Sashe 24
A Garin Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wata iriyar siririyar dariya mai sauti ya saki, tare da duqar da kan shi, hakan ba karamin kyau ya yi wa sultana ba, zuciyar ta ta ji ta tafi wajen shi gaba daya, kafe shi ta yi da idanu, cikin yin qasa da murya yace,
"Ko ran Ran ta ya dade za ta iya sammin Lambar wayar ta, saboda in ta na buqata ta se na dawo?"
Miqa masa hannu ta yi, ta na nufin ya bata wayar shi, hannun shi ya miqa, sauran kadan hannayen su su hadu,da sauri ta janye hannun ta cike da shagwaba ta ce,
"Wayar ka fa za ka bani"
Shi kuma 'yar dariyar da ke tafiya da ita ya yi, ya ce,
"Ohh na zaci gaisawa za mu yi"
Hannu ya sa ya zari wayar a aljihun shi, ta bi qirjin shi da kallo, yanda rigar ta zauna a jikin shi, kamar a jiki aka dinka ya mata kyau, yawo ya yi da wayar a gaban idanun ta ya na murmushi, tare da lumshe idanun shi.
"A gaskiya ran ki shi dade in ki na yi min irin wanga kallo, sai ke gano muni na da ni ke ta boyewa kar ki gani"
Sultana ta gama kamuwa da matsananciyar kunya ,kasa amsar wayar ta yi, sai shi ya zare tata a hannun ta ya sanya lambobin shi ya danna kira, ta ta No ya yi saving, sannan ya miqa mata wayar ta, ya kulle motar ya raka ta har office, sannan ya tafi.
Bai tsaya a ko ina ba sai bakin titi, tun kan ya isa ya yi waya ya sanar da su inda za su dauke shi, ya ɗan jira su kadan kafin suka isa, mota ya shiga suka ja Sai gidan Gwamna Halliru......
*Dan Allah ku dan min hakuri da wannan, ban sani ba ko za a samu ci gaba nan kusa na yi baqi na yi busy sosai, ko wanan ma da kyar na samu nayi*
A GARIN MU
WRITTEN BY HAERMEEBRAERH
PAGE 22:
A mota ya bar su, zai shiga No 1 ya yunqura zai bi shi, kallon shi Lawwali ya yi, cikin hade girar shi,ya ce,
"Ina zaka je?"
Dan yaqe ya yi, sannan ya koma ya zauna, qasan zuciyar shi baqqiqirin a ganin shi ai ko ba a shiga da kowa ba, an shiga da shi, tunda shi ne wanda ke bi ma Ogan nasu, kuma shi ke kula da can daji yanzu.
Lawwali bai saki fuskar shi ba har ya shige gidan, bai jima ba sosai ya dawo dauke da jaka, ya ajiye suka tada mota, sai gidan shi, ya so ya leqa dajin ya ga ya abubuwa ke tafiya, dan yanzu ba ya so a maimaita sakin wani da suka kwamushe, asiri ya tonu,duk da ba wai tsoro yake ji dan an san da zaman su ba, ya sani yayi gagarar da zai iya ji da dik wata tarzomar mahukunta, a shirye yake a yi uwar watsi ko a mutu ko ai rai kawai.
Zaune suke a parlour'n shi, su na kasafta kudin, kamata ya yi a ce in sun raba kudin daidai su shiddan kowa zai samu kusan miliyan 42,amma sai suka yi kasafin kamar kashin dankali, na sama ya danne na qasa, Gwamna shi ne ya fi kwasar kaso mai tsoka, sannan Lawwali, sai kuma suka ware kudin kula da maboyar su, abinci,ruwa, man da za a saka a mota, da abubuwan yau da kullum, kudin shigo da makamai dama a wuyan gwamna yake, ,No 1 na ta jira ya ji kason shi shima ya dara na qasa da shi, sai ya ga an bashi miliyon ashirin, yaqe ya yi ya karba, ya na ta godiya, kamar babu komai a qasan zuciyar shi .
