Sashe 17
A Garin Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yau mutan gidan Gwamna Halliru sun tashi da bayyanannan farin ciki, dan kuwa Sultana farin cikin su ce, a duk sanda take walwala, to suma su na walwala, sanda kuwa take cikin qunci, suma fa ba za su zama cikin farin ciki ba, har sai ta koma normal.
Hakan ce ta sa gwamna yi mata abinda zai sanya ta farin ciki.
Cikin doguwar riga baqa mai fadi mai stones kalar blue da farare su na ta walqiya kamar fuskar ta, ta fito, riqe da jaka, da wayar ta a hannu.
Sultan ma cikin shiri, ya fito, dan su na son su je su ga inda Foundation din nata yake.
Hajiya Ikee an sha ado na alfarma ita da gwamna , sai qamshin turare masu tsada ke tashi,
Sultana ta yi mamakin ganin irin motar da aka ware domin kai ta da komowa da ita daga duk inda za ta, tsohuwar motar ta ta kalla, ta ga batai komai ba, last year aka sai mata, ta so yin magana, amma bata son ta bata moment din, ba komai, zata san ya da ta yi da waccan din.
Qamewa ta yi a lokacin da ya bude mata qofar shiga mazaunin da ya dace da mace mai aji da kima kamar ta,qamshin turaren shi ta shaqa cikin salo mai burgewa, ta kuwa burge Lawwali,idanu suka qurawa juna.
Wata iriyar faduwar gaba ce ta kama Sultana, abinda tunda take a rayuwar ta ta duniya bata taɓa ji ba game da kowa, idanun ta ta lumshe a daidai lokacin da ya furta,
"Ran ki shi dade, Bismillah"
Tsigar jikin ta ce ta kowanne kusurwa da kafa ta jikin ta ta miqe,
'Waye wannan?'
Shi ne abinda zuciyar ta ta furta a hankali, uniform din shi ta kalla,ta rasa gane a wanne bangaren tsaron yake, bayan ta zauna ne ya shiga mazaunin driver ya zauna shima ,motocin su Gwamna ne a gaba, sannan ta su, sai ta masu tsaron lafiyar su na take masu baya.
"Wane ne kai?"..........
*Wane ne shi ? In ji Sulty Babu*
💅🏻 *A GARIN MU* 💅🏻
WRITTEN BY HAERMEEBRAERH
PAGE 17:
"LAWWALI DAN TALO"
"What?"
"Eh suna na kenan, Ni ne sabon drivern ki, kuma guard din ki,"
"Ok, kuma sunan ka kenan? LAWWALI DAN TALO?"
Murmushi Lawwali ya yi, ya ce,
"Eh sunan kenan Ranki shi dade, ko akwai matsala na?"
"Ah ah , tambaya d'ai Ni kai, amma zan iya kiran ka da Auwal?"
Wani irin murmushi ya yi, mai sauti, wanda ya narkar masa da duk wata gaba ta jikin shi, nan da nan ya ji ran shi ya haskaka, Mubarakan shi na kiran shi Auwal, ga Sultana...na neman izinin kiran shi da Auwal, cikin sauri da alamar bada hakuri Sultana ta ce,
"I am so sorry pls, ba niyya ta na sauya maka suna ba, na ga kamar Auwal da Lawwali daya ne, shi ya sa, i can call u with whatever u want me to," (zan iya kiran ka, da duk abinda ka ke so na kira ka da shi)
Shi ma cikin hanzarin da zaquwa ya ce,
"Ran ki shi dade, ki kira Ni da Auwal, sunan da nih-hi so na wallah, qauna ta dai ka kira na da wanga suna ,shi nas-sa kin ka ji na yi shiru"
Sultana ta ji dadi da ba ta bata masa rai ba, dan haka sai ta daga kai kawai, ba ta son ta yi maganar da zata sa ta yi dana sani, ta rasa dalilin da ya sa ta ke ta surutu da mutumin da ta fara gani yau, har da qoqarin sauya masa suna.
