Sashe 47
A Garin Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Cikin tsananin hawaye ya juya ya nufi motar shi, tunda yake a rayuwar shi yau ce rana ta farko da ya yi addu'a ya roqi Allah wani abu da kyakkyawar zuciya.
"Ya Allah ka kare min qauna ta, Allah ka san wad-da ni ka son ta, Allah duk inda take ka zama gatan ta ba na kusa balle na bata kariya, Allah ka kare min ita, kai na mai kare bayin ka a duk inda suke, Mubaraka bata da lehin komi, Allah ka sani komai ke faruwa laihi na ne, kar ka hukunta qauna ta da lehi na"
Ya jima zaune a motar idanun shi sun yi jawur saboda kuka, time ya kalla ya ga bakwai da rabi, cikin sauri ya nufi gida kafin ya isa takwas ta wuce, wanka ya fada, ya yi a gaggauce, ya na shiryawa wayar shi na ringing bai dauka ba dan ya san ko waye.
Sai da ya gama shiri tsaf, ya ci abinci sannan ya fesa turarukan shi masu qamshi mai dad'i, sannan ya samu yaran shi da ke gidan ya sallame su, tare da basu umarnin komawa can sansanin su.
Ya na tafiya kan ya isa gidan Gwamna ya yi waya da wanda ya bawa tsaron No 1 ya ji ya suke, sun sanar da shi duk irin abinda ya ce su yi ba wanda ba su aikata ba, ya na nan ya na jin jiki, murmushin jin dadi ya yi, sannan ya kashe wayar shi.
Ran shi fess ya shiga gidan, a qalla ya sauke manyan nauyin da suke kan shi, saura na gaba.
A tsaye ya gan ta, ta na ta safa da marwa, hankalin ta a tashe, siririyar dariya ya saki, dan kuwa ya san sai ta masa shagwabar ta, akan dad'ewar da ya yi, ta bayan ta ya ja ya tsaya, tare da kama kunnuwan shi, qamshin shi ne ya sanya ta tsayawa cak dan kuwa ta san ya iso kenan.
Cike da shawagabar kuwa ta juya, ta langwabe kan ta gefe daya, ta na kallon shi da wani irin sassanyan kallon da ya sa jikin shi mutuwa.
"Me ya sa ka ke min haka? Ka na so zuciya ta ta buga ko?"
"Tabdi, ashe dama zuciyar ki bata bugawa? To da inji ne a jikin ki ki ke amfani da shi?"
Cikin kama haba da kallon ta a karkace yake maganar, hakan da ya yi ba karamin dariya ya sanya ta ba,ai kuwa dariya ta dinga yi, shi ma ya na taya ta, kallon yanda fuskar ta ke sheqi da walqiya yake ta yi, a hankali ya furta,
"Sultana ke kyakkyawa ce, fuskar ki na sheqi kamar hasken farin wata, zan so ki kasace cikin hwarin ciki har qarshen rayuwar ki"
A hankali ta daina dariyar ta ɗan sunkuyar da kan ta, ta na murmushi,
"Ameeen Allah ya sa, amma ka dena zuga kyau na, duk yadda ka ke ganin kyau na, naka ya wuce nawa,"
Kama baki ya sake yi, sanan ya ce,
"Ran ki shi dade mu bar wagga magana, namiji ina yaga kyawu? Namiji iri na dan talakawa taya zai zama mai kyau?kyau ai shi na wajen ku diyan masu kuddi, mai da sabulu da komi da kuka amfani da shi daban ne da namu,"
Ran Sultana ya baci da kalaman shi, ya kuma kula da hakan, dan haka sassanyar dariya ya yi, ya ce
"Yi hankuri wasa ta nikai, dama dan in ga kin turo dan karamin bakin nan na ki"
Murguda masa bakin ta yi, ta wuce jikin mota ta na murmushi.
Hajiya Ikee na tsaye a jikin window ta na kallon su, Lawwali ne ya daga kai ya kashe mata ido daya tare da dora yatsun shi biyu a gefen goshin shi, ya yi saluting din ta ya bi sultana, da sauri ta saki labulen ta yi baya.
"Dan banzan Yaron nan dama ya na gani na?"
Hannun ta ta kalla da ya kumbura ta inda ya matsa mata jiyan, ta saka qanqara ta saka ruwan dumi ta gasa har yanzu ciwo yake mata.
