Sashe 31
A Garin Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A hankali suke takawa zuwa ga junan su, Sultana ji ta yi kamar ta kwantar da kan ta a faffadan qirjin shi, ko abinda take ji zai ragu, Lawwali ji ya ke kamar ya isa ya rungume ta, ta shafa kan shi da siraran yatsun ta, tare da fada masa cewar 'Komai zai wuce, zai yi daidai' a cikin kunnen shi.
Sun jima su na kallon juna kafin Sultana ta yi qarfin halin cewa,
"Why? Me yasa? Me ya sa za ka tafi a lokacin da zuciya ta, ta amince, ta yarda, ta kuma gamsu da ta kamu da matsanancin ciwon son ka? Me ya sa ka tafi, a lokacin da nake tsananin buqatar ka, ka kuwa san ya nake ji a nan dina? (Ta sanya hannu, ta nuna saitin zuciyar ta, cikin kuka,) ba zaka gane ba, saboda baka san me ne ne soyayya ba ga dukkan alamu,"
Cikin sauri ya dakatar da ita, dan kalaman ta na sake harzuqa zuciyar shi, ta na hango masa mugunta kala kala.
Cikin cije lebunan shi a cikin bakin shi ya shafa kan shi, da hannu daya, sannan ya ce,
"Sultana, ba ke dai ka jin duk abinda kin ka lissahwa ba, ni ma ina ji dika, wataqila har da dori ma, amma sultana ba ke d'aya zuciya ta ke so ba, qauna ta ita ce rayuwa ta, ban da komai banda kowa sama da ita,ita kad'ai ce gata na a duk qasar ga, ba mai so na tsakani da Allah, sama da ita, a yanzu haka ji na nake kamar duk duniya sun juyan baya, ni kadai ne, ban da kowa banda komai,"
"Wait a minute,me ya samu Mubaraka?"
A cikin tashin hankali Sultana ta masa wannan tambayar, a cikin qasa da minti bakwai ya bayyana mata me ya faru dangane da batan ta,da kuma irin neman da yake mata, bai samu ba.
Cikin kuka Sultana ta juya ta rufe bakin ta, ta jima a haka ta na kuka, Lawwali ma ji ya ke kamar ya yi kukan, sai daga baya ta juya gare shi, ta na share hawayen ta, motar ta ta fara budewa zata shiga,sannan ta ce,
"Mu je gida Daddy na nan yau, mu sanar da shi,a sanya neman ta, duk inda ta shiga, i love her, she is a gud gurl, I can't let anything happen to her, she is like a sister to me, mu je gida Auwal, maza shiga mota mu je,"
Kallon gidan su ya yi, cikin takaici, ya na jiyo muryoyin mata ana ta zabga hira, ya ji haushi da be shiga ya tarwatsa su ba, qanwar shi ta bata amma suke hira haka ana dariya har waje ana ji, ya so ya shiga ya gan su, da duk sai ya musu rashin mutunci d'aya bayan d'ayan su, amma ba komai next time.
Kwafa ya yi, ya shige motar shi, ya bi ta su Sultana.
*************************
Gwamna Halliru na ganawa da su No 1 da 4, su na tattaunawa akan yanda Lawwali ya haukace.
Sultana ta je za ta shiga parlour wasu masu tsaron wajen ne suka dakatar da ita, tare da sanar da ita cewar Gwamna ya ce kar a bawa Kowa damar shiga, sai da izinin shi, d'aya daga cikin su ta kalla tace,
"Ka je ka sanar da shi ni ce, na ke son magana da shi, ya na da mahimmanci na gan shi yanzu"
Har security din zai tafi, Lawwali ya qarasa shiga wajen, su na hada ido, security ya ja baya, tare da fadin,
"Ran ka ya dade Oga, Barka da zuwa"
"Gwauna hwa? "
"Shi na ciki Oga"
Mamaki ne danqare a cikin Sultana, an hana ta shiga amma an budewa Lawwali ya shige,me kenan? Lawwali ya fi ta matsayi a gidan Uban ta kenan?
Ko da suka shiga shiru wajen ya dauka, ba No 4 da ake tausa ba, ana nuna masa ba abinda Lawwali zai yi, as long as bai gane ina qanwar shi take ba, har Gwamnan kan shi sai da hankalin shi ya tashi ainun.
Cikin rawar murya, No 4 ya ce,
"O....ogaa, kai ne da rana haka?"
