Sashe 81
A Garin Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ameeen, ina godiya, waccan matar taka ta matsu na san taji me ke hwaruwa, bari mu tai, sai ka iso,"
"Tau ya yi, Allah shi kiyaye hanya"
"Ameen"
Mota Sultan ya shiga cike da farin ciki,ya bayyana wa Sultana me ya faru,ta yi murna kwarai da jin hakan.
Mubaraka kuwa leqawa ta dinga yi ta window ta na kallon Sultan, bayan tafiyar su Lawwali ya kira kowa da kowa, ya fidda makullan gidajen da yake da su a hannun shi, wanda ba shi da su kuma a wajen shi Sultan ya ce zai bashi in sun hadu a cikin gari.
Miqawa wasun su makullan yayi sannan ya sanar da su, ba zai yu kowa ya samu gida shi daya da matar shi ba, wani gidan sai dai mutum biyu, wani gidan ma sai dai mutum uku, daga baya duk wanda Allah ya horewa ya tashi.
Godiya suka dinga yi, tare da addu'a da fatan alkhairi,wasu daga cikin matan har ma da mazan kuka suka dinga yi, sabo kenan, turken wawa.
Suna nan su na jajanta rabuwar su da juna mazajen da suka maida Limaman da suka daura musu aure suka dawo, nan aka sanar da su me ya faru, sun yi godiya sosai, sannan suma sun jimanta rabuwa da junan su.
Lawwali dakin su ya je, ya aika a kira masa Mubaraka.
Ita ta taya shi hade kayan su shi da Sultana, ya bada umarnin kayan gadon a kai masa gidan su, can dakin Mubaraka za a saka.
Su na gyara dakin ne ya bijiro mata da maganar Sultan, kunya ce ta kama ta, shi kuma dariya ya yi, ya ce,
"Ohhh rayuwar duniya kenan, wai Mubaraka 'yar qararramar nan ce yanzu ta girma har ta kai ga saurayi, Allah to shi sanya alkhairi, "
"Kaiii Yah Auwal ni fa ba yanzu za ka yi min auren ba, ni dai ba na so na rabu da ku"
"Tabbb ai kuwa ya zama dole, ko ba aure ai akwai mutuwa ko? Ballantana mace dama ita ba mazauniyar gidan iyayen ta bace, komai daren dad'ewa za ta yi aure, sai wadda Allah ya nufa ba zata taba aure ba a rayuwar ta"
"Haka ne, Allah ya sa mu dace,...Yah Auwal yau za mu bar nan?"
"Ahh ahh, sai gobe ko jibi ma, sai an kai kayan ga gida, an gyara miki d'akin ki, sannan zan maishe ki da hannu na, na damqa musu amanar ki,na gaji da faɗa da kowa ni yanzu, ba na son tashin hankali da kowa, in kin koma ki sanya wa zuciyar ki hankurin zama da su, tunda kin dai san yanda halin su shike,"
"Haka ne Yah Auwal, in shaa Allahu, za ka same ni mai hakuri"
"Allah ya miki albarka Barakana, dama can ke mai hakuri ce,Allah shi qara maki hankuri akan duk abinda zai same ki"
Ameeen, Yah Auwal dina"
Haka sukai ta hirar su, su na tattara kayayyakin Sultana.
*************************
Wata mata ce a tsaye a jikin mota, a gaban wani babban super market ta na waya, kaya aka debo niqi niqi za a saka a bayan mota, ta danna key din hannun ta, ma'aikatan super market din suka zuba kayan, Laminu na can gefe ya na kallon ta, ya jima ya na bin matar tun safe da ya fito daga gida, har yamman nan.
Su na gamawa ta sallame su,ta shige motar ta, ta tada ta, ta hau titi, Laminu ma bin ta ya yi a baya, wata hanya ta dauka, wadda take shiru ba mutane sosai, shi ma binta ya yi, ya sha gaban ta, wani burki ta ci, tare da daga kai, a tsorace, ta kalle shi.
A tare suka fito daga motocin su, Laminu ne ya nufe ta da fuskar tausaya wa, da ban hakuri, ya shammace ta ya shaqa mata wani tsumma a hanci, dauke numfashin ta tayi, ta kama hannun shi ta juyar da shi ta murde shi, ya fadi qasa da guiwowin shi, su na haka wasu motocin jami'an tsaro suka qaraso, su ma tafe suke su na bin su a boye dama.
