Sashe 30
A Garin Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Yaqi ake amma a gida na, wannan shegiyar yarinyar ce ta tafi yawo, bata dawo ba, ta ja muna bala'i, hatta da gambun gidan nan bai tsira ba, sai da Yaron nan ya ɗebe shi yau, komi ya hwashe ya lalata, na jiyo ya na fadawa Lamishi gobe in ba a ga Mubaraka ba sai ya yi jalin ta, ban ko wallah shiga shi gama da ni"
"Innalillahi wa inna'ilaihirraji'una, anya Dan Talo kun yi addu'a kuwa? Yaro awa diyan shedannu? Bashi jin maganar kowa sai dai a ji tashi?"
"Ke Yabbuga shige ciki, kai kuma, dan Allah ka kama matar ka ku tafi gida, kuma da ka ke fad'in Mubaraka ta tahi yawo, ka hini sanin halin ta, iya sani na da ita ba za ai mata shaidar yawo ba, yarinya ce me hankali ,ko tunanin wani abun ne ya same ta baku yi, ku kam Allah ya yi muku sauqi, (gyara tsayuwar shi Ɗan jumma ya yi, ya na kada hannu, ya ce) zan ruhe gida"
Cikin sanyin jiki Mai buruji ta bi Dan Talo da jiki ya wa sanyi, sai yanzu maganar batan Mubarakan ya fara shigar shi, tabbas ita ba me yawo bace, kawai dai yawan fad'a da Lamishi ke yi ne ya sa shi ma yake fada.
Su na shan kwana suka tsaya cak, sai da suka tabbatar motar Lawwali bata nan, suka qarasa.
Su na shiga suka ga Lamishi na hada kayan ta, cikin tashin hankali, Dan Talo na tsaye a bakin qofar shiga dakin ya ce,
"Ke kuma mi na na ki ka yi haka? Ina zaki da wanga tsohon dare?"
"Gidan iyaye na zan tafi, tunda d'an da na haifa da ciki na ya ce sai ya yi ajali na akan qaunar shi, diyar da ni na haihe ta da ciki na, wanga wanne irin bala'i na? Ka dai san yadda Yaron nan shike ko?"
"Tau in kin tai can an ce maki barin ki zai? Kin ga kin ja musu musiba, gwanda ki zauna, gobe mu tai bid'ar ta gaba dayan mu, ki yi tunani dai"
Shiru ta yi, ta na nazari,to ina Mubaraka ta tai? Ita din ba me yawo ba ce, (sai yanzu ta san ba me yawo bace, duk sunayen da take kiran ta da su).
***********************
A hargitse ya shiga dajin, kowa ya san Oga ba lafiya a daren,dan haka kowa ya nutsu, No 1 da sauran yaran shi na kusa ne suka bi shi a baya, dakin da suke ajiye mutanen da suka sato, 'yan uwan su sun kasa biyan kudin fansa ya shiga ,firfito da su ya sa aka dinga yi, sai da ya fidda wajen mutum biyar sannan ya jera su a filin wajen, idanun shi kadai abin tsoro ne, bindigar da aka cika da harsashi ya karba ya dinga kai musu harbi, sai da ya harbe su tass, sannan ya koma dakin shi da ke wajen, ma'ajiyar giyar shi ya je ya bude,ya jima kwarai rabon shi da shan giya ,dakko kwalba ɗaya ya yi, ya kafa kai, bai aje ba sai da ya sha ta kusan rabi, wata iriyar razananniyar qara ya saki, ya buga kwalbar a qasa, wannan qarar ta firgita No 4 ba kadan ba, hankalin shi ya yi bala'in tashi, tsoro ya hana shi tunanin mafita.
In ya ce ze sanar da gaskiya,ya san bai tsira ba, in ya bari har Lawwali ya gano da kan shi nan ma bai tsira ba, ya zai yi??????
*Ina nissani?*
[6/21, 5:15 PM] HAERMEEBRAERH ❤️: 💅🏻 *A GARIN MU* 💅🏻
BY HAERMEEBRAERH
PAGE 27:
Sati biyu ya wuce ba Lawwali ba bayanin shi, ba Sultana kadai ba, hatta da Gwamna Halliru ya fara shiga tashin hankali akan lamarin Lawwali.