Tafiyar awa daya da wasu 'yan mintuna ce ta kai su unguwar da Foundation din yake, motoci sun tsaitsaya, Gwamna da Hajiya Ikee da Sultan suna tsaye su na jiran ta fito, ta tsaya mamakin ganin motocin 'yan jarida da police su zagaye wajen, ga mutane mabuqata an tara su a wajen, dama Daddyn nata ya yi wannan shirin ne? Lallai da gaske yake yi, amma abinda bai mata dadi ba shi ne, yan jarida da ta ga suna tsaitsaye su na jiran fitar ta, ba haka ta ke son gudanar da qungiyar ba, ba ta buqatar sanar da duniya abinda take yi, ta na son yi ne domin Allah.
Kamar Sultan ya karanci tunanin ta, kurdawa ya yi cikin mutanen, ya ɗan taba kafadar Lawwali da ya bude mata mota ya na jiran ta fita, matsa wa ya yi, ya tsaya a gaban ta, cikin murya mai taushi ya ce,
"Sulty baby fito mana, kar ki damu da mutanen nan, ki fito kawai abin ki ki ga waje, sannan ki bawa wadannan mabuqatan abincin,da ke a can wajen, an yi haka ne dan wasu mabuqatan su ga wajen su zo gare ki neman taimako ke gane?"
Daga kai ta yi, amma a qasan ran ta, da an barta, shi mai neman taimako ai ba ya buya, a duk inda suke za ta nemo su.
Cike da jin kunya ta fita, dan bata saba da irin wannan abubuwan ba, shi kan shi Sultan bai ji dadin yanda mahaifin nasu ya tallata abun ba, da ya san za ai haka da bai zo ba, yanzu hotunan su da video din su zai ta zaga gari.
Yanka dan kyallen da aka Saka a bakin qofar shiga building din ta yi da almkashin da ya sha ado da kyalle, addu'a ta yi a zuciyar ta, ta neman sa'a, da nasara akan abinda ta sa gaba, tare da kariya daga dukkan sharri, sannan ta sanya qafata ta dama ta shiga, har cikin offices din guda bakwai, sai manyan store rooms guda hudu, wajen kamar dan irin buqatar ta aka riga aka gina shi,tabbas abinda take buri kenan n biyu a rayuwar ta bayan koyarwa, to ga dama ta samu.
Hawayen farin ciki ne ke son saukar mata, ta maqale su, Hajiya ta rungume, itama ta rungume ta, nan da na kuwa aka hau daukan su hotuna, ji ka ke kyas kyas kyas, Gwamna Halliru ne ya dafa kan ta, sannan ya rada mata wani abu, da hanzari ta daga kan ta, suka fita zuwa farfajiyar wajen, Lawwali na can daga nesa ya yi zooming din ta a wayar shi ya na mata video ,fuskar ta cike da annashuwa da annuri ta ke rabawa mabuqata abinci.
Buhun shinkafa ,qaramin buhun sugar, sai omo, sabulu, mangyada, man ja, indomie da gishiri, su ne abubuwan da sultana ta dauki awa biyu ta na rabawa.
Shiri na musamman aka dauka live ana yaɗawa a gidan talabijin n garin Zamfara ,nan da nan kuwa wasu mutanen suka ji qaunar sultana ta shige su, wasu kuma banda zagi da tsinuwa ba abinda suke mata, wasu zagin ta suke da mahaifan ta har su na fadin.
'Dubi kayan jikin su, shi kadai ya isa wani talakan ya ci da kan shi na wata uku, a haka suke son taimakawa'
Kowa da abinda ya ke fadi, domin shi ɗan Adam kayan Allah ne, ba mai iya masa, ba tare da sun san me ne ne a zuciyar ta ba, sun yanke mata hukunci.
Yanda Sultana bata gaji ba haka ma Lawwali bai gaji da ɗaukan ta ba, domin kuwa gwamna da Hajiya Ikee da suka ga abun ba na qare bane, tafiya suka yi, suka bar ta, Sultan ya so zama, Hajiya ta tisa shi a gaba suka koma gida tare.
Mutane kuwa kamar ingizo su ake, qara zuwa wasu suke, su na layi, Ita kuwa miqawa take, cike da farin ciki, da murmushi, da za a bude qirjin ta wataqila hasken dake ciki sai ya kashe na wani ido, saboda tsabar haske, da farin cikin da ke ciki, tabbas dukkan mai bayarwa domin Allah farin ciki ya tabbata a zuciyar shi .
Sun bar wajen da azahar, ba dan sultana ta so ba, sai dan komai ya qare ne, har da kudin dake jakar ta sai da ta bayar.
