Sashe 15
A Garin Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Daga Hajiya har Yayahn ba wanda ya tanka, kunya ce ma ta kama su, suka hau yi ma su Amina wasa, murmushin yaqe Hansatu kawai take yi, lallai matar yayan ta batta da mutunci da dukkan alamu.
Kafin wani lokaci qanqani an cika dinning table da abinci kala kala, qamshin shi ya sanya yunwar cikin su motsawa, ta yanda har ana iya jiyo kukan yunwar ta na neman agaji, cikin wasa Hajiya ta ce,
"Wayyyooo wayyoo ni yunwa taa, yi hakuri bari kuka haka nan, yanzun ga zan baki abinci ki tafi"
Dariya su Ahmad sukai ta yi, ta na riqe da hannun Bilkisu da Ahmad Amina na biye da ita suka zauna a kan kujerun table din, plates ta sawa kowa a gaban shi, ta na tambayar su me za su ci, da sauri Hansatu ta isa ta karba ta na zuba masu hawaye na zubar mata, mahaifin ta ta tuna, a baya in ta na zuba masa abinci, ya na mata wasa, tare da sanya mata albarka.
Dafa kan ta Hajiya ta yi ta ce,
"Allah ya miki albarka, ki kasance cikin farin ciki har qarshen rayuwar ki"
"Ameeen Hajiya ta"
Isa ya gama qulewa, sun tafi sun bar shi, yunwa sai narkar masa da tumbi take, ko ta ma waiga ta kalle shi, balle ya mata alama, kwafa ya yi a hankali, sannan ya furta,
"Za mu je gida ne"
Yayah ne ya kama hannun shi, ya ce,
"Suruki na mu je mu ci abinci,"
A zaqe Isa ya miqe, ya na zama kuwa, kazar da ke gaban Hansatu ce ta tsone masa ido, to ta riga ta san halin gogan nata, dauka ta yi ta mayar plate din gaban shi, da murmushin yaqe,
"Ah ah, Hafsat ci naki mana, ga wani nan zuba masa,"
Isa maida hannun shi baya ya yi, da har zai kaiwa kazar damqa, hansatu da ta san halin mijin ta, cika masa plate ta yi d kyau, kusan duk abinda ke kan table din sai da ta sa masa,ba kunya ba tsoro, ba godiya haka ya fara ci, su Amina sun jima da fara cin abincin su.
Shiru ka ke ji, banda qarar cokula da taunar Isa ba ka jin komai, hakan kuwa ba qaramin bata ran Aziza ya yi ba, cin abinci kamar wani akuya, dan tsaki ta ja, sannan ta ce,
"Haka ka ke cin abinci?"
Kafe Isa ta yi da ido, ta na yatsina fuska, cike da nuna kyankyamin shi, dan murmushin yaqe ya sakar mata, ya ci gaba da cin abincin shi, da qarfi ta daki table din, sai da yaran suka razana, ta ja kujera baya, ta bar wajen.
Ta na tafe ta na masifa da harshen turanci.
"Ku yi hakuri da halin Azizah, in baki manta ba, akwai wanda muka zaba Maki ki aura a baya, qanwar shi ce, yanzu haka su na da hannun jari mafi yawa a kamfanin mu, yayan nata ke riqe da kamfanin, mutumin kirki ne matuqa, amma Aziza dake renon qasar waje ce, tarbiyyar ta da tamu ta bambamta, a haka ta fara barin wasu munanan halayen mutanen can, ku ci abincin ku, ku rabu da ita, a qasan ran ta, mutuniyar kirki ce, ba ko da yaushe take haka ba"
"Ba bu komai Hajiya,Allah ya sa ta gyara halayen ta gaba daya, domin ku ci gaba da jin dadin zama da ita"
"Ameeen" shi ne abinda yayan ta ya riga kowa fadi, ya na mutuwar son Aziza, amma halayen ta na baqanta ran shi.
Bayan kammala cin abincin su ne, Bilkisu ta ga Hajiya ta goge bakin ta da tissue ta ɗora a kan ragowar abincin ta, ga qashin da ta ci ta tauna duk ta zuba a sauran abincin, tashi ta yi tsam ta dauke, sannan ta kalli Hansatu ta ce,
"Umma ai dai ba kyau wulakanta abinci ko? Hajiya ki dena bata abincin da kika rage, kar watarana ki rasa abinda za ki ci, Umma bari na samo leda mu qulle sauran mun dumama gobe"
Kunya ce ta kama Hansatu matuqa, Hajiya kuwa da Yayah yi sukai kamar ba su ji me Bilkisu ta ce ba, kwashe wanda suka zuba a saman plate din suka yi kawai, suka tara a wani empty mazubi dake wajen,
"In Allah ya yarda daga yau ba zaku sake zama da yunwa ba kunji?"