Sake numfashin ta tayi, ta shaqi iska, duk da haka sai da d'an wanda ta shaqa ya sa ta jiri.
Kamata wani daga jami'an tsaron ya yi, suka sa ta a mota, Laminu kuwa tuni an danna shi a motar 'yan sandan, nan suka dunguma baki dayan su, sai police station, ana zuwa dakin tuhuma aka miqa Laminu.
Binciken da jami'an tsaron suka yi akan mutuwar yaron da suka kama dan ya bada shaida akan wanda ya sa su sace Hajiyan Hansatu ya nuna musu cewa akwai sa hannun Laminu, dan haka suka had'a masa wannan tarkon da jami'ar tsaro mace, suka samu nasarar kama shi.
Laminu ya qi bayyana abokan ta'addancin shi da fari sai da ya ci na jaki, ya ga za su masa lahani a banza, shi ne kuwa ya bayyana sunan Isah, nan da nan kuwa aka kira Yaya Musa aka sanar da shi su na buqatar su a station din, dan jin yanda ta kaya.
Hajiya na ta murna ta shirya ta ce ma Yaya Musa su je,a hanya ta kira Hansatu ta sanar da ita an kira su a police station, an ce a samu wani mahimmin bayani, da ya kamata su sani.
Fatan alkhairi ta musu sannan ta ce in su Ameenatu sun taso daga makaranta za su zo.
Su na isa station din aka sanar da su mummunan labarin da ya sanya Hajiya kuka wiwi, da idanun ta, sai lallashin ta ake ta kasa denawa, ta dauki soyayya mai tsafta ta sanya a zuciyar ta wa Isah ashe mutumin banza ne.
Har wajen Laminu aka je da su, ta kalle shi ta ce,
"Allah wadai da samuwar irin ku cikin al'ummar Annabi Muhammad, Allah ya shirya masu hali irin naku, yanzu ka dube ka, yaro kyakkyawa, wa ze ce za ka aikata wannan mugun abu? Yanzu shi abokin naka kuna waya ne? Dan tun da ya tahi bai kire ni ba, wancan karon kuwa ya na kira na"
Cikin jin kunyar dattijuwar Laminu ya ce,
"Hajiya Isah bai dawo wa yanzu gaskiya, dan kuwa abokin harka ta ta saida koken wani inyamuri ya ce ya sanya koken cikin kayan Isah kamar yanda mun ka tsara, kuma an kama Isah, an kulle shekara goma zai yi a kurkuku,"
"Innalillahi wa inna ilaihirraji'una, kaiii wanga yaro kwai baqin mugu, wato abokin naka ka ci wa amana haka? Shi na can daure ga hukumar da bata san sassauci ba, ka mayar min da d'iya ita da zaura (bazawara) ba su da banbanci, Allah ka isar min, Allah ka isar mana abinda yaran nan su ka yi muna"
Kuka sosai Hajiya take faman yi, a haka suka koma gida, Laminu na nan ana shirye shiryen miqa shi ga kotu, asirin shi ya gama tonuwa.
Tun a hanya Hajiya ta kira Hansatu ta ce ta samu abun hawa ta taho,ta wa driver waya ya kawo su Ameenatu gidan ta, cike da damuwa Hansatu ta ce to, bata so ta tsaya tambayar Hajiyan meke faruwa ta waya.
Rurrufe ko ina ta yi, sannan ta leqa gidan 'Yabbuga ta gaishe ta, ta sanar da ita zata gidan su,a hanyar ta ta zuwa bakin titi, ta wuce ta qofar gidan su Lamishi ta ga ana ta shiga da kayan gado.
Ga wata rumfa nan Dan Talo na ta bugawa a qofar gidan da kan shi.
A bakin gate din gidan su aka ajiye ta, ta shiga, bayan ta gaida mai gadi ta wuce cikin gidan.
A parlour ta tadda Yaya Musa da Yaya Abdullahi (Yayan matar Musa) su na zaune cikin jimami, su na ganin ta kowannen su fuskar shi ta sake danyancewa da tausayin ta.
Hajiya kuwa kuka ta sanya, ta dinga yafitar Hansatu da hannu, wajen ta ta nufa ta zauna daf da ita, ta na so ta yi kuka, dan ta san duk abinda ya sanya Hajiya kuka ba qarami bane.
"Hajiya mi ya faru? Mutuwa an kai? Me ya samu Aunty Azizah?"
