Sashe 10
A Garin Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Lamishi kuwa komawa ta yi wajen Mai Buruji, ta ce su tafi kawai, dan bata ga alamar Sultana za ta ci wani abu ba.
Dakin mahaifan ta ta nufa ta dinga buga qofar da qarfi, Hajiya Ikee ce ta fito ita da Sultan ,Sultan na ganin yanayin Sultana ya san ba lafiya, cikin hanzari ya nufe ta, tare da qoqarin kama ta ta kwace ta yi gefe,
"Ina daddy? "
"Yanzun Nan ya fita, za su fita government house me ne ne sulty na?"
Da gudu ta fita, ba ko takalmi a qafar ta,
Gwamna ya shiga motar da zata kai shi gidan gwamnati kenan, bayan shi da gaban shi kuwa motoci ne masu bashi kariya, duk sun yi shirin tafiya, ganin Sultana ta fito a birkice cikin kuka, da hargowar kiran sunan shi ne ya sa ya dakatar da su, ya fita,
"Sulty baby me ke faruwa? Ina za ki haka?"
"Daddy, Ina zaka je? Za ka je wajen mutanen can ne da aka qonawa garin su? Daddy pls help them, they really need ur help, daddy su ma fa mutane ne, Kuma a qarqashin kulawar ka suke, me ya sa haka take faruwa da su ne?"
Dan kallon gefe da gefen shi ya yi, ya ga kan mutanen da ke wajen a dan duqe, wasu kuma sun qura musu ido, dan jin amsar da zai bayar, dan kama kafadun ta ya yi, ya goge mata hawayen idan ta, wanda ba su daina zuba ba duk da gogewar da yake ta yi,
"Sulty baby, yanzu haka can zani,ki koma ciki, guards ku tsananta tsaro, kar a bar kowa ya shiga ko ya fita,"
Ya kalli idanun Sultana a lokacin da yake fadin hakan, saboda ba yau ta saba satar jiki ta fice ba,sai dai ya ji labarin ta kai taimako wajen Wanda ibtila'i ya fadawa.
".....ina nufin kar a bar kowa ya fita, a tsananta tsaro"
Ture hannun shi ta yi daga kafadun ta, cikin hawaye ta ce,
"Me ya sa ba za a ba wa mutanen can tsaro ba kamar yanda ake ba wa wannan gidan? Shin masu gadin mu a gidannan nawa ne? Yawan su bai isa ya kare wani qaramin garin ba? Me ya sa ba za a kai taimako wajen da ya dace ba?.."
"Keep quiet sultana and go inside kafin na saba maki,"
Mota ya bude cikin fushi ya shige, nan da nan kuwa aka kunna jiniya, motocin da ke bashi kariya na biye da ta shi.
Qoqarin durqusawa take a wajen ta na kuka, Sultan ya tallabe ta, sai wutsil wutsil take tana son kwacewa, motar su Lawwali ce ta shiga gidan , Lawwali ne a gaba gefen mai zaman banza, yau ce rana ta farko da ya fara dora idanun shi a kan Sultana, yau ce rana ta farko da ya taba jin wani abu mai nauyin gaske, wanda bai taba jin kalar shi ba a gaba daya rayuwar shi ya soki zuciyar shi, wani irin yanayi ne mai dad'i cike da shauki, da wani dandano wanda bai san yanda zai fassara shi ba, har motar ta tsaya,yaran shi suka fara fitar da wasu buhuna da aka nannade aka ma wani irin dauri, wanda komai kwakkwafin ka ba ka Isa gane me ye a cikin daurin ba, Lawwali na zaune a mota, har Sultan ya yi nasarar dauke Sultana wajen Lawwali bai ma sani ba, ganin ta kawai yake a cikin kwayar idon shi, kamar a mafarki ta na zuwa gaban shi,shi kuwa sai zabga murmushi yake.
"Oga an gama,"
A dan daburce ya kalli No 1,
"Tau tau, ya Yi, shiga mu tahi, kun aje dai inda Excellency yacce ko?"
"Eh oga,"
"Tau ya yi, muje"
Kallon inda ya ga Sultana a duqe ana fama da ita ya sake yi, ya dan saki murmushi,
'shege Excellency, dole ya dinga kaffa kaffa da zuwan mu, ashe ya aje kadara mai tsada a gidan shi,'
Cikin zuciyar shi ya ke wannan tunani, har suka fita daga gidan suka dauki hanyar dajin su bai magana ba, No 1 na Masa magana gaba daya hankalin shi ya tafi wajen tunanin sultana.