Duk wata barna da ta'asa da Lawwali ke aikatawa ta na komawa kunnen Gwamna Halliru, ga zabe ya gabato sauran kwana goma sha uku, lamarin ya tabarbare fiye da tunanin Gwamna, domin kuwa a yanzu Lawwali ko cikin gari bai cika shiga ba, sai jefi jefi dan ya ji halin da ake ciki game da neman qanwar shi da ya sa a yi.
Lawwali ya koma kamar mahauci, akan neman Mubaraka, ya yi kuka har ba iyaka, ya zama kamar wanda ya rasa iyayen shi da dangin shi a dare daya.
Duk wata motar da ta yi tsautsayin bi ta kusa da dajin su, to sunan su matattu, ko kuma ya sa a kame su, ayi ta azabtar wa, ko ya sa a yi ta amsar kudi wajen dangin su, madadin batan Mubraka ya risinar da shi,sai ya sake ruruta masa wutar rashin imani a zuciyar shi.
Sultana kuwa duk ta fige ta rame saboda rashin Lawwali, ko ta je Foundation din ma watarana da kuka take komawa gida, rashin ganin shi a idanun ta ba karamin azabtar da zuciyar ta yake ba.
Duk ta dora laifin akan Hajiya, domin a tunanin ta maganar da Hajiya ta yi ne ya sanya shi yin fushi ya tafi.
Ta gwada No shi ya fi sau shurin masaqi amma ta qi shiga, kullum sanar da ita ake a kashe wayar take, ta yi kuka ta godewa Allah, ta yi sallah ta yi addu'a akan Allah ya dawo mata da shi in da alkhairi, in babu Allah ya sa mata hakuri da dangana, hakan da ta yi ne ya sa ta ɗan samu sauqi kadan a ran ta, har ta ci gaba da aikin alkhairin da ta sa wa ran ta.
Shiru shirun ta, da rashin shiga mutane da take ya bawa Gwamna damar yada abubuwan da take na alkhairi a gidajen talabijin da rediyo, da duk wata kafar sadarwa, mutane kuwa na ta yabawa, wasu na qara neman taimako a wajen ta, ita kuwa hakan na mata dadi, ganin aikin da take ya na ta bunqasa.
In ta na aikin ta na samun nutsuwa da kwanciyar hankali,da ta dawo gida komai sai ya kwance mata ,ba abinda take gani a idon ta in ba Lawwali ba, tsayuwar shi a jikin mota, da murmushin shi mai sauti, yanayin yanda yake kafe ta da ido, ya na kallon ta, sai ta ji kamar a wannan lokacin ya ke kallon nata, har lumshe ido take, watarana ta yi murmushi in ta tuna, watarana ta fashe da kuka.
An shiga sati na Uku Lawwali be bayyana ba, sai wata safiyar Lahadi, ya shiga gari, direct wajen aski ya nufa,a ka yi masa aski me kyau, aka masa gyaran qafafu da hannuwa, sannan ya sayi turaruka, da kayan abinci ya nufi gidan shi,ko da ya shiga gidan duk ya yi qura, kallon ko ina ya yi, cikin sanyin jiki ya ajiye ledojin hannun shi ya kalli ko ina, wasu irin zaratan hawaye ne masu zafi suka dinga zubar masa.
Mubaraka ce ke masha shara, in ta biyo shi, ta yi wanka ya maida ta gida, ko gyaran da akai wa gidan na qarshe ita ta masa, har ta dinga mishi fadan ta ajiye wani flower vase a tsakiyar table, ta koma ta gan shi a qasa, ya kama kunnen shi ya na bata hakuri, ta na ta tura baki ta na shagwaba, ta ce ta hakura kar ya sake, ta mayar ta gyara komai, ta yi wanka ya maida ta gida, ya na gama tunawa ya sanya wani irin kuka mai ban tausayi, sannan ya ce,
"Barakana ina kin ka tai na? Wanne hali ki ke ciki? Kin ci abinci? Kin yi wanka kuwa? A wanne irin waje ki ke kwana? Barakana, ki yafe wa yayan ki, na kasa kare ki, na kasa nemo ki, baraka na ki dawo gare Ni, ke ce sanyin idaniya ta, na rabu da Sultana duk da son da nake mata, na kasa cire ta a zuciya ta, dan Allah ki dawo ki taya Ni neman soyayyar ta, ba zan iya ba Ni dai,ke Ni ka jira ki sa Sultana ta so ni, Barakaaaa"
Kuka ya dunqule a waje guda ya na yi, kamar qaramin yaro, ya na son dika qannen shi, amma mubaraka ta daban ce, ita kadai ce ke son shi, ita ke kula da shi, ita kadai ta damu da rayuwar shi, tun ya na da burin ya dawo na gari, har ya kangare, ba wanda ya damu da wace iriyar rayuwa yake ciki, kudi kawai iyayen shi suka sanya a gaba, yau kuwa zai kai musu kudin da zai haukata su, amma sai suma sun bayyana masa Barakan shi, ko ya sawa kudin fetur a gaban su ya qona, hakan sai ya fi masu ciwo sama da yanda yake ji a ran shi.