Mutane na ta mata addu'a, wasu har ran su, wasu kuma yi kawai suke, a gefe su na zagin ta, da iyayen ta, su na fadin na munafurci ne, dan an kusa zabe ne, ya ke son ya yi amfani da ita, dan ya zarce.
Sultana na ta daga ma wata dattijuwa hannu ta fada motar ta, Lawwali ya mayar ya rufe.
"Ran ki shi dade ina muka nufa?"
"Gida"
Shi ne abinda ta fadi, ta kwantar da kanta a jikin motar, fuskar ta dauke da murmushin da ya kasa gushewa, ko gajiya bata ji a jikin ta, saboda jin dadi.
Lokaci zuwa lokaci Lawwali na satar kallon ta, a duk lokacin da zai dora ido akan fuskar ta, sai ya ji jinin jikin shi ya tsinke, ya qara gudu, ba qaramin kamu son ta ya masa ba.
Har suka isa gida bata daina fara'a ba.
Bude mata motar ya yi, ya tsaya dan ta fita ya rufe, bata san ya na yi ba, dan durqusa wa ya yi daidai kunnen ta kadan ya ce,
"Ran ki shi dade mun iso,"
A firgice ta kalle shi, fuskar shi ta kalla, ta ga ba wani alamar wasa, ko murmushi, sanar da ita kawai ya yi, ya kalli gefe, ajiyar zuciya ta sauke mai qarfi, ta masa godiya zata fita, har ta fara taku za ta shige ta dawo baya, ta kalle shi, shi ma ita ya kalla, idanun su cikin na juna ta ce,
"Sultana,...ka kira Ni da sultana"
Cikin hanzari ta bar wajen, bin ta ya yi da kallo, cikin wani irin yanayi, domin kuwa ta gama kashe masa duk wata laka ta jikin shi .
Jiki ba kwari ya rufe motar ya gyara parking , sannan ya kashe ya tafi gidan shi ,tun a hanya ya kira Mubaraka ya na bata labarin yanda komai ya kasance, ta na ta taya shi farin ciki, ashar din Lamishi ne ya katse mata wayar da take da Yah Auwal din ta.
Komawar su kenan, ta hangi tukunyar tuwon su na zubewa, rude ya tafasa ya malale a qasa.
Hakan ce ta sa gwamna yi mata abinda zai sanya ta farin ciki.
Cikin doguwar riga baqa mai fadi mai stones kalar blue da farare su na ta walqiya kamar fuskar ta, ta fito, riqe da jaka, da wayar ta a hannu.
Sultan ma cikin shiri, ya fito, dan su na son su je su ga inda Foundation din nata yake.
Hajiya Ikee an sha ado na alfarma ita da gwamna , sai qamshin turare masu tsada ke tashi,
Sultana ta yi mamakin ganin irin motar da aka ware domin kai ta da komowa da ita daga duk inda za ta, tsohuwar motar ta ta kalla, ta ga batai komai ba, last year aka sai mata, ta so yin magana, amma bata son ta bata moment din, ba komai, zata san ya da ta yi da waccan din.
Qamewa ta yi a lokacin da ya bude mata qofar shiga mazaunin da ya dace da mace mai aji da kima kamar ta,qamshin turaren shi ta shaqa cikin salo mai burgewa, ta kuwa burge Lawwali,idanu suka qurawa juna.
Wata iriyar faduwar gaba ce ta kama Sultana, abinda tunda take a rayuwar ta ta duniya bata taɓa ji ba game da kowa, idanun ta ta lumshe a daidai lokacin da ya furta,
"Ran ki shi dade, Bismillah"
Tsigar jikin ta ce ta kowanne kusurwa da kafa ta jikin ta ta miqe,
'Waye wannan?'
Shi ne abinda zuciyar ta ta furta a hankali, uniform din shi ta kalla,ta rasa gane a wanne bangaren tsaron yake, bayan ta zauna ne ya shiga mazaunin driver ya zauna shima ,motocin su Gwamna ne a gaba, sannan ta su, sai ta masu tsaron lafiyar su na take masu baya.
"Wane ne kai?"..........
*Wane ne shi ? In ji Sulty Babu*
💅🏻 *A GARIN MU* 💅🏻
WRITTEN BY HAERMEEBRAERH
PAGE 17:
"LAWWALI DAN TALO"
"What?"