*********************
"Ki na nufin har yanzu ba su dawo ba? Kuma ki ke zaune a gida ki ke kukan banza ba ki tafi Nemo su ba? In wani abu ya samu yara na Hansatu sai na maki abinda ya fi qarfin mutuwa azaba, ..ba Zaki tashi ki tafi makarantar tasu ba?"
A tsawace ya Yi maganar, cikin rashin kwarin jiki, da ciwon da qirjin ta ke Mata ta miqe ta nabin bango, duhu ya fara, ko yar touch light dinnan ba ta da shi, ga shi ba wuta a unguwar, cikin duhun da ya fara Shiga, ta nemi takalmin ta, ta dauki mayafin ta, ta fita.
Ko Bai Mata fada ba, ta na da niyyar in ta idar da sallah ta fita Neman su, amma me ya sa ba zai Taya ta ba, zai aika ta? Ko su tafi tare, yaran ai Shima na shi ne, zuciyar ta ce ta sanar da ita cewar,
'Hansatu yau ne kike tare da Isa ? Yau ko ke Kika Bata ai ba zai je Nemo ki ba, ballantana yaran da ya tsana, ya ke ganin su na daga cikin silar talaucin ku'
Hawaye ne masu tsananin zafi ke sauka a fuskar ta, a zuciyar ta kuwa wani irin quna ta ke ji, qirjin ta ne ya sake Yi Mata suka, sai da ta damqi saitin zuciyar ta, ta durqusa a tsakiyar hanyar, da mazajen kirki na unguwar na ta fitowa daga masallaci Dan komawa gidajen su.
A hanyar Isa ya same ta,
"Tsayuwar me kike anan?"
Daga Kai ta Yi a wahale ta ce
"Gaba (qirji)na ka Yi min ciyo, Amma yanzu zan tafi"
"Hummmm"
Shi ne kawai abinda ya fadi ya wuce ta ya na kwafa, da kyar take tafiya, ko da ta Isa makarantar sai ta gan ta a rufe, tun daga gate din ma alamu sun nuna ba kowa ciki, Mai gadin wajen ta tambaya, ta Masa kwatancen yaran, ya ce Bai gan su ba yau, ya gane su, yara ne nutsattsu masu hankali, ga qoqari, malaman kan su na yaba qoqarin su.
"Hajiya jiya dai sun taho, Amma yau ban gane su ba,mu na gaisawa da abokina Amadu ai kullum, Amma yau ban gane su ba"
Idanun ta sun fara bushewa, Ina yaran ta Suka tafi to? Su ba masu yawo bane,
"To ko gidan mu Suka tafi?....kaii inaa, tun da suka je sau uku na Hana su ba su sake zuwa ba, yau shekara biyu, to Ina suka tafi?"
Yawo Hansatu ta fara, lungu da saqo na unguwar nan, Bata ga ko ji Wanda ya ga yaran ba.
Hankalin ta ya tashi ya Kai qololuwa, yara har uku, ace sun Yi batan dabo? Ina Suka shiga? A wanne hali suke? A hannun wa suke? Wa ya sace su?
Tunani ne ya Mata yawa, ta yanke jiki ta fadi a qofar gidan Asshibi.........
A GARIN MU
WRITTEN BY HAERMEEBRAEH
PAGE 11:
Ta jima kwance a wajen, mutane ba su kula da ita ba, saboda duhun dare da ya shiga , da misalin takwas da wasu 'yan mintinan mijin Asshibi ya dawo, hasken fitilar motar shi ne ya haska ta, dan haka a tsorace ya fito daga motar, ya na gudun mugayen mutane, masu kwanciya da niyyar neman taimako, daga nan su cutar da mutum.
A hankali ya fita daga motar, sannan ya tsaya daga nesa,inda da an ce kyat ya zura a guje, ko da ya yi ta magana ya ji shiru, wayar shi ya dakko ya haska Hansatu ,ganin alamar gajiya, da wahala a tare da ita, ya tabbata wannan ta na buqatar taimako, da wayar shi ya yi amfani ya kira Asshibi, amsawa ta yi tare da sanya babban hijabi, saman qananan kayan ta, bata fi mintuna biyar ba ta fito.