Bari zai ci qaniyar shi duk sanda Gwamna Halliru ya dawo daga tafiya, yaron shi zai ara mata a je har gida a kashe mata shi, in ba ya duniyar gaba daya ta ga yanda zai auri sultana.
Bari ma zata yi maganin shi da kan ta ba sai ta jira gwamna ba.
*************************
Sun isa cikin garin Kano da misalin qarfe uku na rana, a unguwar 'Yan kaba anan Lawwali ya sai masu gida mai kyau, da gate, matar Taheer mai suna Fateema nutuniyar kirki ce, ita da mahaifiyar shi,su na ce mata Goggo Larai, sai yaran shi biyu ,Nusaiba da Hamdiyya.
Da addu'a dauke da bakin su ta neman tsari daga sharrin shaidanun aljanu da mutane suka shiga gidan,wata rantsattsiyar mota ce a harabar gidan, Taheer kallon Mubaraka ya yi, ya ce
"Qauna ta wannan gida da mota hwa duk na ki na"
"Yah Taheer namu dai ba nawa ba, kai din a matsayin yaya ka ke a waje na,dan haka abinda na mallaka namu ne duka"
"Allah shi bani ikon sauke nauyin nan Mubaraka"
Mahaifiyar shi da matar shi suka taya su amsawa da Ameen.
Ko da suka shiga ciki abun ya ba mubaraka mamaki, daga waje gidan bai da wani hatsabibin kyau, amma ta ciki ya qayatar da ita matuqa, bayan sun shiga kantamemen parlour mai dauke da dakuna uku, da kitchen da store akwai wata qaramar qofa, Taheer kiran Mubaraka yayi, ya ce ta bi shi .
Dama ita bata wani zo da kaya ba, dan haka bin shi ta yi ziqau ziqau, su na shiga ta ga babban parlour again, da daki biyu, dakunan ya lalleqa ya na mata bayani, kowanne daki akwai bayi ciki, abinci kuwa Fateema ce za ta dinga dafawa ana kawo mata, Lawwali ya yi hani da babbar murya bai yadda ta yi aiki ba, ya bada umarni a kula da ita ne kawai.
"Yah Taheer ban qi ta taku ba, Amma dan Allah a bani su Hamdiyya su dinga taya Ni kwana tsoro nika ji, kuma dan Allah kar a hana ni aiki, in bana aiki rashin lahiya ni kai, jiki na ciwo yakai,"
Yar dariya ya yi, sanan ya ce,
"To mubaraka, ki zanka gyara bangaren ki, shi kenan?"
"Girki hwa? Ni fa ina son girki Yah Taheer"
Cikin shagwaba ta fadi hakan, murmushi kawai yayi, sannan daga baya ya ce,
"Tau wannan kuma sai na yi wa Fateema magana,dan yanda Oga ya min warning har ita da Goggo sai da an ka yi mata warning, in ta aminceee tau sai ku na yi tare"
"Dan Allah ka hwada mata ba komi, Yah Auwal baya gani, kuma ba zan hwada masa ba"
"Tauu ya yi, bari na tai na samo mana abinci"
"Na gode"
Kallon ta ya yi, ya yi murmushi ya fita.
Ya na fita ta zauna sai hawaye.
Yanzu wannan gidan da ace da kudin halal aka same shi ai mutum ya gama more wa, amma da kudin haramun ne, kwata kwata abun bai burge ta ba, amma ba yanda zata yi, yanzu ta samu dama ne da zata duqufa wajen roqon Allah ya shirya mata yayan ta, ya ganar da shi gaskiya, ya bar mummunar dabi'ar shi, yanzu ba lokacin hutu bane, lokaci ne na ibada.
*************************
Da misalin biyu na dare ya ji motsi ya yi yawa a gidan nashi, kamar ana dira ta katanga, da sauri ya kashe fitilar dakin nashi, tsabar kwarewa da fada da kuma zama cikin shirin ko ta kwana ya san inda komai yake a dakin nashi, cikin sanda ya gama d'aukan duk abinda yake buqata.
Qofar dakin ya bud'e a hankali ya leqa parlour ta jikin glass din window ya ke ganin gilmawar mutane, wani waje ya nufa a cikin duhun ya danna wani makunni kamar makunnin wuta, kujera ya samu ya yi zaman shi.
