Sashe 44
A Garin Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ran Lamishi ya baci, nan da nan kuwa magana ta girmama, aka hau fada, sai ga tone tonen asiri ana ta yi, akan gulmammakin da akai ta kitsawa anan ne matar Yahai taji maganar da daga ita sai 'Yabbuga suka yi ta, ya akai Lamishi da baquwar da bata fi watanni hudu da su ba ta sani?
Ai kuwa sai fad'a ya koma kan 'Yabbuga da Matar Yahai, nan fa suma suka hau nasu maganganun, abu fa ya qi ci ya qi cinyewa, har da dambe.
Asshibi naso ta raba amma abu ya fi qarfin ta, cikin sa'a kuwa Matar Yahai ta samu d'aga 'yabbuga ta maka da qasa, ta haye cikin ta, ta dinga kirba,sai da ta farfashewa 'Yabbuga baki sannan Asshibi da Mai buruji suka samu d'aga ta a jikin 'Yabbuga, Lamishi ta ji dadin hakan, dan kuwa ko ba komai an koya ma 'Yabbuga hankali, ta na miqewa ta hau kade jikin ta ta na fadin,
"Baki daki banza ba, zaki gani, har gida se hukuma ta kama min ke, bari dan Jummaa ya dawo"
"Baku da wanan azziqin da alfamar a Nigeria,"
"Haka kin ka ce ko?"
"Na hwadi,"
Haka nan suka yi ta sa'in sa har aka kirayi magariba suka tafi gidajen su, Asshibi kuwa gidan su Lamishi ta nufa suka yi ta gulmar sauran.
**************************
"Excellency gamu asibiti da shi, ba shi da halin magana shi yassa"
"Mi ya same shi halan?"
"Allah shi taimake ka wasa ta an ka yi, shi na ya samu rauni"
"Allah ya bashi lahiya, ka na ji na ba, wannan ajiyar ina so a qara bata tsaro, gaf nake nai amfani da ita, ba na so Ogan ku ya san me ke faruwa, ka gane?"
"Na gane Excellency,"
"Tau ya yi, ka gaishe shi in ya hwalka"
"Zai ji ranka shi dade "
Bayan sun gama wayar ne, ya sanar da No 1 duk yadda suka yi da gwamna, cikin jin jiki ya ke d'aga kai, alamar ya ji.
Cikin ran shi kuwa ya na tunanin kalar azabar da zai ganawa Mubaraka, duk abinda ya tunano sai ya ga ya yi kadan, qarshe saboda tsananin ciwon kan da yake ji, dole sai hakura ya yi da tunanin zuwa wani lokacin.
*Hummm anya ka daku kuwa No 1???*
💅🏻 *A GARIN MU* 💅🏻
BY HAERMEEBRAERH
PAGE 35:
Satin su Sultana biyu kafin Gwamna ya bata izin fita daga gidan gwamnati, a wannan satikan kuwa duk ta rame, ta yi zuru-zuru rashin ganin Lawwali da bata yi ya fitar da ita daga hayyacin ta, ita kan ta, ta na mamakin kalar soyayyar da take masa, anya wannan soyayyar ba zata zama ajalin ta ba kuwa?
Masu tsaron lafiyar ta ta dinga kallo daya bayan daya, sanda ta fito tafiya,dukkan su kamar sabbi ne, bata taba ganin wasun su ba.
Juyawa ta yi, ta kalli Hajiya Ikee da ta ke zuba mata murmushi, ta kalli Sultan wanda ke kallon ta da tsantsar kulawa da tausaya wa, ta ce,
"Ina driver na?"
Hade fuska Hajiya Ikee ta yi, sannan ta bude baki zata yi magana, al'ajabi ya sanya ta hadiye maganar ta.
Lawwali ne cikin uniform din shi, wanda da gani ka san sabbi ne, sai dai wadannan ba fari bane, ash color ne, da ratsin baqi a jikin riga da wandon kayan, duk yanda zan fasalta maku kalar kyaun da ya yi ba zai yu ba, sai ido ya gan shi kawai.
Hawaye ne kawai ke tsartuwa daga idon Sultana, a lokaci daya kuma ta na dariyar farin ciki, da murnar ganin jarumin maza Auwal din ta.
Ita kan ta Hajiya Ikee kasa magana ta yi tsabar kwarjinin da ya yi mata, Sultan kuwa zuwa ya yi ya daki kafadar Lawwali, tare da matsa ta, ya na zuba murmushi,
"Me na fada maka game da sa min qauna kuka?"