Bayani ya mata, suka isa gaban Hansatu a tare, Asshibi ta ce,
"Boyar Allah, boyar Allah ko ni tashi dannan, ba ki ganin wajen akwai datti,"
A wahalce murya can qasa, Hansatu ta ce,
"'ya'ya na,....ban gan su ba...tun da suka tafi makaranta ban gan su ba....."
Mijin Asshibi na jin haka ya miqe da ga tsugunon da ya yi, gefe can ya koma ya lalubi wayar shi, ya danna kira, cikin qasa qasa da murya ya ce,
"Kai taho garka ta(qofar gida na) ka dauki matar ka, ga ta nan ta hwadi,"
Komawa ya yi wajen su Hansatu ya na jimami, cikin tausaya wa Asshibi ta tallafe ta suka shiga ciki, kamar kar ta bi Asshibi , amma ba ta da kwarin yin musu da ita.
Ko da suka shiga, kunun da ta dama take sirki da shi, shi ta sakawa Hansatu a babban cup, ta saka sigar da madara ta juya sosai, ta kafa mata a baki, Hansatu na jin abu da sigar, ga qamshin kayan yaji, sai yunwar ta ta murda, cikin ta ya bada wani irin sauti da qara.
Ba bata lokaci ta kurba sau biyu, za tai na ukun ta tuno da yaran ta, shin a wanne hali suke ciki, sun ci abinci kuwa, a wanne muhalli suke, su na raye kuwa?
Wani irin kuka ne da tunda aka haife ta bata taɓa yin irin shi ba, ya kwace mata, Asshibi kuwa hawaye ne kawai na tausayi ke saukar mata,ganin hawayen ta kuwa tashin hankalin mijin tane, dan haka dakin shi ya shiga, wayar Isa ya sake kira, cikin fada ya ce ya je ya dauke matar shi, ko ya sanar da ita ina yaran suke.
"To dan tonanniya, gani nan garkar ka, ku turo ta mu tafi,"
Komawa parlour ya Yi, ya ya na Basu hakuri, sai suka ji ana buga qofar,da sauri mijin Asshibi ya fita dan ganin wane.
Sun dan jima da Isa suna tattaunawa kafin ya koma,
"Wani mutum na ya taho, ya na neman Mata tai, yanda ya yi min bayani, ina kyautata zaton ita ce wagga, raka ta can garka"
Da kyar Hansatu ta miqe, cikin dan saka ran wataqila yaran sun koma gida.
Dakin mahaifan ta ta nufa ta dinga buga qofar da qarfi, Hajiya Ikee ce ta fito ita da Sultan ,Sultan na ganin yanayin Sultana ya san ba lafiya, cikin hanzari ya nufe ta, tare da qoqarin kama ta ta kwace ta yi gefe,
"Ina daddy? "
"Yanzun Nan ya fita, za su fita government house me ne ne sulty na?"
Da gudu ta fita, ba ko takalmi a qafar ta,
Gwamna ya shiga motar da zata kai shi gidan gwamnati kenan, bayan shi da gaban shi kuwa motoci ne masu bashi kariya, duk sun yi shirin tafiya, ganin Sultana ta fito a birkice cikin kuka, da hargowar kiran sunan shi ne ya sa ya dakatar da su, ya fita,
"Sulty baby me ke faruwa? Ina za ki haka?"
"Daddy, Ina zaka je? Za ka je wajen mutanen can ne da aka qonawa garin su? Daddy pls help them, they really need ur help, daddy su ma fa mutane ne, Kuma a qarqashin kulawar ka suke, me ya sa haka take faruwa da su ne?"
Dan kallon gefe da gefen shi ya yi, ya ga kan mutanen da ke wajen a dan duqe, wasu kuma sun qura musu ido, dan jin amsar da zai bayar, dan kama kafadun ta ya yi, ya goge mata hawayen idan ta, wanda ba su daina zuba ba duk da gogewar da yake ta yi,
"Sulty baby, yanzu haka can zani,ki koma ciki, guards ku tsananta tsaro, kar a bar kowa ya shiga ko ya fita,"
Ya kalli idanun Sultana a lokacin da yake fadin hakan, saboda ba yau ta saba satar jiki ta fice ba,sai dai ya ji labarin ta kai taimako wajen Wanda ibtila'i ya fadawa.
".....ina nufin kar a bar kowa ya fita, a tsananta tsaro"
Ture hannun shi ta yi daga kafadun ta, cikin hawaye ta ce,
"Me ya sa ba za a ba wa mutanen can tsaro ba kamar yanda ake ba wa wannan gidan? Shin masu gadin mu a gidannan nawa ne? Yawan su bai isa ya kare wani qaramin garin ba? Me ya sa ba za a kai taimako wajen da ya dace ba?.."