"Eh suna na kenan, Ni ne sabon drivern ki, kuma guard din ki,"
"Ok, kuma sunan ka kenan? LAWWALI DAN TALO?"
Murmushi Lawwali ya yi, ya ce,
"Eh sunan kenan Ranki shi dade, ko akwai matsala na?"
"Ah ah , tambaya d'ai Ni kai, amma zan iya kiran ka da Auwal?"
Wani irin murmushi ya yi, mai sauti, wanda ya narkar masa da duk wata gaba ta jikin shi, nan da nan ya ji ran shi ya haskaka, Mubarakan shi na kiran shi Auwal, ga Sultana...na neman izinin kiran shi da Auwal, cikin sauri da alamar bada hakuri Sultana ta ce,
"I am so sorry pls, ba niyya ta na sauya maka suna ba, na ga kamar Auwal da Lawwali daya ne, shi ya sa, i can call u with whatever u want me to," (zan iya kiran ka, da duk abinda ka ke so na kira ka da shi)
Shi ma cikin hanzarin da zaquwa ya ce,
"Ran ki shi dade, ki kira Ni da Auwal, sunan da nih-hi so na wallah, qauna ta dai ka kira na da wanga suna ,shi nas-sa kin ka ji na yi shiru"
Sultana ta ji dadi da ba ta bata masa rai ba, dan haka sai ta daga kai kawai, ba ta son ta yi maganar da zata sa ta yi dana sani, ta rasa dalilin da ya sa ta ke ta surutu da mutumin da ta fara gani yau, har da qoqarin sauya masa suna.
Tafiyar awa daya da wasu 'yan mintuna ce ta kai su unguwar da Foundation din yake, motoci sun tsaitsaya, Gwamna da Hajiya Ikee da Sultan suna tsaye su na jiran ta fito, ta tsaya mamakin ganin motocin 'yan jarida da police su zagaye wajen, ga mutane mabuqata an tara su a wajen, dama Daddyn nata ya yi wannan shirin ne? Lallai da gaske yake yi, amma abinda bai mata dadi ba shi ne, yan jarida da ta ga suna tsaitsaye su na jiran fitar ta, ba haka ta ke son gudanar da qungiyar ba, ba ta buqatar sanar da duniya abinda take yi, ta na son yi ne domin Allah.
Kamar Sultan ya karanci tunanin ta, kurdawa ya yi cikin mutanen, ya ɗan taba kafadar Lawwali da ya bude mata mota ya na jiran ta fita, matsa wa ya yi, ya tsaya a gaban ta, cikin murya mai taushi ya ce,
"Sulty baby fito mana, kar ki damu da mutanen nan, ki fito kawai abin ki ki ga waje, sannan ki bawa wadannan mabuqatan abincin,da ke a can wajen, an yi haka ne dan wasu mabuqatan su ga wajen su zo gare ki neman taimako ke gane?"
Daga kai ta yi, amma a qasan ran ta, da an barta, shi mai neman taimako ai ba ya buya, a duk inda suke za ta nemo su.
Cike da jin kunya ta fita, dan bata saba da irin wannan abubuwan ba, shi kan shi Sultan bai ji dadin yanda mahaifin nasu ya tallata abun ba, da ya san za ai haka da bai zo ba, yanzu hotunan su da video din su zai ta zaga gari.
Yanka dan kyallen da aka Saka a bakin qofar shiga building din ta yi da almkashin da ya sha ado da kyalle, addu'a ta yi a zuciyar ta, ta neman sa'a, da nasara akan abinda ta sa gaba, tare da kariya daga dukkan sharri, sannan ta sanya qafata ta dama ta shiga, har cikin offices din guda bakwai, sai manyan store rooms guda hudu, wajen kamar dan irin buqatar ta aka riga aka gina shi,tabbas abinda take buri kenan n biyu a rayuwar ta bayan koyarwa, to ga dama ta samu.
Hawayen farin ciki ne ke son saukar mata, ta maqale su, Hajiya ta rungume, itama ta rungume ta, nan da na kuwa aka hau daukan su hotuna, ji ka ke kyas kyas kyas, Gwamna Halliru ne ya dafa kan ta, sannan ya rada mata wani abu, da hanzari ta daga kan ta, suka fita zuwa farfajiyar wajen, Lawwali na can daga nesa ya yi zooming din ta a wayar shi ya na mata video ,fuskar ta cike da annashuwa da annuri ta ke rabawa mabuqata abinci.
