Sashe 52
A Garin Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Subhanallah me ya faru haka?"
Hajiya Ikee da Gwamna ne ke tafe, kowannen su zuciya ba dadi, ganin me ke faruwa ne ya sanya su zuwa wajen suma,Hajiya ta tuna ya akai ya samu wannan raunin, sanda ya fasa masu table din su mai kyau da tsada ne ya samu ciwon, kauda kai ta yi ta bata rai, dan ba ta so ma ta kalli jinin da ke diga a saman tsadadden carpet din ta.
"Sultana tai ki dakko fist aid box,yi sauri"
"To Yah Sultan"
Duk ta kidime ta rude, a wajen Lawwali wannan is just a scratch ,amma su a wajen su babban ciwo ne, sai da Sultan ya gama gyara ma Lawwali ciwon sannan Sultana ta kalle shi, cikin kulawa ta ce,
"Gaskiya yau, ba inda zaka, ka zubar da jini da yawa, ka zauna, a samu wasu guards din su kai ni"
"Ba za a yi haka ba Ran ki shi dade, ba damuwa ai an saka min magani, zan iya kai ki"
"Ni dai gaskiya ahhh ahhh, Daddy ka ce wani abu manaa"
Gwamna Halliru ba abinda ya ke da ya wuce kallon ikon Allah ,yaushe Lawwali ya ci shi da yaqi haka?'yar shi har bata iya boye soyayyar shi a gaban su, murmushin gefen baki Lawwali ya yi, ya kafe Gwamna da idanun shi da ke dauke da kallo irin na tsokana.
"Daddyyyy ka mishi magana pls, ya ji ciwo a hannun shi fa"
"Amm...uhmmm..Lawwali ina ga ka d'ai zauna, zan samu masu kai ta kawai"
"Ran ka shi dade Sultana ba uwar daki na bace kadai ta nada matsayi mai girman da ba zan iya barin wani abu ya same ta ba, kasan yanzu yanda duniya talalace, kana kauda ido sai ka nemi naka ka rasa,"
Cikin wani irin salo da kwarewa ya yi maganar, Hajiya Ikee da Gwamna sun gane karatun, karr kuma tarr a zuqatan su.
"Sultana kar ki damu, kuje kawai, wa ya fada maki, dan wanga ciwo na damun mazaje? Ai zaman gida se mata"
Har sun kama hanya za su fita Sultana ta koma ciki,cike da dan jin nauyi ta tsaya gaban Daddyn su, tare da kama hannun shi ta ce,
"Daddy, tunda Allah ya dawo da kai lafiya, ga ka ga Hajiya, Yah Sultan da Auwal din kan shi, ka jima ka na min magana akan rashin kula maza da nake, ka na cewa a haka zan yi aure watarana? Tau Daddy yau ina so na sanar da ku cewa na zabi Auwal ya zama abokin rayuwa ta, dan Allah Daddy kar ka ce ah ah, shi nake so, shi nake fatan ya zama abokin rayuwa ta, ba zan iya rayuwa da kowa a matsayin miji ba bayan shi,dan Allah Daddy"
Hajiya Ikee ce ta bude baki za ta yi magana, suka hada ido da Lawwali da ya sunkuyar da kan shi, amma idanun shi na d'age ya na kallon kowa,kallon da ya mata ya yi matuqar shiga kowace kafa ta jikin ta, nan take ta tuna maganar da Gwamna Halliru ya mata a can parlour'n baqi.
'Ke hwaa baki da hankali, sai ki dinga abu babu lisahi,halan baki ga mi ya nuna mana ba, ido da ido kin gan ni sanda na ke duba makaman da za a kai musu daji,tare da ni da su muna hira cikin nishadi, ido da ido kin ganni ina yanka jarirrai har guda ukku (jarirai) kin ga yanda ya ke kisan mutane kamar ya samu kiyashi,amma kin fi so wai har sai asirin mu ya tonu sannan ki nutsu, d'iyar da ki ke taqama taki ce, za ki aurawa shugaban qasa ta san me muke aikatawa sai ta tsane mu,Za ki iya jure tsanar da 'ya' yanmu za su yi mana? In ki na iyawa ni ban iyawa, Sultana ruhi na ce, ba zan taba bari wani abu ya same ta ba, dan su nake duk wanga abu da kika gani, dan na wadata su da dukiya da jin dadin duniya nake abubuwan ga, dan haka in ki ka kuskura ki ka kawo abinda Yaron nan zai bata min suna a duniya, sai na halaka ki da hannu na wallah'
Ihun murnar Sultana ne ya dawo da ita daga duniyar tunanin da ta lula, Sultana ce ta saki daddyn ta,ta tafi da gudu kamar wata qaramar yarinya, ta fada jikin Hajiya Ikee, ta ce,
"Hajiya Daddy ya amince, zai aura min Auwal, Hajiya ba ki ce komai ba, kin amince da zabi na?"