Lawwali ko kallon No 4 be ba, ya samu kujera ya zauna, tare da harde qafa,No 1 ne ya je ya tsaya a daf da shi,hakan kamar girmamawa ne a gare shi, No1 na ta hararar No 4 tare da yi masa nunin ya nutsu, Sultana kuwa mamakin abinda take gani ya fi qarfin ta, waje ta samu ta tsaya, ta na kallon yanda mahaifin ta ya yi lakwas a gaban Lawwali, bai magana ba akan zaman da Lawwali ya yi a gaban shi .
"Oga har yanzu fa shiru,yanzu haka mun kawo maganar ne wajen Excelency saboda a bamu taimako"
"Mu ma abinda ya kawo mu kenan,na yi iya qoqari na na kasa, ina neman taimako a hukumance, a bido min qauna ta, in ba haka ba,....."
Shiru ya yi, ya taune leben bakin shi na qasa, tare da dukan tafin qafar shi da ya dora a saman dayar qafar tashi.
"Ah ah Sultana, mik-kawo ki nan?"
"Tare muke,"
"Ban gane tare kuke ba, qaqa an kai kuke tare?"
"Dad Mubaraka ce ba a gani ba, kusan sati Uku yanzu, shi ne na rako shi neman taimako wajen ka, amma yanzu na kula is like, ni anka rako, ko wani zai iya min bayani akan abubuwan da nake gani a yanzu?"
Da sauri gwamna ya zari wayar shi, ya kira Head quarter na yan sanda, ya fara bada report din batan Mubaraka, Sultana tuni ta manta da tambayar da take yi, ita da Lawwali sun bawa Gwamna hankulan su.
Wayar aka bawa Lawwali ya yi kwatancen ta,da bayanin ranar da suka nemeta suka rasa, tare da alqawarin ze tura hotunan ta.
Godiya ya miqe sosai ya na wa gwamna, Sultana ma haka.
Gwamna na son bin su ya ji dalilin da ya sa suke a tare, kuma ya na son magana da su No 1, dan haka sai da ya bari su Lawwali sun fita, sannan ya qara jaddada musu su yi taka tsantsan ta yanda asirin su ba zai tonu ba, domin in Lawwali ya san sun sace qanwar shi, har shi kan shi ba zai tsira ba, ballantana su.
Wannan kalamai sun sake birkita No 4, da kyar yake hadiyar yawu, zufa sai karyo masa take, a sati ukun nan, duk 'yar qibar ma da ya yi, saboda kudin da suke samu, duk ta zabge, ya fita hayyacin shi, ba wani kwanciyar hankali a tattare da shi.
Su Sultana kuwa a jikin motar shi, suka tsaya, su na magana, hira ce mai dadi,ta yaushe gamo suke yi, kusan kaso saba'in na hirar dukkan su akan Mubaraka su ke yi, Sultana na son mubaraka, ba wai dan ta na qanwar Lawwali ba,ah ah, yarinyar abar so ce ga duk mai hankali.
Shi kuwa a wajen shi Mubaraka ita ce rayuwar shi, a ganin shi ma ba zai taba samun kan Sultana ba in bata nan.
Bayan sun yi sallama za su tafi ne Sultana ta ce,
"Haka ake sallama da masoyi? "
Kallon yanda ta maida kai gefe ta yi, sai ta masa kyau, murmushi ya yi, kadan, wanda rabon shi da murmushi na gaskiya, ba na mugunta ba, tun kafin batan Mubarakan.
"Ya ya kamata masoyi ya yi sallama ?"
Dan rufe fuskar ta tayi da hannun ta kadan ta ce,
"Kamata ya yi ka ce, Sultana na tafi, zan dawo anjima, ina son ki"
Bude baki Lawwali ya yi, ya na dariya mai sassanyan sauti, ya ce,
"Kaiii ka kaiii ka kaiii, Baraka na ta ce man ke ustaziya ta wallah, ashe ke iya soyayya haka?"