Buhun shinkafa ,qaramin buhun sugar, sai omo, sabulu, mangyada, man ja, indomie da gishiri, su ne abubuwan da sultana ta dauki awa biyu ta na rabawa.
Shiri na musamman aka dauka live ana yaɗawa a gidan talabijin n garin Zamfara ,nan da nan kuwa wasu mutanen suka ji qaunar sultana ta shige su, wasu kuma banda zagi da tsinuwa ba abinda suke mata, wasu zagin ta suke da mahaifan ta har su na fadin.
'Dubi kayan jikin su, shi kadai ya isa wani talakan ya ci da kan shi na wata uku, a haka suke son taimakawa'
Kowa da abinda ya ke fadi, domin shi ɗan Adam kayan Allah ne, ba mai iya masa, ba tare da sun san me ne ne a zuciyar ta ba, sun yanke mata hukunci.
Yanda Sultana bata gaji ba haka ma Lawwali bai gaji da ɗaukan ta ba, domin kuwa gwamna da Hajiya Ikee da suka ga abun ba na qare bane, tafiya suka yi, suka bar ta, Sultan ya so zama, Hajiya ta tisa shi a gaba suka koma gida tare.
Mutane kuwa kamar ingizo su ake, qara zuwa wasu suke, su na layi, Ita kuwa miqawa take, cike da farin ciki, da murmushi, da za a bude qirjin ta wataqila hasken dake ciki sai ya kashe na wani ido, saboda tsabar haske, da farin cikin da ke ciki, tabbas dukkan mai bayarwa domin Allah farin ciki ya tabbata a zuciyar shi .
Sun bar wajen da azahar, ba dan sultana ta so ba, sai dan komai ya qare ne, har da kudin dake jakar ta sai da ta bayar.
Mutane na ta mata addu'a, wasu har ran su, wasu kuma yi kawai suke, a gefe su na zagin ta, da iyayen ta, su na fadin na munafurci ne, dan an kusa zabe ne, ya ke son ya yi amfani da ita, dan ya zarce.
Sultana na ta daga ma wata dattijuwa hannu ta fada motar ta, Lawwali ya mayar ya rufe.
"Ran ki shi dade ina muka nufa?"
"Gida"
Shi ne abinda ta fadi, ta kwantar da kanta a jikin motar, fuskar ta dauke da murmushin da ya kasa gushewa, ko gajiya bata ji a jikin ta, saboda jin dadi.
Lokaci zuwa lokaci Lawwali na satar kallon ta, a duk lokacin da zai dora ido akan fuskar ta, sai ya ji jinin jikin shi ya tsinke, ya qara gudu, ba qaramin kamu son ta ya masa ba.
Har suka isa gida bata daina fara'a ba.
Bude mata motar ya yi, ya tsaya dan ta fita ya rufe, bata san ya na yi ba, dan durqusa wa ya yi daidai kunnen ta kadan ya ce,
"Ran ki shi dade mun iso,"
A firgice ta kalle shi, fuskar shi ta kalla, ta ga ba wani alamar wasa, ko murmushi, sanar da ita kawai ya yi, ya kalli gefe, ajiyar zuciya ta sauke mai qarfi, ta masa godiya zata fita, har ta fara taku za ta shige ta dawo baya, ta kalle shi, shi ma ita ya kalla, idanun su cikin na juna ta ce,
"Sultana,...ka kira Ni da sultana"
Cikin hanzari ta bar wajen, bin ta ya yi da kallo, cikin wani irin yanayi, domin kuwa ta gama kashe masa duk wata laka ta jikin shi .
Jiki ba kwari ya rufe motar ya gyara parking , sannan ya kashe ya tafi gidan shi ,tun a hanya ya kira Mubaraka ya na bata labarin yanda komai ya kasance, ta na ta taya shi farin ciki, ashar din Lamishi ne ya katse mata wayar da take da Yah Auwal din ta.
Komawar su kenan, ta hangi tukunyar tuwon su na zubewa, rude ya tafasa ya malale a qasa.