A haukace ya debi kudin da ya koma da su, masu dimbin yawa a jaka, ya zari makullin motar shi, da wayar shi da ya bari a gidan, bai je ko ina da ita ba, motar shi duk ta yi qura.
Ya na shiga ya fitar da ita, ya koma ya kulle gidan, ya na qoqarin fita daga layin, motoci guda biyu da ke kai Sultana Foundation a yanzu su ka shiga unguwar suma,kamar an ce ta daga kai, Lawwali ta gani fuskar shi ba walwala, idanun shi jawur kamar ba shi ba, ya na tsula gudu,gashi duk ya yi duhu,
"Auwal? Dama Auwal na nan? Shi ne ya daina zuwa? Driver bi motar Auwal duk inda ya yi,"
"Tau Ran ki shi dade"
Dayar motar masu tsaron lafiyar ta na ganin an juya suma suka bi su, ta waya ta sanar da su me ke faruwa, kwantar da hankalin su suka yi suka bi su a baya.
Saboda damuwar da Lawwali ke ciki, be ma kula ana bin shi ba, har sai da ya shiga unguwar su, ya tsaya a qofar gidan su, sannan ya kula da motocin Sultana.
Wani irin yanayi ne mara fassaruwa ya shige shi, kewa ne, tsantsar soyayya ce, da kuma neman taimakon ta, duk sun had'u sun game masa waje daya.
Ita kuwa bata san sanda hawaye ke gudu a fuskar ta ba, ga alama nan, Lawwali na shaye shaye, amma bata duban wannan, domin dama dan Adam tara yake, be cika goma ba, ita dai a kowanne hali yake ta na son shi, ita kadai ta san ya take ji.
"Innalillahi wa inna'ilaihirraji'una, anya Dan Talo kun yi addu'a kuwa? Yaro awa diyan shedannu? Bashi jin maganar kowa sai dai a ji tashi?"
"Ke Yabbuga shige ciki, kai kuma, dan Allah ka kama matar ka ku tafi gida, kuma da ka ke fad'in Mubaraka ta tahi yawo, ka hini sanin halin ta, iya sani na da ita ba za ai mata shaidar yawo ba, yarinya ce me hankali ,ko tunanin wani abun ne ya same ta baku yi, ku kam Allah ya yi muku sauqi, (gyara tsayuwar shi Ɗan jumma ya yi, ya na kada hannu, ya ce) zan ruhe gida"
Cikin sanyin jiki Mai buruji ta bi Dan Talo da jiki ya wa sanyi, sai yanzu maganar batan Mubarakan ya fara shigar shi, tabbas ita ba me yawo bace, kawai dai yawan fad'a da Lamishi ke yi ne ya sa shi ma yake fada.
Su na shan kwana suka tsaya cak, sai da suka tabbatar motar Lawwali bata nan, suka qarasa.
Su na shiga suka ga Lamishi na hada kayan ta, cikin tashin hankali, Dan Talo na tsaye a bakin qofar shiga dakin ya ce,
"Ke kuma mi na na ki ka yi haka? Ina zaki da wanga tsohon dare?"
"Gidan iyaye na zan tafi, tunda d'an da na haifa da ciki na ya ce sai ya yi ajali na akan qaunar shi, diyar da ni na haihe ta da ciki na, wanga wanne irin bala'i na? Ka dai san yadda Yaron nan shike ko?"
"Tau in kin tai can an ce maki barin ki zai? Kin ga kin ja musu musiba, gwanda ki zauna, gobe mu tai bid'ar ta gaba dayan mu, ki yi tunani dai"
Shiru ta yi, ta na nazari,to ina Mubaraka ta tai? Ita din ba me yawo ba ce, (sai yanzu ta san ba me yawo bace, duk sunayen da take kiran ta da su).