Ta na fada ta na kallon Abdullahi, da sauri ya kada mata kai, alamar Ah ah,
"Lafiyar ta qlou, ta na Spain ma yanzu haka,"
"To me ya faru?"
Yaya Musa ne ya daure ya labarta mata komai, Hansatu kuka ta sanya, tare da fadin
"Ba zan taba yafe maka ba Isah, soyayyar ka ba ta amfanar da ni komi ba,ka cutar dani, ba iyaka, na hakura, amma sai da ka haɗa da mahaifiya ta, Isah me ta yi maka? In ni ce baka so sai ka sawwaqe min, me mahaifiya ta ta maka?......Hajiya, Hajiya, kin tuna sanda an ka sace su Ameenatu? Tabbas Isah na da hannu a wannan satar"
"Ahh ahh Hansatu, babu kyau zargi, dan kuwa wannan zargi ne, ba ki tabbatar ba"
"Hajiya ina da yaqinin da sa hannun Isah a wannan lamarin saboda tun sannan suke abota shi da Laminu, Hajiya akwai abubuwan da ban sanar da ke ba saboda bana so hankalin ki ya tashi, na dauki alqawarin tunda ni na bijire muku na zabe shi, komi ze yi min zan shanye ba zan fada wa kowa ba, Hajiya Isah na min......"
Nan dai Hansatu ta dage ta sanar ma da mahaifiyar ta komai da Isah yake mata, Hajiya da kowa da ke wajen ya tausaya mata,sannan sun mata faɗa sosai, musamman akan qin sanar da Hajiya tunda ya tafi wancan karon bai neme ta ba, ai da ta sanar tun a sannan da an dau mataki.
"Tau shi kenan yawuce ,Musa ai ka ga da rabon Allah shi hannunta shi can ga hukumar da sun ka fi mu iya hukunci, yanzu yanda za a yi, kai da Abdullahi,ku shirya ku je can wajen shi, ya sakar min d'iya ta, walle ta gama auren shi, ya qarasa shekarar shi goma ya bid'i wata ya aura, ina dalili.
In ya tsaya muku taurin kai, ku faɗa masa za ku yi qarar shi akan abinda ya yi wa hansatu a can, ku tsoratar da d'an nema, ya sake ta dolen shi, yarinya ta da kyawun ta ba zata rasa mashinshini ba"
"Tau ya yi, Allah shi kiyaye hanya"
"Ameen"
Mota Sultan ya shiga cike da farin ciki,ya bayyana wa Sultana me ya faru,ta yi murna kwarai da jin hakan.
Mubaraka kuwa leqawa ta dinga yi ta window ta na kallon Sultan, bayan tafiyar su Lawwali ya kira kowa da kowa, ya fidda makullan gidajen da yake da su a hannun shi, wanda ba shi da su kuma a wajen shi Sultan ya ce zai bashi in sun hadu a cikin gari.
Miqawa wasun su makullan yayi sannan ya sanar da su, ba zai yu kowa ya samu gida shi daya da matar shi ba, wani gidan sai dai mutum biyu, wani gidan ma sai dai mutum uku, daga baya duk wanda Allah ya horewa ya tashi.
Godiya suka dinga yi, tare da addu'a da fatan alkhairi,wasu daga cikin matan har ma da mazan kuka suka dinga yi, sabo kenan, turken wawa.
Suna nan su na jajanta rabuwar su da juna mazajen da suka maida Limaman da suka daura musu aure suka dawo, nan aka sanar da su me ya faru, sun yi godiya sosai, sannan suma sun jimanta rabuwa da junan su.
Lawwali dakin su ya je, ya aika a kira masa Mubaraka.
Ita ta taya shi hade kayan su shi da Sultana, ya bada umarnin kayan gadon a kai masa gidan su, can dakin Mubaraka za a saka.
Su na gyara dakin ne ya bijiro mata da maganar Sultan, kunya ce ta kama ta, shi kuma dariya ya yi, ya ce,
"Ohhh rayuwar duniya kenan, wai Mubaraka 'yar qararramar nan ce yanzu ta girma har ta kai ga saurayi, Allah to shi sanya alkhairi, "
"Kaiii Yah Auwal ni fa ba yanzu za ka yi min auren ba, ni dai ba na so na rabu da ku"
"Tabbb ai kuwa ya zama dole, ko ba aure ai akwai mutuwa ko? Ballantana mace dama ita ba mazauniyar gidan iyayen ta bace, komai daren dad'ewa za ta yi aure, sai wadda Allah ya nufa ba zata taba aure ba a rayuwar ta"
"Haka ne, Allah ya sa mu dace,...Yah Auwal yau za mu bar nan?"