Daya daga cikin mutum ukun da suka haura gidan na Lawwali ne ya kama hannun qofar, da wani dan qaramin qarfe ya na so ya bude qofar da shi, amma sai ya ji wani irin shocking ya kama shi, ya ja hannun shi ya ja inaa ya maqale, ihu ya dinga zabgawa wanda ya sa abokan aikin nashi tsorata kar a kama su, su ka ruga da gudu suka haura katangar suka bar gidan, Lawwali na jin haka ya miqe ya gyara bindigar shi, ya kunna hasken parlour sannan ya kashe wajen da ya danna dazu. Matashin ya fadi yifff a qasa.
Makulli ya sa ya bude qofar parlour ya shigar da matashin sannan ya rufe qofar ya sake danna abinda ke saka shocking in an taba qofar .
Madara Lawwali ya je ya kawo mai sanyi ya ba matashin ya ce ya shanye.
Kamar wanda yake a yunwace, haka ya dinga diddikar madarar nan, ya na gamawa Lawwali ya ce,
"Wa ya aiko ku? In ka yi min qarya a maganar farko sai na fasa kan ka,na san wa ya aiko ku, ina dai son ji na daga bakin ka"
Cikin in ina matashin ya ce,
"Matar gwauna Hajiya Ikeeleema ta wallah, dan Allah ka yi min rai, ban san gidan ka na wanga ba, ta dai bamu adireshi na kawai, tace mu kashe duk wanda shike cikin gidan ga, dan Allah...."
"Ya isa haka nan, ba abinda zan maka, na san ba ka san waje na an ka aiko ka ba, tashi ka zauna, ni zan kwanta gobe da sahe kar na tashi na gan ka gida na, zan manta dana tab'a sanin ka,"
"To Oga, ni yanzu ma in ka min izini tafiya zan yi"
Daga kafada Lawwali ya yi, ya ce,
"Wad-da ka ga dama"
Lawwali kashe shocking din ya yi, ya shige dakin shi ya fada gado ta ruf da ciki.
"Mtsss Hajiyar ga qaramar yar tasha ta wallah, diyan ga zata turo min su kashe ni, ni ta hana min kwana, mtssss"
Pillow ya ja ya rufe kan shi, ya na son ya samu bacci kafin safiya..........
*Allah dai ya biya ogaaaaa*
💅🏻 *A GARIN MU* 💅🏻
BY HAERMEEBRAERH
PAGE 37:
"Ya Allah ka kare min qauna ta, Allah ka san wad-da ni ka son ta, Allah duk inda take ka zama gatan ta ba na kusa balle na bata kariya, Allah ka kare min ita, kai na mai kare bayin ka a duk inda suke, Mubaraka bata da lehin komi, Allah ka sani komai ke faruwa laihi na ne, kar ka hukunta qauna ta da lehi na"
Ya jima zaune a motar idanun shi sun yi jawur saboda kuka, time ya kalla ya ga bakwai da rabi, cikin sauri ya nufi gida kafin ya isa takwas ta wuce, wanka ya fada, ya yi a gaggauce, ya na shiryawa wayar shi na ringing bai dauka ba dan ya san ko waye.
Sai da ya gama shiri tsaf, ya ci abinci sannan ya fesa turarukan shi masu qamshi mai dad'i, sannan ya samu yaran shi da ke gidan ya sallame su, tare da basu umarnin komawa can sansanin su.
Ya na tafiya kan ya isa gidan Gwamna ya yi waya da wanda ya bawa tsaron No 1 ya ji ya suke, sun sanar da shi duk irin abinda ya ce su yi ba wanda ba su aikata ba, ya na nan ya na jin jiki, murmushin jin dadi ya yi, sannan ya kashe wayar shi.
Ran shi fess ya shiga gidan, a qalla ya sauke manyan nauyin da suke kan shi, saura na gaba.
A tsaye ya gan ta, ta na ta safa da marwa, hankalin ta a tashe, siririyar dariya ya saki, dan kuwa ya san sai ta masa shagwabar ta, akan dad'ewar da ya yi, ta bayan ta ya ja ya tsaya, tare da kama kunnuwan shi, qamshin shi ne ya sanya ta tsayawa cak dan kuwa ta san ya iso kenan.
Cike da shawagabar kuwa ta juya, ta langwabe kan ta gefe daya, ta na kallon shi da wani irin sassanyan kallon da ya sa jikin shi mutuwa.
"Me ya sa ka ke min haka? Ka na so zuciya ta ta buga ko?"