Sauran yaran Lawwali kuwa murna kamar za su shide, ba su taba kama kudi masu kauri haka ba, babban abin takaicin shi ne, su na samun kuɗi dan samu, amma cin su na musu wahala, saboda idanun mutane, kuma sun fi yin rayuwa a daji, duk da cewar wasun su na da iyalai, har da iyaye, amma su na tsoron fitar da dukiyar su ci, (meye amfanin dukiyar da ba za ka ci ba? An kashe mutane a banza, ba a samu rayuwar jin dadi ba, an sace mutane a banza ba a yi ninqaya da dukiyar ba cikin kwanciyar hankali, ga tsoro, ga fargaba, ga zunubin wanda ya kashe mumini akan su, mu yawaita tuna cewar Allah yace duk wanda ya kashe munini kamar ya kashe duka duniya ne, kuma wanda ya raya mumini daya kamar ya raya duka duniya ne,sannan wanda ya kashe mumini da gangan, sakamakon shi jahannama ne,zai dawwama a cikin ta,ba fita, Allah ka tsare mu ka kare mu, ya ilahi me ne jin dadi a kashe kiyashi ma balle mutum? In ya mutu kai me za ka zauna ka yi a duniyar? Ba ku tunanin yanzu ku na gama kashe mutum kuma ku bingire ku mace? Me ka/ki ka tanada a ranar lahira da zai kare ki/ka daga shiga jahannama? Me za ku ce wa Allah a ranar qiyama? Shin wutar ita kuka fi so a inda za a dawwama ba fita, ko kuma talauci da quncin rayuwa a duniya, lahira a samu aljannah madawwamiya, ba fita, ba wahala, ba qunci, ba azaba, sai zallar ni'imar Allah, da jin dadi? Zabi ya na gare mu, tare da yawaita addu'a, Allah ya sa qaddarar mutuwar kowa ba ta hannun mu, domin wasu Allah ya rubuta su ne ajalin wasu, shi yasa suke kashe kashen nan, Allah ya nesan ta mu da ga aikata kisan kai, ameen)
Su na tsaka da murna Lawwali ya ji wayar shi na qara, dubawa ya yi ya ga sunan Sultana da ya yi Saving da 'Ran ki shi dade' da sauri ya dauka, tare da yi masu alamar su yi shiru, ko motsi wajen bai sake yi ba, sallama ya yi, ya ce,
"Ran ki shi dade na neman Lawwali ne?"
Cikin dakewa ya yi maganar saboda idon yaran shi, daga can Sultana sai ta ji ba dadi, domin ba haka ta so ba, ba ta san me ta zata zai fara fadi ba, amma ta sa a ran ta he is going to say something sweet to her ,musamman tunda shi ya iya tsara kalamai, ita ma dakewa ta yi, ta fito masa a oganniyar shi, ta ce,
"Ina ka shiga tun dazu na gama ina jiran ka?"
Miqewa ya yi, tare da dan duwaqa ya na bata hakuri, har cikin ran shi bai so ta gama bai koma ba, cikin sauri ya mu su alama, nan da nan kuwa kowa ya kwashe kudin shi, da shirin su suka zo, kowa ya zo da inda zai saka na shi, su na gama kwashewa suka fita, ya rufe gidan shi, suka tafi.
Nesa da NGO din suka aje shi ya dau adaidata sahu, dubu guda ya damqa masa ya sauka a hanzarce ya shiga ciki.
Ko da ya isa a zaton shi zai gan ta a bakin mota, sai ya ga ba kowa, mota na nan yanda ya barta, sai zafi da ta dauka, ciki ya shiga ya ga duk mutanen wajen sun tafi, sai ita kadai, ta kwantar da kan ta a jikin kujera.
Kallon ta ya ci gaba da yi har da sanya hannun shi a qirji, ya na murmushi, wai fa gajiya ta yi a hakan, office dik AC, kujera kamar an yi ta da soson katifa, amma ta nuna ta gaji saboda ba a saba da wahala ba, sai ya tuna farkon zuwan su wajen, har suka koma da fara'a a fuskar ta,
'to ko dai dadewa ta ce musabbabin bata ran ta?'
"In ka gama kallon nawa za ka iya kai ni gida?"
A dan firgice ya ce,
"Na'am?"