"Ahh ahh, sai gobe ko jibi ma, sai an kai kayan ga gida, an gyara miki d'akin ki, sannan zan maishe ki da hannu na, na damqa musu amanar ki,na gaji da faɗa da kowa ni yanzu, ba na son tashin hankali da kowa, in kin koma ki sanya wa zuciyar ki hankurin zama da su, tunda kin dai san yanda halin su shike,"
"Haka ne Yah Auwal, in shaa Allahu, za ka same ni mai hakuri"
"Allah ya miki albarka Barakana, dama can ke mai hakuri ce,Allah shi qara maki hankuri akan duk abinda zai same ki"
Ameeen, Yah Auwal dina"
Haka sukai ta hirar su, su na tattara kayayyakin Sultana.
*************************
Wata mata ce a tsaye a jikin mota, a gaban wani babban super market ta na waya, kaya aka debo niqi niqi za a saka a bayan mota, ta danna key din hannun ta, ma'aikatan super market din suka zuba kayan, Laminu na can gefe ya na kallon ta, ya jima ya na bin matar tun safe da ya fito daga gida, har yamman nan.
Su na gamawa ta sallame su,ta shige motar ta, ta tada ta, ta hau titi, Laminu ma bin ta ya yi a baya, wata hanya ta dauka, wadda take shiru ba mutane sosai, shi ma binta ya yi, ya sha gaban ta, wani burki ta ci, tare da daga kai, a tsorace, ta kalle shi.
A tare suka fito daga motocin su, Laminu ne ya nufe ta da fuskar tausaya wa, da ban hakuri, ya shammace ta ya shaqa mata wani tsumma a hanci, dauke numfashin ta tayi, ta kama hannun shi ta juyar da shi ta murde shi, ya fadi qasa da guiwowin shi, su na haka wasu motocin jami'an tsaro suka qaraso, su ma tafe suke su na bin su a boye dama.
Sake numfashin ta tayi, ta shaqi iska, duk da haka sai da d'an wanda ta shaqa ya sa ta jiri.
Kamata wani daga jami'an tsaron ya yi, suka sa ta a mota, Laminu kuwa tuni an danna shi a motar 'yan sandan, nan suka dunguma baki dayan su, sai police station, ana zuwa dakin tuhuma aka miqa Laminu.
Binciken da jami'an tsaron suka yi akan mutuwar yaron da suka kama dan ya bada shaida akan wanda ya sa su sace Hajiyan Hansatu ya nuna musu cewa akwai sa hannun Laminu, dan haka suka had'a masa wannan tarkon da jami'ar tsaro mace, suka samu nasarar kama shi.
Laminu ya qi bayyana abokan ta'addancin shi da fari sai da ya ci na jaki, ya ga za su masa lahani a banza, shi ne kuwa ya bayyana sunan Isah, nan da nan kuwa aka kira Yaya Musa aka sanar da shi su na buqatar su a station din, dan jin yanda ta kaya.
Hajiya na ta murna ta shirya ta ce ma Yaya Musa su je,a hanya ta kira Hansatu ta sanar da ita an kira su a police station, an ce a samu wani mahimmin bayani, da ya kamata su sani.
Fatan alkhairi ta musu sannan ta ce in su Ameenatu sun taso daga makaranta za su zo.
Su na isa station din aka sanar da su mummunan labarin da ya sanya Hajiya kuka wiwi, da idanun ta, sai lallashin ta ake ta kasa denawa, ta dauki soyayya mai tsafta ta sanya a zuciyar ta wa Isah ashe mutumin banza ne.