"Keep quiet sultana and go inside kafin na saba maki,"
Mota ya bude cikin fushi ya shige, nan da nan kuwa aka kunna jiniya, motocin da ke bashi kariya na biye da ta shi.
Qoqarin durqusawa take a wajen ta na kuka, Sultan ya tallabe ta, sai wutsil wutsil take tana son kwacewa, motar su Lawwali ce ta shiga gidan , Lawwali ne a gaba gefen mai zaman banza, yau ce rana ta farko da ya fara dora idanun shi a kan Sultana, yau ce rana ta farko da ya taba jin wani abu mai nauyin gaske, wanda bai taba jin kalar shi ba a gaba daya rayuwar shi ya soki zuciyar shi, wani irin yanayi ne mai dad'i cike da shauki, da wani dandano wanda bai san yanda zai fassara shi ba, har motar ta tsaya,yaran shi suka fara fitar da wasu buhuna da aka nannade aka ma wani irin dauri, wanda komai kwakkwafin ka ba ka Isa gane me ye a cikin daurin ba, Lawwali na zaune a mota, har Sultan ya yi nasarar dauke Sultana wajen Lawwali bai ma sani ba, ganin ta kawai yake a cikin kwayar idon shi, kamar a mafarki ta na zuwa gaban shi,shi kuwa sai zabga murmushi yake.
"Oga an gama,"
A dan daburce ya kalli No 1,
"Tau tau, ya Yi, shiga mu tahi, kun aje dai inda Excellency yacce ko?"
"Eh oga,"
"Tau ya yi, muje"
Kallon inda ya ga Sultana a duqe ana fama da ita ya sake yi, ya dan saki murmushi,
'shege Excellency, dole ya dinga kaffa kaffa da zuwan mu, ashe ya aje kadara mai tsada a gidan shi,'
Cikin zuciyar shi ya ke wannan tunani, har suka fita daga gidan suka dauki hanyar dajin su bai magana ba, No 1 na Masa magana gaba daya hankalin shi ya tafi wajen tunanin sultana.
*********************
"Ki na nufin har yanzu ba su dawo ba? Kuma ki ke zaune a gida ki ke kukan banza ba ki tafi Nemo su ba? In wani abu ya samu yara na Hansatu sai na maki abinda ya fi qarfin mutuwa azaba, ..ba Zaki tashi ki tafi makarantar tasu ba?"
A tsawace ya Yi maganar, cikin rashin kwarin jiki, da ciwon da qirjin ta ke Mata ta miqe ta nabin bango, duhu ya fara, ko yar touch light dinnan ba ta da shi, ga shi ba wuta a unguwar, cikin duhun da ya fara Shiga, ta nemi takalmin ta, ta dauki mayafin ta, ta fita.
Ko Bai Mata fada ba, ta na da niyyar in ta idar da sallah ta fita Neman su, amma me ya sa ba zai Taya ta ba, zai aika ta? Ko su tafi tare, yaran ai Shima na shi ne, zuciyar ta ce ta sanar da ita cewar,
'Hansatu yau ne kike tare da Isa ? Yau ko ke Kika Bata ai ba zai je Nemo ki ba, ballantana yaran da ya tsana, ya ke ganin su na daga cikin silar talaucin ku'
Hawaye ne masu tsananin zafi ke sauka a fuskar ta, a zuciyar ta kuwa wani irin quna ta ke ji, qirjin ta ne ya sake Yi Mata suka, sai da ta damqi saitin zuciyar ta, ta durqusa a tsakiyar hanyar, da mazajen kirki na unguwar na ta fitowa daga masallaci Dan komawa gidajen su.
A hanyar Isa ya same ta,
"Tsayuwar me kike anan?"
Daga Kai ta Yi a wahale ta ce
"Gaba (qirji)na ka Yi min ciyo, Amma yanzu zan tafi"
"Hummmm"
Shi ne kawai abinda ya fadi ya wuce ta ya na kwafa, da kyar take tafiya, ko da ta Isa makarantar sai ta gan ta a rufe, tun daga gate din ma alamu sun nuna ba kowa ciki, Mai gadin wajen ta tambaya, ta Masa kwatancen yaran, ya ce Bai gan su ba yau, ya gane su, yara ne nutsattsu masu hankali, ga qoqari, malaman kan su na yaba qoqarin su.