Miqewa ta yi ta zagaye shi, tana dan tura baki, tare da ɗaukan jakar ta da wayar ta, ta fara tafiya, wurga masa key din offices din ta yi, ta ce,
"Ka rurrufe ko ina, this will serve as ur punishment, na tafiya ka dade ba tare da ka kira Ni ba,"
Shan gaban ta ya yi, ya tsaya, tare da kama kunnuwan ta duka biyun da hannayen shi, cikin murya irin ta jaruman maza da ware idanun shi fess akan ta ya ce,
"Habaa Sultyn Daddy, ki yahe ma wanga yaron na ki, mai gadin ki, kuma drivern ki, indai hukunci ne ki ban kowanne iri na Zan dauka, amma ba zan dauki hushin ki ba, murmushin ki kamar hasken da ke haska min hanya ne, fushin ki duhu ne a gare ni, so ki ke in ta tahiya cikin duhu mu fada rami? Ko..."
Muryar ta can qasan maqoshi ta ce,
"Shiiiiii, ya isa haka, ni ba fushi nake ba,da na ga baka dawo bane sai na ji...."
Shiru ta yi, tare da cizon leben ta na qasa, wanda hakan dabi'ar ta ne, da sauri ta bar wajen, Lawwali kuwa ji ya yi wadannan kalaman nata sun fi maqudan kudin da ya samu a yau mahimmanci, duk da ba ta qarasa kalaman taba, ya kula da cewar ba ta son ya yi nesa da ita ne, cikin sauri ya rurrufe ko ina, ya bi bayan ta, juyawa ta yi, ta qi yarda su hada ido, har ya je gaban ta ya bude mata mota bata kalle shi ba, kuma bata dena cizar leben ta ba, sannan murmushin ta bai gushe ba.
Ko a mota ma ta kasa daga ido ta kalle shi ta madubi, shi kuwa idanun shi ya kasa barin fusakar ta da ta kawar gefe, mamakin irin kunyar ta yake yi, kamar ba wayayyiya ba, kamar bata yi karatu a qasar waje ba, kamar shekarun ta ba su haura ashirin da biyar ba. (Kunya halittace, ta wani ta fi ta wani, kunya ado ce, wanda ba shi da ita ya yi hasara, kunya ni'ima ce, wanda aka azurta da ita ya dace)
Ko da suka isa gida kafin ya fita ya bude mata, ta fara qoqarin budewa, ji ta yi qofar a kulle, daga ido ta yi ta kalle shi, su na hada ido ya kashe mata ido daya, dariya ta saki mai sanyi, shi ma haka,
"Ko ran Ran ta ya dade za ta iya sammin Lambar wayar ta, saboda in ta na buqata ta se na dawo?"
Miqa masa hannu ta yi, ta na nufin ya bata wayar shi, hannun shi ya miqa, sauran kadan hannayen su su hadu,da sauri ta janye hannun ta cike da shagwaba ta ce,
"Wayar ka fa za ka bani"
Shi kuma 'yar dariyar da ke tafiya da ita ya yi, ya ce,
"Ohh na zaci gaisawa za mu yi"
Hannu ya sa ya zari wayar a aljihun shi, ta bi qirjin shi da kallo, yanda rigar ta zauna a jikin shi, kamar a jiki aka dinka ya mata kyau, yawo ya yi da wayar a gaban idanun ta ya na murmushi, tare da lumshe idanun shi.
"A gaskiya ran ki shi dade in ki na yi min irin wanga kallo, sai ke gano muni na da ni ke ta boyewa kar ki gani"
Sultana ta gama kamuwa da matsananciyar kunya ,kasa amsar wayar ta yi, sai shi ya zare tata a hannun ta ya sanya lambobin shi ya danna kira, ta ta No ya yi saving, sannan ya miqa mata wayar ta, ya kulle motar ya raka ta har office, sannan ya tafi.
Bai tsaya a ko ina ba sai bakin titi, tun kan ya isa ya yi waya ya sanar da su inda za su dauke shi, ya ɗan jira su kadan kafin suka isa, mota ya shiga suka ja Sai gidan Gwamna Halliru......
*Dan Allah ku dan min hakuri da wannan, ban sani ba ko za a samu ci gaba nan kusa na yi baqi na yi busy sosai, ko wanan ma da kyar na samu nayi*
A GARIN MU
WRITTEN BY HAERMEEBRAERH
PAGE 22:
A mota ya bar su, zai shiga No 1 ya yunqura zai bi shi, kallon shi Lawwali ya yi, cikin hade girar shi,ya ce,
"Ina zaka je?"