Lawwali dan duqawa ya yi, sannan ya ce,
"A min ahuwa ran ka shi dade, an min iyaka da shigowa gidan nan ,yau ma Umarni uwar daki na tabban, ta ce na taho na maishe ta gida, in ban taho ba zata taka daga nan zuwa can gidan da qafa, shi yasa na dawo bakin aiki na, ina fatan za a karbi uziri na"
Cikin share hawaye Sultana ta ce,
"Mu je"
"Ku tai ina? Sulty baby yaushe ki ka hwara kafiya da taurin kai, akan wannan qasqantaccen drivern ne ki ka hwara rashin kunya ko? Mu na hwadi ki na hwadi?....kaiii malam ji nan, bar ganin ka na da qirar majiya qarhi, qarhin mulki ba qarya ne ba, zan iya sanyawa a batar da kai, da kai da kaff dangin ku, ba Lamishi ba ce uwar ka? Ko ba ita ta ba? To zan ci mata mutunci gaban ka, in sa a dauren ku har igiya ta yi saura,in ga uban da ya tsaya maka kafff garin Zamfara, ka rabu da diya ta, tun kana gane hanyar komawa gida,ka karya asirin da ka mata kafin na haukata ka, ka na ji na? Ke kuma wuce mota ta mu tai"
Hannu ta sanya ta fizgi Sultana da tun da ta fara zagi da ci wa Lawwali mutunci take kuka ta na bata hakuri, Lawwali kuwa tsaye yake ya na murmushi, babu mai iya karantar yanayin da yake ciki a fuskar shi.
A cikin zuciyar shi kuwa, kawai tunanin yanda zai yagalgala naman Hajiya Ikee a dajin su yake, manyan mata masu ji da kan su ma sun nuna su na son Lawwali yaran manya da attajirai sun qaunace shi, a duk sanda Gwamna ya dauke shi suka fita babban taron manya, ya na wahala ya bar wajen bai samu wadan da suka maqale masa ba, to ita sultana daban ce da ba zata ta so shi ba? Tunda jini na tsargawa a jijiyoyin jiki da tsokar ta.
Hajiya Ikee ce ta danna Sultana a motar ta, ta zagaya zata zauna, kafin ta zauna Sultana ta fita da gudu ta nufi Lawwali,
"Sultan kar ka bari ta tabi wannan dan talakawan, ta janyo mana tsiya a zuri'a, kar ka kuskura ka bari ta tabe shi zan saba maka"
Yanayin Sultan ya nuna ba ya son riqe sultana, Amma dole ya riqe ta, dan bai saba sab'a Umarnin iyayen nasu ba, rungume ta ya yi, ita kuma ta na tirjewa ta na kuka, tare da miqawa Lawwali hannun ta, shi dai ya na nan tsaye bai motsa ba, bai kuma b'ata rai ba, hasali ma murmushin nan ne a fuskar shi, Hajiya Ikee na kewaya wa ta daga hannu zata wanke Sultana da mari taji an mata wani irin riqon da sai da ta ji fatar hannun ta na tabo qashin ta.
Sultana kuwa ta rintse idanun ta, ta qanqame Sultan, ma'aikatan wajen da dama sun riga sun san Lawwali, tini suka sha jinin jikin su, dan kuwa bacin ran da yake ta boyewa sai da ya bayyana a saman fuskar shi, wanda basu san shi ba kuma a ma'aikatan gidan sun zabura za su kai masa hari, akan me zai riqe hannun matar gwamna haka?
Shugaban masu kula da securities ne ya dakatar da su cike da tsoro, kar su ja musu bala'i, Lawwali ya huce akan su.
Yan kanzagi da 'yan maula da 'yan siyasan da ke giggilmawa ma sun tsaya ganin ikon Allah, a hankali murmushin fuskar Lawwali ya dawo, sannan ya saki hannun Hajiya Ikee, wadda ta ji kamar jijiyoyin wajen sun tsaya da aiki, wani yammmm, zummmm hannun ke mata, a hankali Lawwali ya furta .
"Ran ki shi dad'e,shiga Mota na kai ki gida,daga nan ina da wajen zuwa"
Da sauri kuwa Sultana ta bar wajen, har ta na haɗawa da gudu gudu, ta shige motar ta, ta zauna a gaba.