"Hajiya jiya dai sun taho, Amma yau ban gane su ba,mu na gaisawa da abokina Amadu ai kullum, Amma yau ban gane su ba"
Idanun ta sun fara bushewa, Ina yaran ta Suka tafi to? Su ba masu yawo bane,
"To ko gidan mu Suka tafi?....kaii inaa, tun da suka je sau uku na Hana su ba su sake zuwa ba, yau shekara biyu, to Ina suka tafi?"
Yawo Hansatu ta fara, lungu da saqo na unguwar nan, Bata ga ko ji Wanda ya ga yaran ba.
Hankalin ta ya tashi ya Kai qololuwa, yara har uku, ace sun Yi batan dabo? Ina Suka shiga? A wanne hali suke? A hannun wa suke? Wa ya sace su?
Tunani ne ya Mata yawa, ta yanke jiki ta fadi a qofar gidan Asshibi.........
A GARIN MU
WRITTEN BY HAERMEEBRAEH
PAGE 11:
Ta jima kwance a wajen, mutane ba su kula da ita ba, saboda duhun dare da ya shiga , da misalin takwas da wasu 'yan mintinan mijin Asshibi ya dawo, hasken fitilar motar shi ne ya haska ta, dan haka a tsorace ya fito daga motar, ya na gudun mugayen mutane, masu kwanciya da niyyar neman taimako, daga nan su cutar da mutum.
A hankali ya fita daga motar, sannan ya tsaya daga nesa,inda da an ce kyat ya zura a guje, ko da ya yi ta magana ya ji shiru, wayar shi ya dakko ya haska Hansatu ,ganin alamar gajiya, da wahala a tare da ita, ya tabbata wannan ta na buqatar taimako, da wayar shi ya yi amfani ya kira Asshibi, amsawa ta yi tare da sanya babban hijabi, saman qananan kayan ta, bata fi mintuna biyar ba ta fito.
Bayani ya mata, suka isa gaban Hansatu a tare, Asshibi ta ce,
"Boyar Allah, boyar Allah ko ni tashi dannan, ba ki ganin wajen akwai datti,"
A wahalce murya can qasa, Hansatu ta ce,
"'ya'ya na,....ban gan su ba...tun da suka tafi makaranta ban gan su ba....."
Mijin Asshibi na jin haka ya miqe da ga tsugunon da ya yi, gefe can ya koma ya lalubi wayar shi, ya danna kira, cikin qasa qasa da murya ya ce,
"Kai taho garka ta(qofar gida na) ka dauki matar ka, ga ta nan ta hwadi,"
Komawa ya yi wajen su Hansatu ya na jimami, cikin tausaya wa Asshibi ta tallafe ta suka shiga ciki, kamar kar ta bi Asshibi , amma ba ta da kwarin yin musu da ita.
Ko da suka shiga, kunun da ta dama take sirki da shi, shi ta sakawa Hansatu a babban cup, ta saka sigar da madara ta juya sosai, ta kafa mata a baki, Hansatu na jin abu da sigar, ga qamshin kayan yaji, sai yunwar ta ta murda, cikin ta ya bada wani irin sauti da qara.
Ba bata lokaci ta kurba sau biyu, za tai na ukun ta tuno da yaran ta, shin a wanne hali suke ciki, sun ci abinci kuwa, a wanne muhalli suke, su na raye kuwa?
Wani irin kuka ne da tunda aka haife ta bata taɓa yin irin shi ba, ya kwace mata, Asshibi kuwa hawaye ne kawai na tausayi ke saukar mata,ganin hawayen ta kuwa tashin hankalin mijin tane, dan haka dakin shi ya shiga, wayar Isa ya sake kira, cikin fada ya ce ya je ya dauke matar shi, ko ya sanar da ita ina yaran suke.
"To dan tonanniya, gani nan garkar ka, ku turo ta mu tafi,"
Komawa parlour ya Yi, ya ya na Basu hakuri, sai suka ji ana buga qofar,da sauri mijin Asshibi ya fita dan ganin wane.
Sun dan jima da Isa suna tattaunawa kafin ya koma,
"Wani mutum na ya taho, ya na neman Mata tai, yanda ya yi min bayani, ina kyautata zaton ita ce wagga, raka ta can garka"
Da kyar Hansatu ta miqe, cikin dan saka ran wataqila yaran sun koma gida.