Wani abu ne mai daci da maqaqi ya tokare wuyan Hajiya Ikee, har wani d'aci-d'aci take ji a wuyan ta, idanun ta sun qanqance, saboda baqin cikin da ke cin zuciyar ta, amma ba halin bayyanawa, cikin Muryar da kamar shaqe mata wuya akai, ta ce,
"Na amince, Allah ya sanya albarka"
Rungume ta Sultana ta yi, ta na farin ciki sosai, ranta fari tass, kamar madarar shanu, Sultan ma sai wangale baki yake, ya na taya qanwar shi murna.
Dan gyara tsayuwar shi ya yi, ya wani turo qirji gaba, shi a dole ga babban yaya, gyaran murya ya yi, sannan ya ce
"Ban gane ana ta neman izini ba , ba wanda ya nemi nawa?"
Lawwali ne ya duqa cikin wasa, da dariya, ya ce,
"Ran Babban yaya shi dade, a mana ahuwa, ina neman izinin auren Sultana a hannun ka"
Cikin dake wa, Sultan ya dafa kan Lawwali, ya ce,
"Na baka izinin auren qauna ta, Allah ya muku albarka,"
Dariya sosai Sultana take, Lawwali na taya ta, Sultan ma cikin dariya ya dafa kafadar Lawwali ya ce,
"Congratulations man,Allah ya sa ayi da mu"
"Thanks bro, ameen, bari mu tai, lokaci na tahiya"
"Yau ba za mu zauna mu yi murnar wannan rana ba?"
Cikin shagwaba Sultana ta fadi hakan, ta na dan noqe kafada, ba qaramin kyau ta wa Lawwali ba, iyayen ta kuwa a zuciyar su sai suka gan ta, kamar yar qaramar yarinyar su, da suke matuqar lele, da qauna a zuqatan su.
Sultan ne ya kama kumatun ta, cikin sigar wasa ya ce,
"Ohhh Baby Sulty za ta zama babbaaa, ki tafi NGO din ki, ki gode Allah ma ki na da abun yi, unlike me, sai dai a dahwa a bani na ci, na kwanta, da jikin qiba gare ni, da na fi wata mata da aka kira da Hameedan Hamma (Lols)"
Dariya sosai Sultana ta yi, amma abu daya na d'an damun zuciyar ta, kallon kallon da ke tsakanin iyayen ta da Lawwali, da kuma rashin fara'ar su, da walwalar su, a wajen ta wannan babban abun farin ciki ne, da sauri ta kawar da tunanin komai, da ta tuna dalilin da ya sa iyayen ta ba su cikin farin ciki sosai,Lawwali talaka ne, kuma driver, sun amince ne kawai saboda farin cikin ta, babu komai, hakan ma sun taimaki rayuwar ta ai, ta na godiya.
Sallama suka ma iyayen na su suka tafi, ko da ya je bude mata mota da sauri ta bude, ta ce ta gode, ya kula da hannun shi, ba dan ya ce ba komai ba ma, yau ba inda za su.
Zuciyar su fari tasss suka isa, Lawwali kan shi jin amincewar su Hajiya Ikee ya ke a matsayin wata babbar nasara da ya taba samu a rayuwar shi,duk da dai har yanzu auren Sultana ya na nan a matsayin auren daukar fansa a zuciyar shi, (zan so ganin anyaa Oga zai cika wannan alqawari da ya daukar wa kan shi? Sultana ce fa).
************************
Kwanan su Hansatu uku ba wuta, saboda NEPA sun yanke musu wuta, sakamakon rashin biyan kudin da ba su yi ba, wayar ta babu caji, sai dai ta kai gidan 'Yabbuga, daga kaiwa jiya, yau an kai 'Yabbuga ta fara masifar za a dame ta da saka cire din caji, ba aikin ta ba kenan, kar su dame ta.
Dan haka Hansatu da kan ta, ta saka Hijabi ta kai wayar ta gidan Asshibi, dan sun dan saba yanzu, su na dan ziyarar junan su.