"Tabdi, ashe dama zuciyar ki bata bugawa? To da inji ne a jikin ki ki ke amfani da shi?"
Cikin kama haba da kallon ta a karkace yake maganar, hakan da ya yi ba karamin dariya ya sanya ta ba,ai kuwa dariya ta dinga yi, shi ma ya na taya ta, kallon yanda fuskar ta ke sheqi da walqiya yake ta yi, a hankali ya furta,
"Sultana ke kyakkyawa ce, fuskar ki na sheqi kamar hasken farin wata, zan so ki kasace cikin hwarin ciki har qarshen rayuwar ki"
A hankali ta daina dariyar ta ɗan sunkuyar da kan ta, ta na murmushi,
"Ameeen Allah ya sa, amma ka dena zuga kyau na, duk yadda ka ke ganin kyau na, naka ya wuce nawa,"
Kama baki ya sake yi, sanan ya ce,
"Ran ki shi dade mu bar wagga magana, namiji ina yaga kyawu? Namiji iri na dan talakawa taya zai zama mai kyau?kyau ai shi na wajen ku diyan masu kuddi, mai da sabulu da komi da kuka amfani da shi daban ne da namu,"
Ran Sultana ya baci da kalaman shi, ya kuma kula da hakan, dan haka sassanyar dariya ya yi, ya ce
"Yi hankuri wasa ta nikai, dama dan in ga kin turo dan karamin bakin nan na ki"
Murguda masa bakin ta yi, ta wuce jikin mota ta na murmushi.
Hajiya Ikee na tsaye a jikin window ta na kallon su, Lawwali ne ya daga kai ya kashe mata ido daya tare da dora yatsun shi biyu a gefen goshin shi, ya yi saluting din ta ya bi sultana, da sauri ta saki labulen ta yi baya.
"Dan banzan Yaron nan dama ya na gani na?"
Hannun ta ta kalla da ya kumbura ta inda ya matsa mata jiyan, ta saka qanqara ta saka ruwan dumi ta gasa har yanzu ciwo yake mata.
Bari zai ci qaniyar shi duk sanda Gwamna Halliru ya dawo daga tafiya, yaron shi zai ara mata a je har gida a kashe mata shi, in ba ya duniyar gaba daya ta ga yanda zai auri sultana.
Bari ma zata yi maganin shi da kan ta ba sai ta jira gwamna ba.
*************************
Sun isa cikin garin Kano da misalin qarfe uku na rana, a unguwar 'Yan kaba anan Lawwali ya sai masu gida mai kyau, da gate, matar Taheer mai suna Fateema nutuniyar kirki ce, ita da mahaifiyar shi,su na ce mata Goggo Larai, sai yaran shi biyu ,Nusaiba da Hamdiyya.
Da addu'a dauke da bakin su ta neman tsari daga sharrin shaidanun aljanu da mutane suka shiga gidan,wata rantsattsiyar mota ce a harabar gidan, Taheer kallon Mubaraka ya yi, ya ce
"Qauna ta wannan gida da mota hwa duk na ki na"
"Yah Taheer namu dai ba nawa ba, kai din a matsayin yaya ka ke a waje na,dan haka abinda na mallaka namu ne duka"
"Allah shi bani ikon sauke nauyin nan Mubaraka"
Mahaifiyar shi da matar shi suka taya su amsawa da Ameen.
Ko da suka shiga ciki abun ya ba mubaraka mamaki, daga waje gidan bai da wani hatsabibin kyau, amma ta ciki ya qayatar da ita matuqa, bayan sun shiga kantamemen parlour mai dauke da dakuna uku, da kitchen da store akwai wata qaramar qofa, Taheer kiran Mubaraka yayi, ya ce ta bi shi .
Dama ita bata wani zo da kaya ba, dan haka bin shi ta yi ziqau ziqau, su na shiga ta ga babban parlour again, da daki biyu, dakunan ya lalleqa ya na mata bayani, kowanne daki akwai bayi ciki, abinci kuwa Fateema ce za ta dinga dafawa ana kawo mata, Lawwali ya yi hani da babbar murya bai yadda ta yi aiki ba, ya bada umarni a kula da ita ne kawai.