Daga kai yaran sukai suna kallon Uncle din nasu cikin farin ciki.
Basu suka fara shirin komawa gidan su ba, sai bayan isha'i,Hajiya ta haɗa masu ashirin ta arziki,dan kuwa sai da bayan mota ya qi rufuwa.
Kayan sawa ne, na Hansatu da yaran, da na Isa kan shi, Isa kuwa bayan sabbi shi da Hansatu har da kwance na Yayah da Aziza da Hajiya suka samu, yaran ne kawai aka sai masu sabbi tun kan su je.
Har qofar gida motar ta tsaya, Yabbuga na jin qarar mota ta diba da gudu ta labe a zaure, ta na leqen su, Dan Jumma kuwa mamaki ya gama kashe shi,gulmar ta ta har ta kai, su na tsaka da hirar su ta zabura ta yi waje haka?
Sai da ta gama ganin kayan da Isa ya shigar shi da Hansatu sannan ta koma ta labe a katanga, daidai inda ta kan ji maganar su, ta na tsaye ta ji maganar Isa,
"Bubbude mu ga meye a ciki, dan iskanci shi ne dazu ku ka tafi cin abinci kuka bar ni zaune ga dan iska, na je gidan su Mata ta cin azziqi ko?"
"Ka yi hakuri ba haka bane"
"Dalla Malama bude naga me aka saka a ciki,"
Ganin abun azziqin ne ya yi yawa, nan da nan ya fara washe baki, ya na zuba, har zama ya samu waje ya yi, ya na ma Hansatu hira, mamaki ya gama kashe ta.
Ranar Isa sai da ya gwada mata soyayyar da suka dade ba su yi irin ta ba.
Ta ji dadin hakan matuqa, addu'a ta dinga yi Allah ya tabbatar da su cikin azziqi mai albarka.
Yabbuga kuwa ta nade komai jira take washe gari ta yi ta guntsawa qawayen ta na gulma, duk yanda ta so ta yi maganar abu da Dan jumma ya qi bata hadin kai, tai ta Masifa ita daya, har bacci ya dauke ta.........
Sai mu jira uwar gulma ta tashi daga kwana😅
💅🏻 *A GARIN MU* 💅🏻
WRITTEN BY HAERMEEBRAERH
PAGE 16:
Da misalin 8:12am, Yabbuga na tsaye a qofar dakin Hansatu, riqe da jug din da ta ciko shi da wani tsinkakken kunun da ta tsulawa ruwan zafi, sai sallama take wage baki ta na dokawa, Isah ne ya fito ya na miqa, rigar shi a kafada, ko kauda ido Yabbuga ba ta yi ba, ta fara gaida shi ,
"Ango na Hansatu, an kwan lahiya?"
"Lahiya lau, qaqa an kayi yau kittaho gidan ga da swahiya haka?"
"Ohhh ni Yabbugan Dan jumma abin arziqi dai be amshi kare ba, wagga tambaya awab-ba a son zuwa na?"
"Ni ban ce ba, na ga dai ba ki saba taho wa da sahe ba, Ni rabo na ma da na gane ki gidan ga na mance"
Sai a sannan kunya ta kama Yabbuga.
"Yo jiya ina zaune na kunna gidan redio nijji Mallam na wa'azi akan zama da maqwacci lhiya, shi na nicce bari mu gyara, rayuwar ga ba tabbas"
Isah dai kurkure bakin shi ya yi, ya fice.
Hansatu ce ta qarasa fita tsakar gidan, dan dama ta na tsaye, ta nutsu ta yi shiru ne kar a ce kuma ta yi laifi.
"Barka da sahiya Yabbuga,"
"Barka dai Hansuwa, shin ina 'yan yara ban gane su ba"
"Su na ciki, karatu Ni ka masu, ke san abinda ya hwaru, ina tsoron barin su sake hita,kuma dama basu zuwa boko, to mu na karatu a gida "
"Allah Sarki, tauu ga wanga nikkawo musu, a gasa hanji, ko da dai na ga jiya kun tai gari a mota,"
Cikin dariyar son jin gulma ta yi maganar, Hansatu murmushi ta yi ya karba, ta na godiya, a zaton ta Yabbuga tafiya za ta yi, sai ta ga ta na qoqarin binta ciki, kasa hana ta shiga ta yi, suka shiga ciki, kayan da Yabbuga ta gani jibge sun so tsorata ta, amma ta dake,
"Ah ahhh wanga abin arziqi hwa, daga ina?"
Murmushi kawai Hansatu ta yi, ta nemi tsohuwar tabarmar ta ta shimfidawa Yabbuga, tunda suke a unguwar wannan shi ne zuwan Yabbuga na Shida har ta zauna a dakin ta.
Tun ta na farko farkon zuwa, lokacin ta na da abubuwa,sai kuma yau.
Abu kamar a mafarki kawai Hansatu gani ta yi yabbuga na bude buhuna ta na leqawa, mamaki ma ya hana Hansatu magana, Ita kuwa ta na budewa ta na Suratu, tare da yaba abubuwan da ta gani.
Isah ne ya shigo, tare da fadin,
"Ku jira Ni ina zuwa,"
Dakin ya fada ba ko sallama, Yabbuga kuwa qamewa ta yi a gefe, dan tun da ta ji Muryar Isah ta daina leqen buhunan.
"Ke miqon wannan buhun da na ware jiya,"
"To"
Shi ne kawai abinda Hansatu ta ce,gashi ga buhun ya dauka amma ba zai dauka ba sai ya sata aiki.
Da kyar ta ke jan buhun, ta kai waje, kayan abinci ne danqare a ciki, da suturu masu tsada, ya tattare, a cewar shi ba ya so su saba da abin duniya ,shi kuwa ba shi gare shi ba, kuma da iyayen ta suka tula musu kayan abinci ba na cefane da shekarun shi zai sai kayan miya?
Maza ne a tsakar gidan guda uku, daya mai gwanjo ne, daya mai shago ne, daya mai sai da kayan abinci ne na awo.
Sai da Hansatu ta fitar da buhu uku, sanan ta koma ta na maida numfashin baqin ciki, da gajiya.
Ta na tsaye ya gama siyar da komai, aka bashi kudin ya kalmasa a aljihu.
Ya kalli Hansatu da ke tsaye ,
"An jima ki dafa taliya, mun kwana biyu ba mu ci ta ba, kwai ragowar manjan nan ko? Ki soya, ga hamsin a siyo yaji, wannan ashirin din ki sai Maggi, kin San taliya da manja akwai dad'i,se na dawo"
Kafin wani lokaci qanqani an cika dinning table da abinci kala kala, qamshin shi ya sanya yunwar cikin su motsawa, ta yanda har ana iya jiyo kukan yunwar ta na neman agaji, cikin wasa Hajiya ta ce,
"Wayyyooo wayyoo ni yunwa taa, yi hakuri bari kuka haka nan, yanzun ga zan baki abinci ki tafi"
Dariya su Ahmad sukai ta yi, ta na riqe da hannun Bilkisu da Ahmad Amina na biye da ita suka zauna a kan kujerun table din, plates ta sawa kowa a gaban shi, ta na tambayar su me za su ci, da sauri Hansatu ta isa ta karba ta na zuba masu hawaye na zubar mata, mahaifin ta ta tuna, a baya in ta na zuba masa abinci, ya na mata wasa, tare da sanya mata albarka.
Dafa kan ta Hajiya ta yi ta ce,
"Allah ya miki albarka, ki kasance cikin farin ciki har qarshen rayuwar ki"
"Ameeen Hajiya ta"
Isa ya gama qulewa, sun tafi sun bar shi, yunwa sai narkar masa da tumbi take, ko ta ma waiga ta kalle shi, balle ya mata alama, kwafa ya yi a hankali, sannan ya furta,
"Za mu je gida ne"
Yayah ne ya kama hannun shi, ya ce,
"Suruki na mu je mu ci abinci,"
A zaqe Isa ya miqe, ya na zama kuwa, kazar da ke gaban Hansatu ce ta tsone masa ido, to ta riga ta san halin gogan nata, dauka ta yi ta mayar plate din gaban shi, da murmushin yaqe,
"Ah ah, Hafsat ci naki mana, ga wani nan zuba masa,"
Isa maida hannun shi baya ya yi, da har zai kaiwa kazar damqa, hansatu da ta san halin mijin ta, cika masa plate ta yi d kyau, kusan duk abinda ke kan table din sai da ta sa masa,ba kunya ba tsoro, ba godiya haka ya fara ci, su Amina sun jima da fara cin abincin su.
Shiru ka ke ji, banda qarar cokula da taunar Isa ba ka jin komai, hakan kuwa ba qaramin bata ran Aziza ya yi ba, cin abinci kamar wani akuya, dan tsaki ta ja, sannan ta ce,
"Haka ka ke cin abinci?"
Kafe Isa ta yi da ido, ta na yatsina fuska, cike da nuna kyankyamin shi, dan murmushin yaqe ya sakar mata, ya ci gaba da cin abincin shi, da qarfi ta daki table din, sai da yaran suka razana, ta ja kujera baya, ta bar wajen.
Ta na tafe ta na masifa da harshen turanci.
"Ku yi hakuri da halin Azizah, in baki manta ba, akwai wanda muka zaba Maki ki aura a baya, qanwar shi ce, yanzu haka su na da hannun jari mafi yawa a kamfanin mu, yayan nata ke riqe da kamfanin, mutumin kirki ne matuqa, amma Aziza dake renon qasar waje ce, tarbiyyar ta da tamu ta bambamta, a haka ta fara barin wasu munanan halayen mutanen can, ku ci abincin ku, ku rabu da ita, a qasan ran ta, mutuniyar kirki ce, ba ko da yaushe take haka ba"
"Ba bu komai Hajiya,Allah ya sa ta gyara halayen ta gaba daya, domin ku ci gaba da jin dadin zama da ita"
"Ameeen" shi ne abinda yayan ta ya riga kowa fadi, ya na mutuwar son Aziza, amma halayen ta na baqanta ran shi.
Bayan kammala cin abincin su ne, Bilkisu ta ga Hajiya ta goge bakin ta da tissue ta ɗora a kan ragowar abincin ta, ga qashin da ta ci ta tauna duk ta zuba a sauran abincin, tashi ta yi tsam ta dauke, sannan ta kalli Hansatu ta ce,
"Umma ai dai ba kyau wulakanta abinci ko? Hajiya ki dena bata abincin da kika rage, kar watarana ki rasa abinda za ki ci, Umma bari na samo leda mu qulle sauran mun dumama gobe"
Kunya ce ta kama Hansatu matuqa, Hajiya kuwa da Yayah yi sukai kamar ba su ji me Bilkisu ta ce ba, kwashe wanda suka zuba a saman plate din suka yi kawai, suka tara a wani empty mazubi dake wajen,
"In Allah ya yarda daga yau ba zaku sake zama da yunwa ba kunji?"
Daga kai yaran sukai suna kallon Uncle din nasu cikin farin ciki.
Basu suka fara shirin komawa gidan su ba, sai bayan isha'i,Hajiya ta haɗa masu ashirin ta arziki,dan kuwa sai da bayan mota ya qi rufuwa.
Kayan sawa ne, na Hansatu da yaran, da na Isa kan shi, Isa kuwa bayan sabbi shi da Hansatu har da kwance na Yayah da Aziza da Hajiya suka samu, yaran ne kawai aka sai masu sabbi tun kan su je.
Har qofar gida motar ta tsaya, Yabbuga na jin qarar mota ta diba da gudu ta labe a zaure, ta na leqen su, Dan Jumma kuwa mamaki ya gama kashe shi,gulmar ta ta har ta kai, su na tsaka da hirar su ta zabura ta yi waje haka?
Sai da ta gama ganin kayan da Isa ya shigar shi da Hansatu sannan ta koma ta labe a katanga, daidai inda ta kan ji maganar su, ta na tsaye ta ji maganar Isa,
"Bubbude mu ga meye a ciki, dan iskanci shi ne dazu ku ka tafi cin abinci kuka bar ni zaune ga dan iska, na je gidan su Mata ta cin azziqi ko?"
"Ka yi hakuri ba haka bane"
"Dalla Malama bude naga me aka saka a ciki,"
Ganin abun azziqin ne ya yi yawa, nan da nan ya fara washe baki, ya na zuba, har zama ya samu waje ya yi, ya na ma Hansatu hira, mamaki ya gama kashe ta.
Ranar Isa sai da ya gwada mata soyayyar da suka dade ba su yi irin ta ba.
Ta ji dadin hakan matuqa, addu'a ta dinga yi Allah ya tabbatar da su cikin azziqi mai albarka.
Yabbuga kuwa ta nade komai jira take washe gari ta yi ta guntsawa qawayen ta na gulma, duk yanda ta so ta yi maganar abu da Dan jumma ya qi bata hadin kai, tai ta Masifa ita daya, har bacci ya dauke ta.........
Sai mu jira uwar gulma ta tashi daga kwana😅
💅🏻 *A GARIN MU* 💅🏻
WRITTEN BY HAERMEEBRAERH
PAGE 16:
Da misalin 8:12am, Yabbuga na tsaye a qofar dakin Hansatu, riqe da jug din da ta ciko shi da wani tsinkakken kunun da ta tsulawa ruwan zafi, sai sallama take wage baki ta na dokawa, Isah ne ya fito ya na miqa, rigar shi a kafada, ko kauda ido Yabbuga ba ta yi ba, ta fara gaida shi ,
"Ango na Hansatu, an kwan lahiya?"
"Lahiya lau, qaqa an kayi yau kittaho gidan ga da swahiya haka?"
"Ohhh ni Yabbugan Dan jumma abin arziqi dai be amshi kare ba, wagga tambaya awab-ba a son zuwa na?"
"Ni ban ce ba, na ga dai ba ki saba taho wa da sahe ba, Ni rabo na ma da na gane ki gidan ga na mance"
Sai a sannan kunya ta kama Yabbuga.
"Yo jiya ina zaune na kunna gidan redio nijji Mallam na wa'azi akan zama da maqwacci lhiya, shi na nicce bari mu gyara, rayuwar ga ba tabbas"
Isah dai kurkure bakin shi ya yi, ya fice.
Hansatu ce ta qarasa fita tsakar gidan, dan dama ta na tsaye, ta nutsu ta yi shiru ne kar a ce kuma ta yi laifi.
"Barka da sahiya Yabbuga,"
"Barka dai Hansuwa, shin ina 'yan yara ban gane su ba"
"Su na ciki, karatu Ni ka masu, ke san abinda ya hwaru, ina tsoron barin su sake hita,kuma dama basu zuwa boko, to mu na karatu a gida "
"Allah Sarki, tauu ga wanga nikkawo musu, a gasa hanji, ko da dai na ga jiya kun tai gari a mota,"
Cikin dariyar son jin gulma ta yi maganar, Hansatu murmushi ta yi ya karba, ta na godiya, a zaton ta Yabbuga tafiya za ta yi, sai ta ga ta na qoqarin binta ciki, kasa hana ta shiga ta yi, suka shiga ciki, kayan da Yabbuga ta gani jibge sun so tsorata ta, amma ta dake,
"Ah ahhh wanga abin arziqi hwa, daga ina?"
Murmushi kawai Hansatu ta yi, ta nemi tsohuwar tabarmar ta ta shimfidawa Yabbuga, tunda suke a unguwar wannan shi ne zuwan Yabbuga na Shida har ta zauna a dakin ta.
Tun ta na farko farkon zuwa, lokacin ta na da abubuwa,sai kuma yau.
Abu kamar a mafarki kawai Hansatu gani ta yi yabbuga na bude buhuna ta na leqawa, mamaki ma ya hana Hansatu magana, Ita kuwa ta na budewa ta na Suratu, tare da yaba abubuwan da ta gani.
Isah ne ya shigo, tare da fadin,
"Ku jira Ni ina zuwa,"
Dakin ya fada ba ko sallama, Yabbuga kuwa qamewa ta yi a gefe, dan tun da ta ji Muryar Isah ta daina leqen buhunan.
"Ke miqon wannan buhun da na ware jiya,"
"To"
Shi ne kawai abinda Hansatu ta ce,gashi ga buhun ya dauka amma ba zai dauka ba sai ya sata aiki.
Da kyar ta ke jan buhun, ta kai waje, kayan abinci ne danqare a ciki, da suturu masu tsada, ya tattare, a cewar shi ba ya so su saba da abin duniya ,shi kuwa ba shi gare shi ba, kuma da iyayen ta suka tula musu kayan abinci ba na cefane da shekarun shi zai sai kayan miya?
Maza ne a tsakar gidan guda uku, daya mai gwanjo ne, daya mai shago ne, daya mai sai da kayan abinci ne na awo.
Sai da Hansatu ta fitar da buhu uku, sanan ta koma ta na maida numfashin baqin ciki, da gajiya.
Ta na tsaye ya gama siyar da komai, aka bashi kudin ya kalmasa a aljihu.
Ya kalli Hansatu da ke tsaye ,
"An jima ki dafa taliya, mun kwana biyu ba mu ci ta ba, kwai ragowar manjan nan ko? Ki soya, ga hamsin a siyo yaji, wannan ashirin din ki sai Maggi, kin San taliya da manja akwai dad'i,se na dawo"