Shima shigewa ya yi, ya zauna, ya ja motar, Sultan ma take musu baya ya yi, cikin tsananin fushi da jin nauyin mutanen da suka zuba mata ido, Hajiya Ikee ta fada motar ta ta zauna, jan ta akai motocin da ke take ma nata baya suka bi su.
Lallai idan Gwamna ya dawo daga tafiyar da ya yi, za a yi ta ta qare, maganar Lawwali ta zo qarshe a shafin rayuwar su.
************************
A ranar da No 1 ya ji sauqi a ranar ya shirya dan zuwa maboyar da aka ajiye su Mubaraka, duk abinda yake No 4 na kai wa Oga bayani ta message, Oga ya gama shirya duk yanda za a yi, jiran zuwan No 1 kawai yake.
Agogon shi ne last abinda ya daura, sannan ya kalli No 4 ya ce,
"Mu tai, ka kai ni, da ina iya tuqa motar ma da kai na zan je, ba ni buqatar rakiya, amma ba zan iya ba saboda yanayin da nake jin kaina a ciki"
"Kar ka damu, zan iya kai ka duk inda ka ke buqata, kai dan uwa na ne"
"Na gode, mu tai ko"
"To Oga"
Sun fita daga dajin No 4 ya koma wajen No 1 dan zuwa maboyar su Mubaraka.
No 1 na gaba a mota, No 4 ya aikawa Lawwali saqon gasu nan sun bar gidan.
Shi kuwa waya ya yi ma sabbin yaran da ya horar, guda bakwai, su ma suka tabbatar masa da a shirye suke.
Cikin duhun magariba suke tafe, kafin su isa har an yi sallah, wanda su ba ta gaban su, sunan musulmai ne kawai da su, amma duk wani abu da Musulmin kirki yake su ba sa yi.
A qofar gidan su ka kashe motar, su ka fita, No 1 ne a gaba, ya na dingisa qafa, ya sanya key ya bude qofar, ya na fito.
Kafin ya kunna fitilar ya ji fito a bayan shi,cikin sauri da faduwar gaba ya lalibi makunnin fitilar dan kunnawa, hasken ta bai gama haskaka ko ina ba wani daga matasan ya sa bindiga ya harbe kwan fitilar, qara da ihun 'yan matan ne ya cika gidan,tun da suke a gidan basu taba jin an yi dambe ba ma, ballantana harbin bindiga, yau tasu ta qare.
Ai kuwa sai fad'a ya koma kan 'Yabbuga da Matar Yahai, nan fa suma suka hau nasu maganganun, abu fa ya qi ci ya qi cinyewa, har da dambe.
Asshibi naso ta raba amma abu ya fi qarfin ta, cikin sa'a kuwa Matar Yahai ta samu d'aga 'yabbuga ta maka da qasa, ta haye cikin ta, ta dinga kirba,sai da ta farfashewa 'Yabbuga baki sannan Asshibi da Mai buruji suka samu d'aga ta a jikin 'Yabbuga, Lamishi ta ji dadin hakan, dan kuwa ko ba komai an koya ma 'Yabbuga hankali, ta na miqewa ta hau kade jikin ta ta na fadin,
"Baki daki banza ba, zaki gani, har gida se hukuma ta kama min ke, bari dan Jummaa ya dawo"
"Baku da wanan azziqin da alfamar a Nigeria,"
"Haka kin ka ce ko?"
"Na hwadi,"
Haka nan suka yi ta sa'in sa har aka kirayi magariba suka tafi gidajen su, Asshibi kuwa gidan su Lamishi ta nufa suka yi ta gulmar sauran.
**************************
"Excellency gamu asibiti da shi, ba shi da halin magana shi yassa"
"Mi ya same shi halan?"
"Allah shi taimake ka wasa ta an ka yi, shi na ya samu rauni"
"Allah ya bashi lahiya, ka na ji na ba, wannan ajiyar ina so a qara bata tsaro, gaf nake nai amfani da ita, ba na so Ogan ku ya san me ke faruwa, ka gane?"
"Na gane Excellency,"
"Tau ya yi, ka gaishe shi in ya hwalka"
"Zai ji ranka shi dade "
Bayan sun gama wayar ne, ya sanar da No 1 duk yadda suka yi da gwamna, cikin jin jiki ya ke d'aga kai, alamar ya ji.