"Yah Taheer ban qi ta taku ba, Amma dan Allah a bani su Hamdiyya su dinga taya Ni kwana tsoro nika ji, kuma dan Allah kar a hana ni aiki, in bana aiki rashin lahiya ni kai, jiki na ciwo yakai,"
Yar dariya ya yi, sanan ya ce,
"To mubaraka, ki zanka gyara bangaren ki, shi kenan?"
"Girki hwa? Ni fa ina son girki Yah Taheer"
Cikin shagwaba ta fadi hakan, murmushi kawai yayi, sannan daga baya ya ce,
"Tau wannan kuma sai na yi wa Fateema magana,dan yanda Oga ya min warning har ita da Goggo sai da an ka yi mata warning, in ta aminceee tau sai ku na yi tare"
"Dan Allah ka hwada mata ba komi, Yah Auwal baya gani, kuma ba zan hwada masa ba"
"Tauu ya yi, bari na tai na samo mana abinci"
"Na gode"
Kallon ta ya yi, ya yi murmushi ya fita.
Ya na fita ta zauna sai hawaye.
Yanzu wannan gidan da ace da kudin halal aka same shi ai mutum ya gama more wa, amma da kudin haramun ne, kwata kwata abun bai burge ta ba, amma ba yanda zata yi, yanzu ta samu dama ne da zata duqufa wajen roqon Allah ya shirya mata yayan ta, ya ganar da shi gaskiya, ya bar mummunar dabi'ar shi, yanzu ba lokacin hutu bane, lokaci ne na ibada.
*************************
Da misalin biyu na dare ya ji motsi ya yi yawa a gidan nashi, kamar ana dira ta katanga, da sauri ya kashe fitilar dakin nashi, tsabar kwarewa da fada da kuma zama cikin shirin ko ta kwana ya san inda komai yake a dakin nashi, cikin sanda ya gama d'aukan duk abinda yake buqata.
Qofar dakin ya bud'e a hankali ya leqa parlour ta jikin glass din window ya ke ganin gilmawar mutane, wani waje ya nufa a cikin duhun ya danna wani makunni kamar makunnin wuta, kujera ya samu ya yi zaman shi.
Daya daga cikin mutum ukun da suka haura gidan na Lawwali ne ya kama hannun qofar, da wani dan qaramin qarfe ya na so ya bude qofar da shi, amma sai ya ji wani irin shocking ya kama shi, ya ja hannun shi ya ja inaa ya maqale, ihu ya dinga zabgawa wanda ya sa abokan aikin nashi tsorata kar a kama su, su ka ruga da gudu suka haura katangar suka bar gidan, Lawwali na jin haka ya miqe ya gyara bindigar shi, ya kunna hasken parlour sannan ya kashe wajen da ya danna dazu. Matashin ya fadi yifff a qasa.
Makulli ya sa ya bude qofar parlour ya shigar da matashin sannan ya rufe qofar ya sake danna abinda ke saka shocking in an taba qofar .
Madara Lawwali ya je ya kawo mai sanyi ya ba matashin ya ce ya shanye.
Kamar wanda yake a yunwace, haka ya dinga diddikar madarar nan, ya na gamawa Lawwali ya ce,
"Wa ya aiko ku? In ka yi min qarya a maganar farko sai na fasa kan ka,na san wa ya aiko ku, ina dai son ji na daga bakin ka"
Cikin in ina matashin ya ce,
"Matar gwauna Hajiya Ikeeleema ta wallah, dan Allah ka yi min rai, ban san gidan ka na wanga ba, ta dai bamu adireshi na kawai, tace mu kashe duk wanda shike cikin gidan ga, dan Allah...."
"Ya isa haka nan, ba abinda zan maka, na san ba ka san waje na an ka aiko ka ba, tashi ka zauna, ni zan kwanta gobe da sahe kar na tashi na gan ka gida na, zan manta dana tab'a sanin ka,"
"To Oga, ni yanzu ma in ka min izini tafiya zan yi"
Daga kafada Lawwali ya yi, ya ce,
"Wad-da ka ga dama"
Lawwali kashe shocking din ya yi, ya shige dakin shi ya fada gado ta ruf da ciki.
"Mtsss Hajiyar ga qaramar yar tasha ta wallah, diyan ga zata turo min su kashe ni, ni ta hana min kwana, mtssss"
Pillow ya ja ya rufe kan shi, ya na son ya samu bacci kafin safiya..........
*Allah dai ya biya ogaaaaa*
💅🏻 *A GARIN MU* 💅🏻
BY HAERMEEBRAERH
PAGE 37: