Sashe 8
A Garin Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sun isa gidan da misalin takwas na safiya, sai da suka sha tambayoyi da kuma neman izinin barin Mubaraka shiga gidan wajen Hajiya Ikee, bayan bayani da Mai Buruji ta mata, dai ta amince, aka bar su su shiga, Mubaraka zuwan ta na farko kenan, dan haka sai kalle kalle take, irin na qauyawan da suka je binni, direct dakin Sultana Mai Buruji ta kai ta, suna tafe ta na sanar da ita duk binda ya kamata ta yi.
A zaune ta tarar da Sultana ta na karanta qur'ani, sai ta ji wani irin dad'i ya kama ta, durqusa wa ta yi ta gaishe ta cikin girmamawa ,itama ta amsa, bayani ta sake mata, cikin murmushi Sultana ta ce,
"Ai kuwa ga kamannin ku nan sun fito ke da Umman naki, Bismillah in kin wanke toilete zaki gyaran nan, sannan ki dan wanken wadannan kayan"
"To inshaa Allahu,"
Bayi ta je ta wanke tass, ta na yi ta na mamakin irin haduwar wajen,kayan bayin da ta gani a wata roba ta dauka ta duba an aje komai, amma ita da za a barta da hannu za ta wanke su, ba sai an wani sanya a washing machine ba.
Ko da ta fita gani ta yi Sultana ta koma saman sallaya ta bar mata gadon ta gyara, ai kuwa cikin azama ta fara gyarawa.
Karatun da Sultana take Yi itama ta fara bi, dan shiru Sultana ta Yi, cikin murmushi mai sauti,take bin Mubaraka da kallo, sai ta ji yarinyar ta shiga ran ta,
"Masha Allah, Mubaraka ko? Ashe ke din hafiza ce,masha Allah Muryar ki na da dadin karatu, izun ki nawa?"
"Na sauke Aunty sultana ,Amma ba a Mana bikin sauka ba, na gode da yaba min,"
Har ran ta ta ji dadin yabawar da Sultana ta Mata, ta so samun wannan yabon wajen iyayen ta, amma ina, ba su san mahimmancin karatun qur'ani ba su, balle su yaba.
A haka ta gama gyara dakin suna karatu ita da Sultana, cikin nishadi, sai Sultana ta ji kamar ta jima da sanin Mubaraka, yarinyar ta shiga ranta cikin lokaci qanqani, sai take jin ta kamar a mkaranta take, da ta gama aikin ta ma, hira suka dan yi, anan Sultana ta ke jin wasu labaran da bata ji dad'in su ba, game da rayuwar Mubaraka, ta na son karatu, iyayen ba su damu ba, a nan ne ta ji kwadayin son shiga cikin gari,ta na son ta je ta ga yanda mutane suke rayuwa a cikin unguwanni, da kewaye, amma ta san zai wahala ta samu hakan.
Daga baya Mubaraka Neman izinin zuwa wankin ta yi, sai da ta sake zuwa wajen Mai Buruji ta nuna mata wajen, dan yanayin kyaun gidan na ruda ta, ta manta hanyar zuwa wajen da ake wankin, har tunanin yanda za ta koma wajen Sultana ma take.
Yawo take a gidan Dan ganin ya gidan ya ke,ta na tafe ta na qarewa qayataccen gidan kallo, ta na jinjina lamari irin na masu kud'i, cikin murmushi ta ayyana a ran ta
'Dole gida ya had'u ya tsaru, gidan gwamna guda'
Tunanin ta ya tsaya cak a daidai sanda ta shiga wata farfajiya, a hankali take jiyo kukan qaramin yaro, ta na tafe, har ta kai saitin inda kukan ke fitowa, ta na saurarawa sai ta ji ya na fad'in,
" Dan Allah ku kyale ni da zafi, wayyoo na Shiga uku"
Wani gini ta gani, an dan kebance shi daga jikin ginin babban gidan, dan haka can ta nufa, rasa ta inda za ta leqa ta Yi, saboda ya nayin gidan ba qaramin gini aka Masa ba ta yanda zata samu damar leqawa ta ga me ke faruwa.