Dan yaqe ya yi, sannan ya koma ya zauna, qasan zuciyar shi baqqiqirin a ganin shi ai ko ba a shiga da kowa ba, an shiga da shi, tunda shi ne wanda ke bi ma Ogan nasu, kuma shi ke kula da can daji yanzu.
Lawwali bai saki fuskar shi ba har ya shige gidan, bai jima ba sosai ya dawo dauke da jaka, ya ajiye suka tada mota, sai gidan shi, ya so ya leqa dajin ya ga ya abubuwa ke tafiya, dan yanzu ba ya so a maimaita sakin wani da suka kwamushe, asiri ya tonu,duk da ba wai tsoro yake ji dan an san da zaman su ba, ya sani yayi gagarar da zai iya ji da dik wata tarzomar mahukunta, a shirye yake a yi uwar watsi ko a mutu ko ai rai kawai.
Zaune suke a parlour'n shi, su na kasafta kudin, kamata ya yi a ce in sun raba kudin daidai su shiddan kowa zai samu kusan miliyan 42,amma sai suka yi kasafin kamar kashin dankali, na sama ya danne na qasa, Gwamna shi ne ya fi kwasar kaso mai tsoka, sannan Lawwali, sai kuma suka ware kudin kula da maboyar su, abinci,ruwa, man da za a saka a mota, da abubuwan yau da kullum, kudin shigo da makamai dama a wuyan gwamna yake, ,No 1 na ta jira ya ji kason shi shima ya dara na qasa da shi, sai ya ga an bashi miliyon ashirin, yaqe ya yi ya karba, ya na ta godiya, kamar babu komai a qasan zuciyar shi .
Sauran yaran Lawwali kuwa murna kamar za su shide, ba su taba kama kudi masu kauri haka ba, babban abin takaicin shi ne, su na samun kuɗi dan samu, amma cin su na musu wahala, saboda idanun mutane, kuma sun fi yin rayuwa a daji, duk da cewar wasun su na da iyalai, har da iyaye, amma su na tsoron fitar da dukiyar su ci, (meye amfanin dukiyar da ba za ka ci ba? An kashe mutane a banza, ba a samu rayuwar jin dadi ba, an sace mutane a banza ba a yi ninqaya da dukiyar ba cikin kwanciyar hankali, ga tsoro, ga fargaba, ga zunubin wanda ya kashe mumini akan su, mu yawaita tuna cewar Allah yace duk wanda ya kashe munini kamar ya kashe duka duniya ne, kuma wanda ya raya mumini daya kamar ya raya duka duniya ne,sannan wanda ya kashe mumini da gangan, sakamakon shi jahannama ne,zai dawwama a cikin ta,ba fita, Allah ka tsare mu ka kare mu, ya ilahi me ne jin dadi a kashe kiyashi ma balle mutum? In ya mutu kai me za ka zauna ka yi a duniyar? Ba ku tunanin yanzu ku na gama kashe mutum kuma ku bingire ku mace? Me ka/ki ka tanada a ranar lahira da zai kare ki/ka daga shiga jahannama? Me za ku ce wa Allah a ranar qiyama? Shin wutar ita kuka fi so a inda za a dawwama ba fita, ko kuma talauci da quncin rayuwa a duniya, lahira a samu aljannah madawwamiya, ba fita, ba wahala, ba qunci, ba azaba, sai zallar ni'imar Allah, da jin dadi? Zabi ya na gare mu, tare da yawaita addu'a, Allah ya sa qaddarar mutuwar kowa ba ta hannun mu, domin wasu Allah ya rubuta su ne ajalin wasu, shi yasa suke kashe kashen nan, Allah ya nesan ta mu da ga aikata kisan kai, ameen)
Su na tsaka da murna Lawwali ya ji wayar shi na qara, dubawa ya yi ya ga sunan Sultana da ya yi Saving da 'Ran ki shi dade' da sauri ya dauka, tare da yi masu alamar su yi shiru, ko motsi wajen bai sake yi ba, sallama ya yi, ya ce,
"Ran ki shi dade na neman Lawwali ne?"