Mayafin ta ta ja sosai ta rufe fuska sannan ta ce,
"To ai soyayya kowa na yi"
"Ok, to sultana Ina son ki,"
Wani irin dad'i ne ya ziyarce ta, musamman da ta kalle shi ta ga babu wasa a kalaman shi, iyakar gaskiyar shi yake fada, ta ji sautin Muryar shi, ba alamar gatse ko wasa, amayar da ta ta zuciyar ta ce,
"Auwal ina son ka, In na ce ina son ka, ba ina nufin ina son ka fiye da yanda kk so na bane, ina nufin ina son ka a kowanne hali, ina son ka ko da wani sabani ya haɗa mu, ina son ka ko da ka na cikin damuwar da ta sa ka nesanta da ni, ina son ka sama da nisan nan da ke tsakanin mu,ina son ka sama da yanda na ke jin zafin rashin ka a rai na, ina son ka sama da dukkan wani abu da zai qoqarin shiga tsakanin mu, ina nufin nafi son ka Auwal"
Ya Salam, Lawwali ya gama narkewa,kalaman sultana sun wanke masa wani kaso na baqin cikin da ke ran shi,dama haka take fata, shi ne dalilin da ya sanya ta cire kunya ta furta abinda ke ran ta, sai bayan ta gama kashe masa gabban jikin shi, ta juya da gudu gudu ta shige gida,dan kuwa kunyar shi ba zata bar ta ta tsaya jin me zai ce ba again.
Lawwali ya jima a wajen, kafin ya shiga motar shi, ya tada ya bar gidan.
Su No 1 kuwa ya na fita suma suka bar gidan, dan zuwa sauyawa su Mubaraka maboya kamar yanda Gwamna ya bada shawara, da kuma wajen zama.
Lawwali har ya isa gida bai dena murmushi ba, ya jima ya na dirzar dattin jikin shi,kafin ya samu abinci ya ci rabon shi da abinci sosai kamar na ranar ba zai iya fadin ga lokacin ba.
Ya na kammalawa ya kwanta, dan hutawa.
**********************
Vissa ta samu, na tafiyar Isah Saudiya, ana sauran kwana biyu tafiyar Isa, Hajiya ta sa Isan ya kai mata su Hansatu su gaisa, Hansatu ta sha mamakin jin duk abinda ke faruwa a bakin mahaifiyar ta, ace duk wadannan abubuwan na faruwa bata sani ba? Haka ta dinga yaqe ta na yabawa Isah ,tare da yanka qarya kala kala, dan ta kare shi, yaran ta na ta mamakin qaryar da take ta shinfidawa.
Ba daban ta basu tarbiyya mai kyau ba, tabbas da sun tona mata asiri, dan kuwa ba su so ta rufa masa asiri ba.
Sun jima su na kallon juna kafin Sultana ta yi qarfin halin cewa,
"Why? Me yasa? Me ya sa za ka tafi a lokacin da zuciya ta, ta amince, ta yarda, ta kuma gamsu da ta kamu da matsanancin ciwon son ka? Me ya sa ka tafi, a lokacin da nake tsananin buqatar ka, ka kuwa san ya nake ji a nan dina? (Ta sanya hannu, ta nuna saitin zuciyar ta, cikin kuka,) ba zaka gane ba, saboda baka san me ne ne soyayya ba ga dukkan alamu,"
Cikin sauri ya dakatar da ita, dan kalaman ta na sake harzuqa zuciyar shi, ta na hango masa mugunta kala kala.
Cikin cije lebunan shi a cikin bakin shi ya shafa kan shi, da hannu daya, sannan ya ce,
"Sultana, ba ke dai ka jin duk abinda kin ka lissahwa ba, ni ma ina ji dika, wataqila har da dori ma, amma sultana ba ke d'aya zuciya ta ke so ba, qauna ta ita ce rayuwa ta, ban da komai banda kowa sama da ita,ita kad'ai ce gata na a duk qasar ga, ba mai so na tsakani da Allah, sama da ita, a yanzu haka ji na nake kamar duk duniya sun juyan baya, ni kadai ne, ban da kowa banda komai,"
"Wait a minute,me ya samu Mubaraka?"
A cikin tashin hankali Sultana ta masa wannan tambayar, a cikin qasa da minti bakwai ya bayyana mata me ya faru dangane da batan ta,da kuma irin neman da yake mata, bai samu ba.