Ta tarar da Mijin Asshibi zai fita, suka gaisa, ta tambaye shi ko Asshibi na nan ta kawo caji ne, ya tabbatar mata da cewar ta na ciki, ya fice abin shi.
Ya na shiga Mota ya danna kiran Isah, bayan sun gaisa, ya tambaye shi ya Makkan, Isah ya kalli kayan abincin da ke gaban shi, ya shafa tumbin shi da ya fara ajiye wa ya ce,
"Laminu Makka ta yi, ka ci ka sha ka kwanta ka yi bacci, ba me tashin ka,in kuwa ka na da suruka kamar tawa ko ba ka sana'a zaka warwasa Alhaji"
"Shegen kaya, ka na can ka na tatsar surukar ka a nan"
"Bari kawai Laminu, shekaran jiya ni ce mata an kwace sauran goro da ni tai da shi, ta tausaya min sosai, ta aikon da dubu dari biyu,"
"Dan iska, shi ne ba ka turo min ko yar hamsin ba ce nima na dan more kuddin surukar taka"
Hansatu ce ta je zata wuce, ya yi shiru ya dena magana, sai da ta fita ya ce,
"A gaskiya Isah in ka dawo ka ga Hansatun ka ba zaka gane ta ba, ka ga yanda ta yi qiba, ta yi mulmul da ita, wagga ba da ban taka ta ba ai sai na kai mata ziyara"
Da sauri Isah ya zauna daidai, ya ce,
"Kar ka kuskura, kar ka soma taba min mata, ko da ka ga ina abinda na ke so, dan na san na kama ta a hannu ne, har yanzu a hannu take, ina son mata ta, kar ka kuskura....akwai wata harqalla da ya kamata fa mu hada Alhaji, za ta kawo wuta sosai, ya kamata a hada ta yau yau din nan, kafin ta zo karbar wayar ta anjima"
"Kwantas, ni ba abinda zan da matar aure, ga 'yan mata nan, masu taken zawarawan gida? Ka biya kudin shawarma yanzu ka samu yadda ka ka so, wace harqalla ka ke magana akai?"
"Shegen sama Asshibi na gida ana cin amanar ta a waje, sai ka koma gida ka zam kamar bawan ta, ita ko gani takai kamar duk duniya ta hi kowa Sa'ar miji"
"Iya taku kenan"
Hajiya Ikee da Gwamna ne ke tafe, kowannen su zuciya ba dadi, ganin me ke faruwa ne ya sanya su zuwa wajen suma,Hajiya ta tuna ya akai ya samu wannan raunin, sanda ya fasa masu table din su mai kyau da tsada ne ya samu ciwon, kauda kai ta yi ta bata rai, dan ba ta so ma ta kalli jinin da ke diga a saman tsadadden carpet din ta.
"Sultana tai ki dakko fist aid box,yi sauri"
"To Yah Sultan"
Duk ta kidime ta rude, a wajen Lawwali wannan is just a scratch ,amma su a wajen su babban ciwo ne, sai da Sultan ya gama gyara ma Lawwali ciwon sannan Sultana ta kalle shi, cikin kulawa ta ce,
"Gaskiya yau, ba inda zaka, ka zubar da jini da yawa, ka zauna, a samu wasu guards din su kai ni"
"Ba za a yi haka ba Ran ki shi dade, ba damuwa ai an saka min magani, zan iya kai ki"
"Ni dai gaskiya ahhh ahhh, Daddy ka ce wani abu manaa"
Gwamna Halliru ba abinda ya ke da ya wuce kallon ikon Allah ,yaushe Lawwali ya ci shi da yaqi haka?'yar shi har bata iya boye soyayyar shi a gaban su, murmushin gefen baki Lawwali ya yi, ya kafe Gwamna da idanun shi da ke dauke da kallo irin na tsokana.
"Daddyyyy ka mishi magana pls, ya ji ciwo a hannun shi fa"
"Amm...uhmmm..Lawwali ina ga ka d'ai zauna, zan samu masu kai ta kawai"
"Ran ka shi dade Sultana ba uwar daki na bace kadai ta nada matsayi mai girman da ba zan iya barin wani abu ya same ta ba, kasan yanzu yanda duniya talalace, kana kauda ido sai ka nemi naka ka rasa,"
Cikin wani irin salo da kwarewa ya yi maganar, Hajiya Ikee da Gwamna sun gane karatun, karr kuma tarr a zuqatan su.