Cikin ran shi kuwa ya na tunanin kalar azabar da zai ganawa Mubaraka, duk abinda ya tunano sai ya ga ya yi kadan, qarshe saboda tsananin ciwon kan da yake ji, dole sai hakura ya yi da tunanin zuwa wani lokacin.
*Hummm anya ka daku kuwa No 1???*
💅🏻 *A GARIN MU* 💅🏻
BY HAERMEEBRAERH
PAGE 35:
Satin su Sultana biyu kafin Gwamna ya bata izin fita daga gidan gwamnati, a wannan satikan kuwa duk ta rame, ta yi zuru-zuru rashin ganin Lawwali da bata yi ya fitar da ita daga hayyacin ta, ita kan ta, ta na mamakin kalar soyayyar da take masa, anya wannan soyayyar ba zata zama ajalin ta ba kuwa?
Masu tsaron lafiyar ta ta dinga kallo daya bayan daya, sanda ta fito tafiya,dukkan su kamar sabbi ne, bata taba ganin wasun su ba.
Juyawa ta yi, ta kalli Hajiya Ikee da ta ke zuba mata murmushi, ta kalli Sultan wanda ke kallon ta da tsantsar kulawa da tausaya wa, ta ce,
"Ina driver na?"
Hade fuska Hajiya Ikee ta yi, sannan ta bude baki zata yi magana, al'ajabi ya sanya ta hadiye maganar ta.
Lawwali ne cikin uniform din shi, wanda da gani ka san sabbi ne, sai dai wadannan ba fari bane, ash color ne, da ratsin baqi a jikin riga da wandon kayan, duk yanda zan fasalta maku kalar kyaun da ya yi ba zai yu ba, sai ido ya gan shi kawai.
Hawaye ne kawai ke tsartuwa daga idon Sultana, a lokaci daya kuma ta na dariyar farin ciki, da murnar ganin jarumin maza Auwal din ta.
Ita kan ta Hajiya Ikee kasa magana ta yi tsabar kwarjinin da ya yi mata, Sultan kuwa zuwa ya yi ya daki kafadar Lawwali, tare da matsa ta, ya na zuba murmushi,
"Me na fada maka game da sa min qauna kuka?"
Lawwali dan duqawa ya yi, sannan ya ce,
"A min ahuwa ran ka shi dade, an min iyaka da shigowa gidan nan ,yau ma Umarni uwar daki na tabban, ta ce na taho na maishe ta gida, in ban taho ba zata taka daga nan zuwa can gidan da qafa, shi yasa na dawo bakin aiki na, ina fatan za a karbi uziri na"
Cikin share hawaye Sultana ta ce,
"Mu je"
"Ku tai ina? Sulty baby yaushe ki ka hwara kafiya da taurin kai, akan wannan qasqantaccen drivern ne ki ka hwara rashin kunya ko? Mu na hwadi ki na hwadi?....kaiii malam ji nan, bar ganin ka na da qirar majiya qarhi, qarhin mulki ba qarya ne ba, zan iya sanyawa a batar da kai, da kai da kaff dangin ku, ba Lamishi ba ce uwar ka? Ko ba ita ta ba? To zan ci mata mutunci gaban ka, in sa a dauren ku har igiya ta yi saura,in ga uban da ya tsaya maka kafff garin Zamfara, ka rabu da diya ta, tun kana gane hanyar komawa gida,ka karya asirin da ka mata kafin na haukata ka, ka na ji na? Ke kuma wuce mota ta mu tai"
Hannu ta sanya ta fizgi Sultana da tun da ta fara zagi da ci wa Lawwali mutunci take kuka ta na bata hakuri, Lawwali kuwa tsaye yake ya na murmushi, babu mai iya karantar yanayin da yake ciki a fuskar shi.
A cikin zuciyar shi kuwa, kawai tunanin yanda zai yagalgala naman Hajiya Ikee a dajin su yake, manyan mata masu ji da kan su ma sun nuna su na son Lawwali yaran manya da attajirai sun qaunace shi, a duk sanda Gwamna ya dauke shi suka fita babban taron manya, ya na wahala ya bar wajen bai samu wadan da suka maqale masa ba, to ita sultana daban ce da ba zata ta so shi ba? Tunda jini na tsargawa a jijiyoyin jiki da tsokar ta.