Har wajen Laminu aka je da su, ta kalle shi ta ce,
"Allah wadai da samuwar irin ku cikin al'ummar Annabi Muhammad, Allah ya shirya masu hali irin naku, yanzu ka dube ka, yaro kyakkyawa, wa ze ce za ka aikata wannan mugun abu? Yanzu shi abokin naka kuna waya ne? Dan tun da ya tahi bai kire ni ba, wancan karon kuwa ya na kira na"
Cikin jin kunyar dattijuwar Laminu ya ce,
"Hajiya Isah bai dawo wa yanzu gaskiya, dan kuwa abokin harka ta ta saida koken wani inyamuri ya ce ya sanya koken cikin kayan Isah kamar yanda mun ka tsara, kuma an kama Isah, an kulle shekara goma zai yi a kurkuku,"
"Innalillahi wa inna ilaihirraji'una, kaiii wanga yaro kwai baqin mugu, wato abokin naka ka ci wa amana haka? Shi na can daure ga hukumar da bata san sassauci ba, ka mayar min da d'iya ita da zaura (bazawara) ba su da banbanci, Allah ka isar min, Allah ka isar mana abinda yaran nan su ka yi muna"
Kuka sosai Hajiya take faman yi, a haka suka koma gida, Laminu na nan ana shirye shiryen miqa shi ga kotu, asirin shi ya gama tonuwa.
Tun a hanya Hajiya ta kira Hansatu ta ce ta samu abun hawa ta taho,ta wa driver waya ya kawo su Ameenatu gidan ta, cike da damuwa Hansatu ta ce to, bata so ta tsaya tambayar Hajiyan meke faruwa ta waya.
Rurrufe ko ina ta yi, sannan ta leqa gidan 'Yabbuga ta gaishe ta, ta sanar da ita zata gidan su,a hanyar ta ta zuwa bakin titi, ta wuce ta qofar gidan su Lamishi ta ga ana ta shiga da kayan gado.
Ga wata rumfa nan Dan Talo na ta bugawa a qofar gidan da kan shi.
A bakin gate din gidan su aka ajiye ta, ta shiga, bayan ta gaida mai gadi ta wuce cikin gidan.
A parlour ta tadda Yaya Musa da Yaya Abdullahi (Yayan matar Musa) su na zaune cikin jimami, su na ganin ta kowannen su fuskar shi ta sake danyancewa da tausayin ta.
Hajiya kuwa kuka ta sanya, ta dinga yafitar Hansatu da hannu, wajen ta ta nufa ta zauna daf da ita, ta na so ta yi kuka, dan ta san duk abinda ya sanya Hajiya kuka ba qarami bane.
"Hajiya mi ya faru? Mutuwa an kai? Me ya samu Aunty Azizah?"
Ta na fada ta na kallon Abdullahi, da sauri ya kada mata kai, alamar Ah ah,
"Lafiyar ta qlou, ta na Spain ma yanzu haka,"
"To me ya faru?"
Yaya Musa ne ya daure ya labarta mata komai, Hansatu kuka ta sanya, tare da fadin
"Ba zan taba yafe maka ba Isah, soyayyar ka ba ta amfanar da ni komi ba,ka cutar dani, ba iyaka, na hakura, amma sai da ka haɗa da mahaifiya ta, Isah me ta yi maka? In ni ce baka so sai ka sawwaqe min, me mahaifiya ta ta maka?......Hajiya, Hajiya, kin tuna sanda an ka sace su Ameenatu? Tabbas Isah na da hannu a wannan satar"
"Ahh ahh Hansatu, babu kyau zargi, dan kuwa wannan zargi ne, ba ki tabbatar ba"
"Hajiya ina da yaqinin da sa hannun Isah a wannan lamarin saboda tun sannan suke abota shi da Laminu, Hajiya akwai abubuwan da ban sanar da ke ba saboda bana so hankalin ki ya tashi, na dauki alqawarin tunda ni na bijire muku na zabe shi, komi ze yi min zan shanye ba zan fada wa kowa ba, Hajiya Isah na min......"
Nan dai Hansatu ta dage ta sanar ma da mahaifiyar ta komai da Isah yake mata, Hajiya da kowa da ke wajen ya tausaya mata,sannan sun mata faɗa sosai, musamman akan qin sanar da Hajiya tunda ya tafi wancan karon bai neme ta ba, ai da ta sanar tun a sannan da an dau mataki.
"Tau shi kenan yawuce ,Musa ai ka ga da rabon Allah shi hannunta shi can ga hukumar da sun ka fi mu iya hukunci, yanzu yanda za a yi, kai da Abdullahi,ku shirya ku je can wajen shi, ya sakar min d'iya ta, walle ta gama auren shi, ya qarasa shekarar shi goma ya bid'i wata ya aura, ina dalili.
In ya tsaya muku taurin kai, ku faɗa masa za ku yi qarar shi akan abinda ya yi wa hansatu a can, ku tsoratar da d'an nema, ya sake ta dolen shi, yarinya ta da kyawun ta ba zata rasa mashinshini ba"