"Sultana kar ki damu, kuje kawai, wa ya fada maki, dan wanga ciwo na damun mazaje? Ai zaman gida se mata"
Har sun kama hanya za su fita Sultana ta koma ciki,cike da dan jin nauyi ta tsaya gaban Daddyn su, tare da kama hannun shi ta ce,
"Daddy, tunda Allah ya dawo da kai lafiya, ga ka ga Hajiya, Yah Sultan da Auwal din kan shi, ka jima ka na min magana akan rashin kula maza da nake, ka na cewa a haka zan yi aure watarana? Tau Daddy yau ina so na sanar da ku cewa na zabi Auwal ya zama abokin rayuwa ta, dan Allah Daddy kar ka ce ah ah, shi nake so, shi nake fatan ya zama abokin rayuwa ta, ba zan iya rayuwa da kowa a matsayin miji ba bayan shi,dan Allah Daddy"
Hajiya Ikee ce ta bude baki za ta yi magana, suka hada ido da Lawwali da ya sunkuyar da kan shi, amma idanun shi na d'age ya na kallon kowa,kallon da ya mata ya yi matuqar shiga kowace kafa ta jikin ta, nan take ta tuna maganar da Gwamna Halliru ya mata a can parlour'n baqi.
'Ke hwaa baki da hankali, sai ki dinga abu babu lisahi,halan baki ga mi ya nuna mana ba, ido da ido kin gan ni sanda na ke duba makaman da za a kai musu daji,tare da ni da su muna hira cikin nishadi, ido da ido kin ganni ina yanka jarirrai har guda ukku (jarirai) kin ga yanda ya ke kisan mutane kamar ya samu kiyashi,amma kin fi so wai har sai asirin mu ya tonu sannan ki nutsu, d'iyar da ki ke taqama taki ce, za ki aurawa shugaban qasa ta san me muke aikatawa sai ta tsane mu,Za ki iya jure tsanar da 'ya' yanmu za su yi mana? In ki na iyawa ni ban iyawa, Sultana ruhi na ce, ba zan taba bari wani abu ya same ta ba, dan su nake duk wanga abu da kika gani, dan na wadata su da dukiya da jin dadin duniya nake abubuwan ga, dan haka in ki ka kuskura ki ka kawo abinda Yaron nan zai bata min suna a duniya, sai na halaka ki da hannu na wallah'
Ihun murnar Sultana ne ya dawo da ita daga duniyar tunanin da ta lula, Sultana ce ta saki daddyn ta,ta tafi da gudu kamar wata qaramar yarinya, ta fada jikin Hajiya Ikee, ta ce,
"Hajiya Daddy ya amince, zai aura min Auwal, Hajiya ba ki ce komai ba, kin amince da zabi na?"
Wani abu ne mai daci da maqaqi ya tokare wuyan Hajiya Ikee, har wani d'aci-d'aci take ji a wuyan ta, idanun ta sun qanqance, saboda baqin cikin da ke cin zuciyar ta, amma ba halin bayyanawa, cikin Muryar da kamar shaqe mata wuya akai, ta ce,
"Na amince, Allah ya sanya albarka"
Rungume ta Sultana ta yi, ta na farin ciki sosai, ranta fari tass, kamar madarar shanu, Sultan ma sai wangale baki yake, ya na taya qanwar shi murna.
Dan gyara tsayuwar shi ya yi, ya wani turo qirji gaba, shi a dole ga babban yaya, gyaran murya ya yi, sannan ya ce
"Ban gane ana ta neman izini ba , ba wanda ya nemi nawa?"
Lawwali ne ya duqa cikin wasa, da dariya, ya ce,
"Ran Babban yaya shi dade, a mana ahuwa, ina neman izinin auren Sultana a hannun ka"
Cikin dake wa, Sultan ya dafa kan Lawwali, ya ce,
"Na baka izinin auren qauna ta, Allah ya muku albarka,"
Dariya sosai Sultana take, Lawwali na taya ta, Sultan ma cikin dariya ya dafa kafadar Lawwali ya ce,
"Congratulations man,Allah ya sa ayi da mu"
"Thanks bro, ameen, bari mu tai, lokaci na tahiya"
"Yau ba za mu zauna mu yi murnar wannan rana ba?"
Cikin shagwaba Sultana ta fadi hakan, ta na dan noqe kafada, ba qaramin kyau ta wa Lawwali ba, iyayen ta kuwa a zuciyar su sai suka gan ta, kamar yar qaramar yarinyar su, da suke matuqar lele, da qauna a zuqatan su.
Sultan ne ya kama kumatun ta, cikin sigar wasa ya ce,
"Ohhh Baby Sulty za ta zama babbaaa, ki tafi NGO din ki, ki gode Allah ma ki na da abun yi, unlike me, sai dai a dahwa a bani na ci, na kwanta, da jikin qiba gare ni, da na fi wata mata da aka kira da Hameedan Hamma (Lols)"
Dariya sosai Sultana ta yi, amma abu daya na d'an damun zuciyar ta, kallon kallon da ke tsakanin iyayen ta da Lawwali, da kuma rashin fara'ar su, da walwalar su, a wajen ta wannan babban abun farin ciki ne, da sauri ta kawar da tunanin komai, da ta tuna dalilin da ya sa iyayen ta ba su cikin farin ciki sosai,Lawwali talaka ne, kuma driver, sun amince ne kawai saboda farin cikin ta, babu komai, hakan ma sun taimaki rayuwar ta ai, ta na godiya.
Sallama suka ma iyayen na su suka tafi, ko da ya je bude mata mota da sauri ta bude, ta ce ta gode, ya kula da hannun shi, ba dan ya ce ba komai ba ma, yau ba inda za su.
Zuciyar su fari tasss suka isa, Lawwali kan shi jin amincewar su Hajiya Ikee ya ke a matsayin wata babbar nasara da ya taba samu a rayuwar shi,duk da dai har yanzu auren Sultana ya na nan a matsayin auren daukar fansa a zuciyar shi, (zan so ganin anyaa Oga zai cika wannan alqawari da ya daukar wa kan shi? Sultana ce fa).
************************
Kwanan su Hansatu uku ba wuta, saboda NEPA sun yanke musu wuta, sakamakon rashin biyan kudin da ba su yi ba, wayar ta babu caji, sai dai ta kai gidan 'Yabbuga, daga kaiwa jiya, yau an kai 'Yabbuga ta fara masifar za a dame ta da saka cire din caji, ba aikin ta ba kenan, kar su dame ta.
Dan haka Hansatu da kan ta, ta saka Hijabi ta kai wayar ta gidan Asshibi, dan sun dan saba yanzu, su na dan ziyarar junan su.
Ta tarar da Mijin Asshibi zai fita, suka gaisa, ta tambaye shi ko Asshibi na nan ta kawo caji ne, ya tabbatar mata da cewar ta na ciki, ya fice abin shi.
Ya na shiga Mota ya danna kiran Isah, bayan sun gaisa, ya tambaye shi ya Makkan, Isah ya kalli kayan abincin da ke gaban shi, ya shafa tumbin shi da ya fara ajiye wa ya ce,
"Laminu Makka ta yi, ka ci ka sha ka kwanta ka yi bacci, ba me tashin ka,in kuwa ka na da suruka kamar tawa ko ba ka sana'a zaka warwasa Alhaji"
"Shegen kaya, ka na can ka na tatsar surukar ka a nan"
"Bari kawai Laminu, shekaran jiya ni ce mata an kwace sauran goro da ni tai da shi, ta tausaya min sosai, ta aikon da dubu dari biyu,"
"Dan iska, shi ne ba ka turo min ko yar hamsin ba ce nima na dan more kuddin surukar taka"
Hansatu ce ta je zata wuce, ya yi shiru ya dena magana, sai da ta fita ya ce,
"A gaskiya Isah in ka dawo ka ga Hansatun ka ba zaka gane ta ba, ka ga yanda ta yi qiba, ta yi mulmul da ita, wagga ba da ban taka ta ba ai sai na kai mata ziyara"
Da sauri Isah ya zauna daidai, ya ce,
"Kar ka kuskura, kar ka soma taba min mata, ko da ka ga ina abinda na ke so, dan na san na kama ta a hannu ne, har yanzu a hannu take, ina son mata ta, kar ka kuskura....akwai wata harqalla da ya kamata fa mu hada Alhaji, za ta kawo wuta sosai, ya kamata a hada ta yau yau din nan, kafin ta zo karbar wayar ta anjima"
"Kwantas, ni ba abinda zan da matar aure, ga 'yan mata nan, masu taken zawarawan gida? Ka biya kudin shawarma yanzu ka samu yadda ka ka so, wace harqalla ka ke magana akai?"
"Shegen sama Asshibi na gida ana cin amanar ta a waje, sai ka koma gida ka zam kamar bawan ta, ita ko gani takai kamar duk duniya ta hi kowa Sa'ar miji"
"Iya taku kenan"