***********************
A hargitse ya shiga dajin, kowa ya san Oga ba lafiya a daren,dan haka kowa ya nutsu, No 1 da sauran yaran shi na kusa ne suka bi shi a baya, dakin da suke ajiye mutanen da suka sato, 'yan uwan su sun kasa biyan kudin fansa ya shiga ,firfito da su ya sa aka dinga yi, sai da ya fidda wajen mutum biyar sannan ya jera su a filin wajen, idanun shi kadai abin tsoro ne, bindigar da aka cika da harsashi ya karba ya dinga kai musu harbi, sai da ya harbe su tass, sannan ya koma dakin shi da ke wajen, ma'ajiyar giyar shi ya je ya bude,ya jima kwarai rabon shi da shan giya ,dakko kwalba ɗaya ya yi, ya kafa kai, bai aje ba sai da ya sha ta kusan rabi, wata iriyar razananniyar qara ya saki, ya buga kwalbar a qasa, wannan qarar ta firgita No 4 ba kadan ba, hankalin shi ya yi bala'in tashi, tsoro ya hana shi tunanin mafita.
In ya ce ze sanar da gaskiya,ya san bai tsira ba, in ya bari har Lawwali ya gano da kan shi nan ma bai tsira ba, ya zai yi??????
*Ina nissani?*
[6/21, 5:15 PM] HAERMEEBRAERH ❤️: 💅🏻 *A GARIN MU* 💅🏻
BY HAERMEEBRAERH
PAGE 27:
Sati biyu ya wuce ba Lawwali ba bayanin shi, ba Sultana kadai ba, hatta da Gwamna Halliru ya fara shiga tashin hankali akan lamarin Lawwali.
Duk wata barna da ta'asa da Lawwali ke aikatawa ta na komawa kunnen Gwamna Halliru, ga zabe ya gabato sauran kwana goma sha uku, lamarin ya tabarbare fiye da tunanin Gwamna, domin kuwa a yanzu Lawwali ko cikin gari bai cika shiga ba, sai jefi jefi dan ya ji halin da ake ciki game da neman qanwar shi da ya sa a yi.
Lawwali ya koma kamar mahauci, akan neman Mubaraka, ya yi kuka har ba iyaka, ya zama kamar wanda ya rasa iyayen shi da dangin shi a dare daya.
Duk wata motar da ta yi tsautsayin bi ta kusa da dajin su, to sunan su matattu, ko kuma ya sa a kame su, ayi ta azabtar wa, ko ya sa a yi ta amsar kudi wajen dangin su, madadin batan Mubraka ya risinar da shi,sai ya sake ruruta masa wutar rashin imani a zuciyar shi.
Sultana kuwa duk ta fige ta rame saboda rashin Lawwali, ko ta je Foundation din ma watarana da kuka take komawa gida, rashin ganin shi a idanun ta ba karamin azabtar da zuciyar ta yake ba.
Duk ta dora laifin akan Hajiya, domin a tunanin ta maganar da Hajiya ta yi ne ya sanya shi yin fushi ya tafi.
Ta gwada No shi ya fi sau shurin masaqi amma ta qi shiga, kullum sanar da ita ake a kashe wayar take, ta yi kuka ta godewa Allah, ta yi sallah ta yi addu'a akan Allah ya dawo mata da shi in da alkhairi, in babu Allah ya sa mata hakuri da dangana, hakan da ta yi ne ya sa ta ɗan samu sauqi kadan a ran ta, har ta ci gaba da aikin alkhairin da ta sa wa ran ta.
Shiru shirun ta, da rashin shiga mutane da take ya bawa Gwamna damar yada abubuwan da take na alkhairi a gidajen talabijin da rediyo, da duk wata kafar sadarwa, mutane kuwa na ta yabawa, wasu na qara neman taimako a wajen ta, ita kuwa hakan na mata dadi, ganin aikin da take ya na ta bunqasa.
In ta na aikin ta na samun nutsuwa da kwanciyar hankali,da ta dawo gida komai sai ya kwance mata ,ba abinda take gani a idon ta in ba Lawwali ba, tsayuwar shi a jikin mota, da murmushin shi mai sauti, yanayin yanda yake kafe ta da ido, ya na kallon ta, sai ta ji kamar a wannan lokacin ya ke kallon nata, har lumshe ido take, watarana ta yi murmushi in ta tuna, watarana ta fashe da kuka.