Wankin da ta je shanyawa ta maida hankali wajen shanyawa , ta shanya biyu ta samu gefe ta zauna zaman jira riqe da bokoti, da kuma sabuwar wayar ta da earpiece da Lawwali ya siya mata, ta tabbata koma su wane za su fito, to kuwa zata jira,hannun ta ta sanya qasan rigar ta ta zaro wayar ta da earpiece din ta, ta danna a kunnen ta ta rage qirar'ar da ta kunna sosai, hankalin ta tashe, ta rasa me akewa yaron da ta ji ya na ihu, ji take kamar ta fada dakin ko da za a kashe ta sai dai a kashe ta, amma ta na so ta ga agajin me yaro qarami yake nema a wannan babban gidan, da alama gidan nan na dauke da wani sirri...
Bata gama tunanin ba ta ji ana son bude qofar qara volume din wayar ta tayi, ta ci gaba da shanya, ba tare da ta nuna alamar ta San komai ba, da gefen Ido Kuma cikin dabara ta ke kallon wajen, qaramin yaro almajiri aka fitar qafafun shi a ware yake takawa, dik inda ya wuce jini ke diga, Yayan ta Lawwali ta gani da wani amintaccen yaron shi riqe da yaron, kukan da take riqewa ne ya ke qoqarin tona asirin ta.
Su na wucewa Excellency ya fito, ya na qarasa gyara rigar shi ,tare da yarfe zufa,wata takarda ce a hannun shi ya na tafe ya na nannade wa, ya zagaya bayan ginin wajen, ya bude wani Dan Rami a wajen suck away ya wulla takardar da in ba qarya Mubaraka zatai ba rubutun larabci ne a jiki, domin ma'abociyar karatun irin takardun ce ita a kullum, dan haka ta san me idon ta ya hango.
Wata iriyar zufa ta ji ta karyo Mata, shin meye wannan?
'ya Allah ka Sa ba abinda nake zargi bane' shi ne abinda ta ayyana a ran ta.
Cikin tashin hankali ta shanya rigar Sultana ta bacci ta qarshe.
Ta durqusa ta dau bokiti za ta tafi ta ji an ce
"Keee"
Ta so ta nuna ta ji Amma sai ta Dake, ta fara rera karatun qur'ani ta na bin na wayarta.
Kula da abinda ke kunnen ta ne ya Sanya Excellency jinkirtawa,ya daina motsi, ya na son tabbatar da shin ta gan shi ko bata gan shi ba, har ta dau bokin ta za ta tafi zuciyar ta ta hau ayyana mata ta juya, kwakwalwar ta Kuma ta bata shawarar ta ci gaba da tafiya, shawarar kwakwalwarta ta dauka ta ci gaba da tafiya, kamar bata ga komai ba, kuma bata ji komai ba.
Bata tsaya ba kuwa se da ta kai qaramar qofar da zata sada ta da cikin babban gidan, hannun ta mai rawar tsoron da ya mamaye zuciyar ta ta sanya ta bude qofar, tai wuf ta shige.
Ta na Isa dakin da washing machine din ya ke ta ajiye bokitin ta dinga kuka, kamar zuciyar ta ta Fado bakin ta.
Ta na tsaka da kuka ta ji dawowar su Lawwali, lallabawa ta Yi ta bi su a hankali, a daidai wani lungu ta tsaya, ta ji suna magana qasa qasa ba ta ji me ake fadi ba dai, Amma tabbas har da Gwauna, ta najin motsin komawar su ta gudu ta koma ciki itama, mayafin ta ta Sanya, ta fita gate, su Lawwali na fita Suka gan ta, ta na tafiya a qasa, tsaida abun hawan ya sa aka Yi.
Sannan ya ce ta Shiga
Gani ya Yi ta na kuka, cikin damuwa ya ce,
"Barakana ya akai? Kukan me ki ke?"
Kafe shi ta Yi da jajayen idanun ta, kamar ta amsa shi ta fasa.
"Kai na ke ciwo"
"Subhanallahi....Kai mu wuce chemist"
Can kuwa Suka je, a ka hado Mata magani kala kala, ya sai Mata yagot da lemun roba ya sai Mata gasasshen nama, ya ce su tafi.
Har gida Suka Kai ta, ya kama hannun ta suka shige, yaran shi na mota su na jiran shi,
Lawwali na shiga ya Bata Rai,
"Uban wa ya aike ta aiki gidan can ? Na ce waye ya aike ta aiki can gidan yau?"