Cikin kuka Sultana ta juya ta rufe bakin ta, ta jima a haka ta na kuka, Lawwali ma ji ya ke kamar ya yi kukan, sai daga baya ta juya gare shi, ta na share hawayen ta, motar ta ta fara budewa zata shiga,sannan ta ce,
"Mu je gida Daddy na nan yau, mu sanar da shi,a sanya neman ta, duk inda ta shiga, i love her, she is a gud gurl, I can't let anything happen to her, she is like a sister to me, mu je gida Auwal, maza shiga mota mu je,"
Kallon gidan su ya yi, cikin takaici, ya na jiyo muryoyin mata ana ta zabga hira, ya ji haushi da be shiga ya tarwatsa su ba, qanwar shi ta bata amma suke hira haka ana dariya har waje ana ji, ya so ya shiga ya gan su, da duk sai ya musu rashin mutunci d'aya bayan d'ayan su, amma ba komai next time.
Kwafa ya yi, ya shige motar shi, ya bi ta su Sultana.
*************************
Gwamna Halliru na ganawa da su No 1 da 4, su na tattaunawa akan yanda Lawwali ya haukace.
Sultana ta je za ta shiga parlour wasu masu tsaron wajen ne suka dakatar da ita, tare da sanar da ita cewar Gwamna ya ce kar a bawa Kowa damar shiga, sai da izinin shi, d'aya daga cikin su ta kalla tace,
"Ka je ka sanar da shi ni ce, na ke son magana da shi, ya na da mahimmanci na gan shi yanzu"
Har security din zai tafi, Lawwali ya qarasa shiga wajen, su na hada ido, security ya ja baya, tare da fadin,
"Ran ka ya dade Oga, Barka da zuwa"
"Gwauna hwa? "
"Shi na ciki Oga"
Mamaki ne danqare a cikin Sultana, an hana ta shiga amma an budewa Lawwali ya shige,me kenan? Lawwali ya fi ta matsayi a gidan Uban ta kenan?
Ko da suka shiga shiru wajen ya dauka, ba No 4 da ake tausa ba, ana nuna masa ba abinda Lawwali zai yi, as long as bai gane ina qanwar shi take ba, har Gwamnan kan shi sai da hankalin shi ya tashi ainun.
Cikin rawar murya, No 4 ya ce,
"O....ogaa, kai ne da rana haka?"
Lawwali ko kallon No 4 be ba, ya samu kujera ya zauna, tare da harde qafa,No 1 ne ya je ya tsaya a daf da shi,hakan kamar girmamawa ne a gare shi, No1 na ta hararar No 4 tare da yi masa nunin ya nutsu, Sultana kuwa mamakin abinda take gani ya fi qarfin ta, waje ta samu ta tsaya, ta na kallon yanda mahaifin ta ya yi lakwas a gaban Lawwali, bai magana ba akan zaman da Lawwali ya yi a gaban shi .
"Oga har yanzu fa shiru,yanzu haka mun kawo maganar ne wajen Excelency saboda a bamu taimako"
"Mu ma abinda ya kawo mu kenan,na yi iya qoqari na na kasa, ina neman taimako a hukumance, a bido min qauna ta, in ba haka ba,....."
Shiru ya yi, ya taune leben bakin shi na qasa, tare da dukan tafin qafar shi da ya dora a saman dayar qafar tashi.
"Ah ah Sultana, mik-kawo ki nan?"
"Tare muke,"
"Ban gane tare kuke ba, qaqa an kai kuke tare?"
"Dad Mubaraka ce ba a gani ba, kusan sati Uku yanzu, shi ne na rako shi neman taimako wajen ka, amma yanzu na kula is like, ni anka rako, ko wani zai iya min bayani akan abubuwan da nake gani a yanzu?"
Da sauri gwamna ya zari wayar shi, ya kira Head quarter na yan sanda, ya fara bada report din batan Mubaraka, Sultana tuni ta manta da tambayar da take yi, ita da Lawwali sun bawa Gwamna hankulan su.
Wayar aka bawa Lawwali ya yi kwatancen ta,da bayanin ranar da suka nemeta suka rasa, tare da alqawarin ze tura hotunan ta.
Godiya ya miqe sosai ya na wa gwamna, Sultana ma haka.
Gwamna na son bin su ya ji dalilin da ya sa suke a tare, kuma ya na son magana da su No 1, dan haka sai da ya bari su Lawwali sun fita, sannan ya qara jaddada musu su yi taka tsantsan ta yanda asirin su ba zai tonu ba, domin in Lawwali ya san sun sace qanwar shi, har shi kan shi ba zai tsira ba, ballantana su.