An shiga sati na Uku Lawwali be bayyana ba, sai wata safiyar Lahadi, ya shiga gari, direct wajen aski ya nufa,a ka yi masa aski me kyau, aka masa gyaran qafafu da hannuwa, sannan ya sayi turaruka, da kayan abinci ya nufi gidan shi,ko da ya shiga gidan duk ya yi qura, kallon ko ina ya yi, cikin sanyin jiki ya ajiye ledojin hannun shi ya kalli ko ina, wasu irin zaratan hawaye ne masu zafi suka dinga zubar masa.
Mubaraka ce ke masha shara, in ta biyo shi, ta yi wanka ya maida ta gida, ko gyaran da akai wa gidan na qarshe ita ta masa, har ta dinga mishi fadan ta ajiye wani flower vase a tsakiyar table, ta koma ta gan shi a qasa, ya kama kunnen shi ya na bata hakuri, ta na ta tura baki ta na shagwaba, ta ce ta hakura kar ya sake, ta mayar ta gyara komai, ta yi wanka ya maida ta gida, ya na gama tunawa ya sanya wani irin kuka mai ban tausayi, sannan ya ce,
"Barakana ina kin ka tai na? Wanne hali ki ke ciki? Kin ci abinci? Kin yi wanka kuwa? A wanne irin waje ki ke kwana? Barakana, ki yafe wa yayan ki, na kasa kare ki, na kasa nemo ki, baraka na ki dawo gare Ni, ke ce sanyin idaniya ta, na rabu da Sultana duk da son da nake mata, na kasa cire ta a zuciya ta, dan Allah ki dawo ki taya Ni neman soyayyar ta, ba zan iya ba Ni dai,ke Ni ka jira ki sa Sultana ta so ni, Barakaaaa"
Kuka ya dunqule a waje guda ya na yi, kamar qaramin yaro, ya na son dika qannen shi, amma mubaraka ta daban ce, ita kadai ce ke son shi, ita ke kula da shi, ita kadai ta damu da rayuwar shi, tun ya na da burin ya dawo na gari, har ya kangare, ba wanda ya damu da wace iriyar rayuwa yake ciki, kudi kawai iyayen shi suka sanya a gaba, yau kuwa zai kai musu kudin da zai haukata su, amma sai suma sun bayyana masa Barakan shi, ko ya sawa kudin fetur a gaban su ya qona, hakan sai ya fi masu ciwo sama da yanda yake ji a ran shi.
A haukace ya debi kudin da ya koma da su, masu dimbin yawa a jaka, ya zari makullin motar shi, da wayar shi da ya bari a gidan, bai je ko ina da ita ba, motar shi duk ta yi qura.
Ya na shiga ya fitar da ita, ya koma ya kulle gidan, ya na qoqarin fita daga layin, motoci guda biyu da ke kai Sultana Foundation a yanzu su ka shiga unguwar suma,kamar an ce ta daga kai, Lawwali ta gani fuskar shi ba walwala, idanun shi jawur kamar ba shi ba, ya na tsula gudu,gashi duk ya yi duhu,
"Auwal? Dama Auwal na nan? Shi ne ya daina zuwa? Driver bi motar Auwal duk inda ya yi,"
"Tau Ran ki shi dade"
Dayar motar masu tsaron lafiyar ta na ganin an juya suma suka bi su, ta waya ta sanar da su me ke faruwa, kwantar da hankalin su suka yi suka bi su a baya.
Saboda damuwar da Lawwali ke ciki, be ma kula ana bin shi ba, har sai da ya shiga unguwar su, ya tsaya a qofar gidan su, sannan ya kula da motocin Sultana.
Wani irin yanayi ne mara fassaruwa ya shige shi, kewa ne, tsantsar soyayya ce, da kuma neman taimakon ta, duk sun had'u sun game masa waje daya.
Ita kuwa bata san sanda hawaye ke gudu a fuskar ta ba, ga alama nan, Lawwali na shaye shaye, amma bata duban wannan, domin dama dan Adam tara yake, be cika goma ba, ita dai a kowanne hali yake ta na son shi, ita kadai ta san ya take ji.