"Uban ka na, ishasshe,nicce uban ka na, Dan uban ka ba ka Yi min hwadin banza, (baka yi min fad'in banza) ni uban ka zan CI ni kwana lahiya"
"Ni ba fad'a nake nema ba Lamishi, kin San yarinyar Nan Bata Saba da aikin wahala ba, wacce a aike ta aiki can gidan?ta je makaranta ta dawo ta je aiki? Habaa"
"To na tashi masassara ta damen, Shina nicce ta tai ta taya ni, yo wankin sultana nawa ne? Diyar da kamar yanzu ta Sanya ta cire haka tuwahin ta suke, Kai ka daure ma yarinyar ga gin**take Mana iskanci wallah"
Mubaraka ce ta ja hannun Lawwali Suka je dakin ta, ta ce
"Yah ni fa qarya na Yi Amma ba ciwon Kai nake ba"
Cikin mamaki ya kalle ta, Mubaraka da qarya?
"Ke ko me ya faru haka?"
"Yah Auwal ka fadan gaskiyar abinda kuka wa almajirin nan, na ji kukan shi, ya dawo ya na zubar da jini ta qafar shi, shin..... Innalillahi....wayyooo Allah na....Yah Auwal ka rantse min da Allah Kai baka.....wayyooo Allah na"
Jikin Mubaraka ne ya hau rawa ta ma kasa kukan.
"Ba bu ni Mubaraka ba na aikata luwadi, na Yi maki alqawari ba bu ni, yaro kawai muka samo saboda umarnin me gida ne"
Kukan da take riqewa ne ya kwace Mata, ta dinga Yi kamar zata shide,tausayin yaron ne ya Mata yawa, hango girman Gwauna ta Yi, ta hango yaron, wani kukan ta fara tare da tari Mai qarfi, ta na shessheqa,ruwa ya bude ya fara bata, ta Yi wurgi da ruwan, cikin kuka ta ce,
"Yah Auwal ka bar aiki da shi, zai Kai ka wuta, yah Auwal ko ba abinci za mu rayu ba zamu iya second daya cikin wutar Allah ba, yah Auwal ka min alqawarin baka taba aikata wanan abun da kowa ba, ba kuma za ka bari a yi da Kai ba,"
"Na maki alqawari na tsani luwadi,qazanta ne, ban taba ba, ba a taba Yi min ba, Dan Allah ki dena kuka, zuciya ta zafi take in Ina jin kukan ki, yanzu Lamishi sai ta zo,"
Muryar ta kuwa Suka jiyo,
"Shegiya 'yar bid'ar a Yi, wato kuka ki ke masa shi Kuma uban mu ya zo ya Dake mu ko? To ki suma,na hada ku dika na ci uban ku"
Ta kasa daina kuka, to me ya Yi da takarda Mai rubutun Arabic?
A zaune ta tarar da Sultana ta na karanta qur'ani, sai ta ji wani irin dad'i ya kama ta, durqusa wa ta yi ta gaishe ta cikin girmamawa ,itama ta amsa, bayani ta sake mata, cikin murmushi Sultana ta ce,
"Ai kuwa ga kamannin ku nan sun fito ke da Umman naki, Bismillah in kin wanke toilete zaki gyaran nan, sannan ki dan wanken wadannan kayan"
"To inshaa Allahu,"
Bayi ta je ta wanke tass, ta na yi ta na mamakin irin haduwar wajen,kayan bayin da ta gani a wata roba ta dauka ta duba an aje komai, amma ita da za a barta da hannu za ta wanke su, ba sai an wani sanya a washing machine ba.
Ko da ta fita gani ta yi Sultana ta koma saman sallaya ta bar mata gadon ta gyara, ai kuwa cikin azama ta fara gyarawa.
Karatun da Sultana take Yi itama ta fara bi, dan shiru Sultana ta Yi, cikin murmushi mai sauti,take bin Mubaraka da kallo, sai ta ji yarinyar ta shiga ran ta,
"Masha Allah, Mubaraka ko? Ashe ke din hafiza ce,masha Allah Muryar ki na da dadin karatu, izun ki nawa?"
"Na sauke Aunty sultana ,Amma ba a Mana bikin sauka ba, na gode da yaba min,"
Har ran ta ta ji dadin yabawar da Sultana ta Mata, ta so samun wannan yabon wajen iyayen ta, amma ina, ba su san mahimmancin karatun qur'ani ba su, balle su yaba.