Hajiya Ikee ce ta danna Sultana a motar ta, ta zagaya zata zauna, kafin ta zauna Sultana ta fita da gudu ta nufi Lawwali,
"Sultan kar ka bari ta tabi wannan dan talakawan, ta janyo mana tsiya a zuri'a, kar ka kuskura ka bari ta tabe shi zan saba maka"
Yanayin Sultan ya nuna ba ya son riqe sultana, Amma dole ya riqe ta, dan bai saba sab'a Umarnin iyayen nasu ba, rungume ta ya yi, ita kuma ta na tirjewa ta na kuka, tare da miqawa Lawwali hannun ta, shi dai ya na nan tsaye bai motsa ba, bai kuma b'ata rai ba, hasali ma murmushin nan ne a fuskar shi, Hajiya Ikee na kewaya wa ta daga hannu zata wanke Sultana da mari taji an mata wani irin riqon da sai da ta ji fatar hannun ta na tabo qashin ta.
Sultana kuwa ta rintse idanun ta, ta qanqame Sultan, ma'aikatan wajen da dama sun riga sun san Lawwali, tini suka sha jinin jikin su, dan kuwa bacin ran da yake ta boyewa sai da ya bayyana a saman fuskar shi, wanda basu san shi ba kuma a ma'aikatan gidan sun zabura za su kai masa hari, akan me zai riqe hannun matar gwamna haka?
Shugaban masu kula da securities ne ya dakatar da su cike da tsoro, kar su ja musu bala'i, Lawwali ya huce akan su.
Yan kanzagi da 'yan maula da 'yan siyasan da ke giggilmawa ma sun tsaya ganin ikon Allah, a hankali murmushin fuskar Lawwali ya dawo, sannan ya saki hannun Hajiya Ikee, wadda ta ji kamar jijiyoyin wajen sun tsaya da aiki, wani yammmm, zummmm hannun ke mata, a hankali Lawwali ya furta .
"Ran ki shi dad'e,shiga Mota na kai ki gida,daga nan ina da wajen zuwa"
Da sauri kuwa Sultana ta bar wajen, har ta na haɗawa da gudu gudu, ta shige motar ta, ta zauna a gaba.
Shima shigewa ya yi, ya zauna, ya ja motar, Sultan ma take musu baya ya yi, cikin tsananin fushi da jin nauyin mutanen da suka zuba mata ido, Hajiya Ikee ta fada motar ta ta zauna, jan ta akai motocin da ke take ma nata baya suka bi su.
Lallai idan Gwamna ya dawo daga tafiyar da ya yi, za a yi ta ta qare, maganar Lawwali ta zo qarshe a shafin rayuwar su.
************************
A ranar da No 1 ya ji sauqi a ranar ya shirya dan zuwa maboyar da aka ajiye su Mubaraka, duk abinda yake No 4 na kai wa Oga bayani ta message, Oga ya gama shirya duk yanda za a yi, jiran zuwan No 1 kawai yake.
Agogon shi ne last abinda ya daura, sannan ya kalli No 4 ya ce,
"Mu tai, ka kai ni, da ina iya tuqa motar ma da kai na zan je, ba ni buqatar rakiya, amma ba zan iya ba saboda yanayin da nake jin kaina a ciki"
"Kar ka damu, zan iya kai ka duk inda ka ke buqata, kai dan uwa na ne"
"Na gode, mu tai ko"
"To Oga"
Sun fita daga dajin No 4 ya koma wajen No 1 dan zuwa maboyar su Mubaraka.
No 1 na gaba a mota, No 4 ya aikawa Lawwali saqon gasu nan sun bar gidan.
Shi kuwa waya ya yi ma sabbin yaran da ya horar, guda bakwai, su ma suka tabbatar masa da a shirye suke.
Cikin duhun magariba suke tafe, kafin su isa har an yi sallah, wanda su ba ta gaban su, sunan musulmai ne kawai da su, amma duk wani abu da Musulmin kirki yake su ba sa yi.
A qofar gidan su ka kashe motar, su ka fita, No 1 ne a gaba, ya na dingisa qafa, ya sanya key ya bude qofar, ya na fito.
Kafin ya kunna fitilar ya ji fito a bayan shi,cikin sauri da faduwar gaba ya lalibi makunnin fitilar dan kunnawa, hasken ta bai gama haskaka ko ina ba wani daga matasan ya sa bindiga ya harbe kwan fitilar, qara da ihun 'yan matan ne ya cika gidan,tun da suke a gidan basu taba jin an yi dambe ba ma, ballantana harbin bindiga, yau tasu ta qare.