Wannan kalamai sun sake birkita No 4, da kyar yake hadiyar yawu, zufa sai karyo masa take, a sati ukun nan, duk 'yar qibar ma da ya yi, saboda kudin da suke samu, duk ta zabge, ya fita hayyacin shi, ba wani kwanciyar hankali a tattare da shi.
Su Sultana kuwa a jikin motar shi, suka tsaya, su na magana, hira ce mai dadi,ta yaushe gamo suke yi, kusan kaso saba'in na hirar dukkan su akan Mubaraka su ke yi, Sultana na son mubaraka, ba wai dan ta na qanwar Lawwali ba,ah ah, yarinyar abar so ce ga duk mai hankali.
Shi kuwa a wajen shi Mubaraka ita ce rayuwar shi, a ganin shi ma ba zai taba samun kan Sultana ba in bata nan.
Bayan sun yi sallama za su tafi ne Sultana ta ce,
"Haka ake sallama da masoyi? "
Kallon yanda ta maida kai gefe ta yi, sai ta masa kyau, murmushi ya yi, kadan, wanda rabon shi da murmushi na gaskiya, ba na mugunta ba, tun kafin batan Mubarakan.
"Ya ya kamata masoyi ya yi sallama ?"
Dan rufe fuskar ta tayi da hannun ta kadan ta ce,
"Kamata ya yi ka ce, Sultana na tafi, zan dawo anjima, ina son ki"
Bude baki Lawwali ya yi, ya na dariya mai sassanyan sauti, ya ce,
"Kaiii ka kaiii ka kaiii, Baraka na ta ce man ke ustaziya ta wallah, ashe ke iya soyayya haka?"
Mayafin ta ta ja sosai ta rufe fuska sannan ta ce,
"To ai soyayya kowa na yi"
"Ok, to sultana Ina son ki,"
Wani irin dad'i ne ya ziyarce ta, musamman da ta kalle shi ta ga babu wasa a kalaman shi, iyakar gaskiyar shi yake fada, ta ji sautin Muryar shi, ba alamar gatse ko wasa, amayar da ta ta zuciyar ta ce,
"Auwal ina son ka, In na ce ina son ka, ba ina nufin ina son ka fiye da yanda kk so na bane, ina nufin ina son ka a kowanne hali, ina son ka ko da wani sabani ya haɗa mu, ina son ka ko da ka na cikin damuwar da ta sa ka nesanta da ni, ina son ka sama da nisan nan da ke tsakanin mu,ina son ka sama da yanda na ke jin zafin rashin ka a rai na, ina son ka sama da dukkan wani abu da zai qoqarin shiga tsakanin mu, ina nufin nafi son ka Auwal"
Ya Salam, Lawwali ya gama narkewa,kalaman sultana sun wanke masa wani kaso na baqin cikin da ke ran shi,dama haka take fata, shi ne dalilin da ya sanya ta cire kunya ta furta abinda ke ran ta, sai bayan ta gama kashe masa gabban jikin shi, ta juya da gudu gudu ta shige gida,dan kuwa kunyar shi ba zata bar ta ta tsaya jin me zai ce ba again.
Lawwali ya jima a wajen, kafin ya shiga motar shi, ya tada ya bar gidan.
Su No 1 kuwa ya na fita suma suka bar gidan, dan zuwa sauyawa su Mubaraka maboya kamar yanda Gwamna ya bada shawara, da kuma wajen zama.
Lawwali har ya isa gida bai dena murmushi ba, ya jima ya na dirzar dattin jikin shi,kafin ya samu abinci ya ci rabon shi da abinci sosai kamar na ranar ba zai iya fadin ga lokacin ba.
Ya na kammalawa ya kwanta, dan hutawa.
**********************
Vissa ta samu, na tafiyar Isah Saudiya, ana sauran kwana biyu tafiyar Isa, Hajiya ta sa Isan ya kai mata su Hansatu su gaisa, Hansatu ta sha mamakin jin duk abinda ke faruwa a bakin mahaifiyar ta, ace duk wadannan abubuwan na faruwa bata sani ba? Haka ta dinga yaqe ta na yabawa Isah ,tare da yanka qarya kala kala, dan ta kare shi, yaran ta na ta mamakin qaryar da take ta shinfidawa.
Ba daban ta basu tarbiyya mai kyau ba, tabbas da sun tona mata asiri, dan kuwa ba su so ta rufa masa asiri ba.