A haka ta gama gyara dakin suna karatu ita da Sultana, cikin nishadi, sai Sultana ta ji kamar ta jima da sanin Mubaraka, yarinyar ta shiga ranta cikin lokaci qanqani, sai take jin ta kamar a mkaranta take, da ta gama aikin ta ma, hira suka dan yi, anan Sultana ta ke jin wasu labaran da bata ji dad'in su ba, game da rayuwar Mubaraka, ta na son karatu, iyayen ba su damu ba, a nan ne ta ji kwadayin son shiga cikin gari,ta na son ta je ta ga yanda mutane suke rayuwa a cikin unguwanni, da kewaye, amma ta san zai wahala ta samu hakan.
Daga baya Mubaraka Neman izinin zuwa wankin ta yi, sai da ta sake zuwa wajen Mai Buruji ta nuna mata wajen, dan yanayin kyaun gidan na ruda ta, ta manta hanyar zuwa wajen da ake wankin, har tunanin yanda za ta koma wajen Sultana ma take.
Yawo take a gidan Dan ganin ya gidan ya ke,ta na tafe ta na qarewa qayataccen gidan kallo, ta na jinjina lamari irin na masu kud'i, cikin murmushi ta ayyana a ran ta
'Dole gida ya had'u ya tsaru, gidan gwamna guda'
Tunanin ta ya tsaya cak a daidai sanda ta shiga wata farfajiya, a hankali take jiyo kukan qaramin yaro, ta na tafe, har ta kai saitin inda kukan ke fitowa, ta na saurarawa sai ta ji ya na fad'in,
" Dan Allah ku kyale ni da zafi, wayyoo na Shiga uku"
Wani gini ta gani, an dan kebance shi daga jikin ginin babban gidan, dan haka can ta nufa, rasa ta inda za ta leqa ta Yi, saboda ya nayin gidan ba qaramin gini aka Masa ba ta yanda zata samu damar leqawa ta ga me ke faruwa.
Wankin da ta je shanyawa ta maida hankali wajen shanyawa , ta shanya biyu ta samu gefe ta zauna zaman jira riqe da bokoti, da kuma sabuwar wayar ta da earpiece da Lawwali ya siya mata, ta tabbata koma su wane za su fito, to kuwa zata jira,hannun ta ta sanya qasan rigar ta ta zaro wayar ta da earpiece din ta, ta danna a kunnen ta ta rage qirar'ar da ta kunna sosai, hankalin ta tashe, ta rasa me akewa yaron da ta ji ya na ihu, ji take kamar ta fada dakin ko da za a kashe ta sai dai a kashe ta, amma ta na so ta ga agajin me yaro qarami yake nema a wannan babban gidan, da alama gidan nan na dauke da wani sirri...
Bata gama tunanin ba ta ji ana son bude qofar qara volume din wayar ta tayi, ta ci gaba da shanya, ba tare da ta nuna alamar ta San komai ba, da gefen Ido Kuma cikin dabara ta ke kallon wajen, qaramin yaro almajiri aka fitar qafafun shi a ware yake takawa, dik inda ya wuce jini ke diga, Yayan ta Lawwali ta gani da wani amintaccen yaron shi riqe da yaron, kukan da take riqewa ne ya ke qoqarin tona asirin ta.
Su na wucewa Excellency ya fito, ya na qarasa gyara rigar shi ,tare da yarfe zufa,wata takarda ce a hannun shi ya na tafe ya na nannade wa, ya zagaya bayan ginin wajen, ya bude wani Dan Rami a wajen suck away ya wulla takardar da in ba qarya Mubaraka zatai ba rubutun larabci ne a jiki, domin ma'abociyar karatun irin takardun ce ita a kullum, dan haka ta san me idon ta ya hango.
Wata iriyar zufa ta ji ta karyo Mata, shin meye wannan?
'ya Allah ka Sa ba abinda nake zargi bane' shi ne abinda ta ayyana a ran ta.
Cikin tashin hankali ta shanya rigar Sultana ta bacci ta qarshe.
Ta durqusa ta dau bokiti za ta tafi ta ji an ce
"Keee"
Ta so ta nuna ta ji Amma sai ta Dake, ta fara rera karatun qur'ani ta na bin na wayarta.
Kula da abinda ke kunnen ta ne ya Sanya Excellency jinkirtawa,ya daina motsi, ya na son tabbatar da shin ta gan shi ko bata gan shi ba, har ta dau bokin ta za ta tafi zuciyar ta ta hau ayyana mata ta juya, kwakwalwar ta Kuma ta bata shawarar ta ci gaba da tafiya, shawarar kwakwalwarta ta dauka ta ci gaba da tafiya, kamar bata ga komai ba, kuma bata ji komai ba.
