna, ko ya ka ce Yah Sultan"
Dauke kan shi ya yi, sannan ya ce,
"Ku shiga ciki, bari na shiga gari na samo malamin da zai zo a hwara tun yanzu, makullan gidan su na cikin safe din Daddy, ki bude ki basuwa in an zo amsa"
"Toh sai ka dawo"
*Ku taimakawa gwamna Halliru da malami me ruqyaaa*
💅🏻 *A GARIN MU* 💅🏻
BY HAERMEEBRAERH
PAGE 60:
Sultan ya yi yawo, iya yawo amma bai samu dacewa da malami ko guda d'aya da zai taimake su ya je ya yi wa Gwamna Halliru ruqiyya ba, wanda suka amince za su je kuma bai gamsu da kalar tasu ruqiyyar ba, dan kuwa cewa suke aljanun yanka suke so a musu su sha jini, za su rabu da shi, (da damar masu cewa su na cire aljanu da yanka, ko kuma aljani ya fadi buqatar shi a masa sanan ya fita, ba rugiyya suke ba, domin ba haka ake ruqiyya ba a sunnar Annabi Muhammad ,bai bamu umarnin yi wa aljani hidima ba, kar fa mu manta Allah ya daukaka mu sama da su, kuma cutar da mu suke saboda ba ma ganin su, amma kuma a dinga musu hidima? Ko a je wajen su neman taimako? Duk wanda yake haka ya sabawa Allah, in bai tuba ba Allah zai kama shi, ko ya azabtar da shi kamar yanda gwamna halliru ke shan wahala a hannun su, ya nemi taimakon su ba na Allah ba, su kuma a yanzu suna azabtar da shi, saboda abinda ya kasance ya na aikatawa).
Da kyar ya samu wani malami guda ɗaya da ya amince zai je ya ga Gwamnan, amma sai da yamma, bayan ya sallami d'aliban shi da ke d'aukan karatu a wajen shi.
Sultan ya koma gida a gajiye, tun daga gate ya ke jiyo kururuwa da ihun gwamnan, gidan shiru, ba wata hayaniya, dan kuwa duk ma'aikatan sun gudu, mai gadi ne guda d'aya kawai ya rage, shi ma dan bashi da wajen zuwa ne, ya sa ya ke zaune a nan din.
Da shigar Sultan gidan, Sultana ta tunkare shi, idanun ta sun yi luhu luhu, saboda kukan da ta sha ta qoshi, ganin mahaifin nasu a cikin mawuyacin halin nan ba qaramin tashin hankali bane a gare ta, ko ba komai, ya gwada masu soyayyar da bata da misali.
"Yah Sultan ya na gan ka kai d'ai? Suman Daddy uku bayan tahiyar ka, na rasa me zan masa ya samu sauqin abinda yake ji"
Kuka ta fashe da shi, saboda tsananin tausayin mahaifin nasu, sultan ne ya kama hannun ta, idanun shi sun yi jajawur, ya ce,
"Mu je ciki, ki dena kukan haka nan, kukan ki ba shi zai bashi lahiya ba,daddy addu'a shi ke buqata, mu tai a samu a kunna karatun Alkur'ani kahin mallam ya taho, dan ba yanzu ne zai taho ba, sai yamma"
Cikin ikon Allah kuwa ana kunna masa karatun Alkur'ani bacci mai dadi ya dauke shi, zama suka yi jingum jingum su na kallon shi, kowannen su da abinda yake saqawa a zuciyar shi.
Hayaniya suka jiyo sosai, daga wajen gate din gidan, a tare suka tashi suka nufi waje, Hajiya babu ko mayafi, daga ita sai leshin jikin ta da d'ankwali, Sultana kuwa tun da suka je bata cire mayafin ta ba, haka suka fita.
'Yan jarida ne sun kai su takwas a qofar gidan, sai roqon mai gadin suke ya bar su su shiga daukan rahoto.
Su na ganin iyalin gwamnan kuwa suka hau daukan su hoto, tare da qoqarin yi musu tambayoyi, tambayoyin kuwa sun matuqar sanya Sultan da Sultana jin nauyi da kunyar amsa su, tambayoyi ne wanda da suke tattare da gaskiya, amma kuma ba za su iya amsa su ba kai tsaye.
Dan haka Sultan ya musu izinin shiga,kamar jira suke, cikin turereniya da rige rige suka shige gidan.
Zama Sultan ya yi a saman kujera da ke a farfajiyar gidan, sannan ya ce,
"Tambayoyin duk da kun ka yi muna, sun nuna cewa wasu daga cikin 'yan jarida musulmai ba su san amfanin aikin jarida ba ga rayuwar su, ta duniya da lahira, domin kuwa da damar su su yad'a labarin da zai jawo su yi suna, ko su samu wata daukaka ta duniya, ko arziqi shi d'ai suke bid'a, ba labaran da za su gyara, kuma su taimaki al'umma ba,misali, yanzu kun taho ku na so ku ji mi na na ya sami tsohon Gwamna, kun taho da list din zargin da mutane ka yi akan shi, me ya sa sanda shi na kan mulki, ba ku zuwa dan taimaka masa wajen yi mishi tambayoyin da za su sa ya yi aiki dole? Ko ku na nufin ba ku da wadannan tambayoyin tun gabanin ciwon shi?
To Bari na baku amsa, amsar da na ke so ku yad'a ta a duniya kowa ya ji, da farko dai dole ne mu san cewa duk abinda ya ke faruwa gare mu a wannan qasa, da wannan yanki,na harikar kidnapping, da kashe kashen rayuka, da sace dukiyoyin al'umma, ba komai ya jawo mana ba, sai sab'awa Allah, daga mu har shugabannin mu, domin kuwa Allah ya ce,
"Wancan ne, haka abin yake, lallai Allah bai kasance yana canza wata ni’ima da ya ni’imta akan wasu mutane ba face har sai sun canza abin da yake cikin rayukansu, kuma lallai Allah mai ji ne, kuma masani.”
(Suratul Anfal: 53)