Cikin dakewa ya yi maganar saboda idon yaran shi, daga can Sultana sai ta ji ba dadi, domin ba haka ta so ba, ba ta san me ta zata zai fara fadi ba, amma ta sa a ran ta he is going to say something sweet to her ,musamman tunda shi ya iya tsara kalamai, ita ma dakewa ta yi, ta fito masa a oganniyar shi, ta ce,
"Ina ka shiga tun dazu na gama ina jiran ka?"
Miqewa ya yi, tare da dan duwaqa ya na bata hakuri, har cikin ran shi bai so ta gama bai koma ba, cikin sauri ya mu su alama, nan da nan kuwa kowa ya kwashe kudin shi, da shirin su suka zo, kowa ya zo da inda zai saka na shi, su na gama kwashewa suka fita, ya rufe gidan shi, suka tafi.
Nesa da NGO din suka aje shi ya dau adaidata sahu, dubu guda ya damqa masa ya sauka a hanzarce ya shiga ciki.
Ko da ya isa a zaton shi zai gan ta a bakin mota, sai ya ga ba kowa, mota na nan yanda ya barta, sai zafi da ta dauka, ciki ya shiga ya ga duk mutanen wajen sun tafi, sai ita kadai, ta kwantar da kan ta a jikin kujera.
Kallon ta ya ci gaba da yi har da sanya hannun shi a qirji, ya na murmushi, wai fa gajiya ta yi a hakan, office dik AC, kujera kamar an yi ta da soson katifa, amma ta nuna ta gaji saboda ba a saba da wahala ba, sai ya tuna farkon zuwan su wajen, har suka koma da fara'a a fuskar ta,
'to ko dai dadewa ta ce musabbabin bata ran ta?'
"In ka gama kallon nawa za ka iya kai ni gida?"
A dan firgice ya ce,
"Na'am?"
Miqewa ta yi ta zagaye shi, tana dan tura baki, tare da ɗaukan jakar ta da wayar ta, ta fara tafiya, wurga masa key din offices din ta yi, ta ce,
"Ka rurrufe ko ina, this will serve as ur punishment, na tafiya ka dade ba tare da ka kira Ni ba,"
Shan gaban ta ya yi, ya tsaya, tare da kama kunnuwan ta duka biyun da hannayen shi, cikin murya irin ta jaruman maza da ware idanun shi fess akan ta ya ce,
"Habaa Sultyn Daddy, ki yahe ma wanga yaron na ki, mai gadin ki, kuma drivern ki, indai hukunci ne ki ban kowanne iri na Zan dauka, amma ba zan dauki hushin ki ba, murmushin ki kamar hasken da ke haska min hanya ne, fushin ki duhu ne a gare ni, so ki ke in ta tahiya cikin duhu mu fada rami? Ko..."
Muryar ta can qasan maqoshi ta ce,
"Shiiiiii, ya isa haka, ni ba fushi nake ba,da na ga baka dawo bane sai na ji...."
Shiru ta yi, tare da cizon leben ta na qasa, wanda hakan dabi'ar ta ne, da sauri ta bar wajen, Lawwali kuwa ji ya yi wadannan kalaman nata sun fi maqudan kudin da ya samu a yau mahimmanci, duk da ba ta qarasa kalaman taba, ya kula da cewar ba ta son ya yi nesa da ita ne, cikin sauri ya rurrufe ko ina, ya bi bayan ta, juyawa ta yi, ta qi yarda su hada ido, har ya je gaban ta ya bude mata mota bata kalle shi ba, kuma bata dena cizar leben ta ba, sannan murmushin ta bai gushe ba.
Ko a mota ma ta kasa daga ido ta kalle shi ta madubi, shi kuwa idanun shi ya kasa barin fusakar ta da ta kawar gefe, mamakin irin kunyar ta yake yi, kamar ba wayayyiya ba, kamar bata yi karatu a qasar waje ba, kamar shekarun ta ba su haura ashirin da biyar ba. (Kunya halittace, ta wani ta fi ta wani, kunya ado ce, wanda ba shi da ita ya yi hasara, kunya ni'ima ce, wanda aka azurta da ita ya dace)
Ko da suka isa gida kafin ya fita ya bude mata, ta fara qoqarin budewa, ji ta yi qofar a kulle, daga ido ta yi ta kalle shi, su na hada ido ya kashe mata ido daya, dariya ta saki mai sanyi, shi ma haka,