Bata tsaya ba kuwa se da ta kai qaramar qofar da zata sada ta da cikin babban gidan, hannun ta mai rawar tsoron da ya mamaye zuciyar ta ta sanya ta bude qofar, tai wuf ta shige.
Ta na Isa dakin da washing machine din ya ke ta ajiye bokitin ta dinga kuka, kamar zuciyar ta ta Fado bakin ta.
Ta na tsaka da kuka ta ji dawowar su Lawwali, lallabawa ta Yi ta bi su a hankali, a daidai wani lungu ta tsaya, ta ji suna magana qasa qasa ba ta ji me ake fadi ba dai, Amma tabbas har da Gwauna, ta najin motsin komawar su ta gudu ta koma ciki itama, mayafin ta ta Sanya, ta fita gate, su Lawwali na fita Suka gan ta, ta na tafiya a qasa, tsaida abun hawan ya sa aka Yi.
Sannan ya ce ta Shiga
Gani ya Yi ta na kuka, cikin damuwa ya ce,
"Barakana ya akai? Kukan me ki ke?"
Kafe shi ta Yi da jajayen idanun ta, kamar ta amsa shi ta fasa.
"Kai na ke ciwo"
"Subhanallahi....Kai mu wuce chemist"
Can kuwa Suka je, a ka hado Mata magani kala kala, ya sai Mata yagot da lemun roba ya sai Mata gasasshen nama, ya ce su tafi.
Har gida Suka Kai ta, ya kama hannun ta suka shige, yaran shi na mota su na jiran shi,
Lawwali na shiga ya Bata Rai,
"Uban wa ya aike ta aiki gidan can ? Na ce waye ya aike ta aiki can gidan yau?"
"Uban ka na, ishasshe,nicce uban ka na, Dan uban ka ba ka Yi min hwadin banza, (baka yi min fad'in banza) ni uban ka zan CI ni kwana lahiya"
"Ni ba fad'a nake nema ba Lamishi, kin San yarinyar Nan Bata Saba da aikin wahala ba, wacce a aike ta aiki can gidan?ta je makaranta ta dawo ta je aiki? Habaa"
"To na tashi masassara ta damen, Shina nicce ta tai ta taya ni, yo wankin sultana nawa ne? Diyar da kamar yanzu ta Sanya ta cire haka tuwahin ta suke, Kai ka daure ma yarinyar ga gin**take Mana iskanci wallah"
Mubaraka ce ta ja hannun Lawwali Suka je dakin ta, ta ce
"Yah ni fa qarya na Yi Amma ba ciwon Kai nake ba"
Cikin mamaki ya kalle ta, Mubaraka da qarya?
"Ke ko me ya faru haka?"
"Yah Auwal ka fadan gaskiyar abinda kuka wa almajirin nan, na ji kukan shi, ya dawo ya na zubar da jini ta qafar shi, shin..... Innalillahi....wayyooo Allah na....Yah Auwal ka rantse min da Allah Kai baka.....wayyooo Allah na"
Jikin Mubaraka ne ya hau rawa ta ma kasa kukan.
"Ba bu ni Mubaraka ba na aikata luwadi, na Yi maki alqawari ba bu ni, yaro kawai muka samo saboda umarnin me gida ne"
Kukan da take riqewa ne ya kwace Mata, ta dinga Yi kamar zata shide,tausayin yaron ne ya Mata yawa, hango girman Gwauna ta Yi, ta hango yaron, wani kukan ta fara tare da tari Mai qarfi, ta na shessheqa,ruwa ya bude ya fara bata, ta Yi wurgi da ruwan, cikin kuka ta ce,
"Yah Auwal ka bar aiki da shi, zai Kai ka wuta, yah Auwal ko ba abinci za mu rayu ba zamu iya second daya cikin wutar Allah ba, yah Auwal ka min alqawarin baka taba aikata wanan abun da kowa ba, ba kuma za ka bari a yi da Kai ba,"
"Na maki alqawari na tsani luwadi,qazanta ne, ban taba ba, ba a taba Yi min ba, Dan Allah ki dena kuka, zuciya ta zafi take in Ina jin kukan ki, yanzu Lamishi sai ta zo,"
Muryar ta kuwa Suka jiyo,
"Shegiya 'yar bid'ar a Yi, wato kuka ki ke masa shi Kuma uban mu ya zo ya Dake mu ko? To ki suma,na hada ku dika na ci uban ku"
Ta kasa daina kuka, to me ya Yi da takarda Mai rubutun Arabic?