Sashe 71
A Garin Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kwantar da kan ta tayi a qirjin shi, a ran ta ta na ayyana, da ta san inda aka kwantar da mahaifin ta da sun je asibitin ko daga nesa ne ta hango shi, hawaye ne taji su na zuba a idanun ta, da sauri ta sa hannu za ta goge, lawwali ya riga ta, cikin murya mai sanyi ya ke magana,
"Sultyna ki dena kukan ga, ya na karyar min da zuciya, na ji kamar na faasa abinda na ke da niyya, ke dai san quduri na da yasa na ke abinda nake a yanzu, ki bani goyon baya komi zai wuce,in shaa Allahu"
"Allah ya yarda, ina son ka miji na"
Wani irin dad'i ne ya lullube Lawwali, kalmar da ba wanda ya taba furta masa bayan qanwar shi sai Kuma ita, amma a bakin Mubaraka kad'ai ya fara jin wannan kalma, se ga shi ya samu matar dake yawan furta masa, yi ya yi kamar bai ji ba ya ɗan had'e gira ya ce,
"Na'am mi ki ka ce??"
Murmushi tayi dan ta gane me yake nufi, so yake ta maimaita masa, tashi tayi ta haye jikin shi, ta kwantar da shi a saman gadon sosai, ta yanda suke fuskantar junan su, sai da ta sumbace shi sosai sannan ta kalli kwayar idon shi ta ce,
"Cewa nayi....ina son hancin ka, da idon ka, da nan wajen..(ta nuna lips din shi) ina son kowacce gaba da ke jikin ka...ina son ka, ko da ace ni makauniya ce, kuma kurma ce, sannan bebiya ce, zan qirqiri kowacce hanya ce dan sanar da kai ni Sultana ina son ka Auwal, ba zan taba dena son ka a raina ba, har sai sanda na dena numfashi a duniya, ina maka son da ban taba yi wa wani ba, kai ne na farko a cikin zuciya ta, kuma kai ne na qarshe"
Wani irin numfashi mai sauti Lawwali ke saukewa ya rasa kalar dad'in da Sultana ke sanya shi ji a wanan lokaci, rungume ta ya yi sosai a jikin shi, har sai da ta saki wata siririyar qara, sannan ya sake ta ya na murmushi.
"Yi hankuri Sultyna, ji nikai kamar na bude fata da tsokar jiki na, na balle qashin da ya yi wa zuciya ta rumfa na ajiye ki a can ciki ki zauna daram, saboda yanda nake jin...."
Shiru ya yi bai furta ba, a hankali ta daga kan ta, cikin wani kallo mai kashe jiki, ta na lasar leben ta na qasa ta ce,
"Me ka ke ji?"
"Ina jin son ki Sultana, ina jin qaunar ki sultana, ba na son rabuwa da ke har bayan mutuwa ta, amma na san zai wahala mu had'u, saboda kowa makomar shi d...."
Ba tare data shirya ba ta ji saukar wasu hawaye Masu zafi, a kuncin ta, dan kuwa ta fuskanci me yake so ya fada,
"Subhanallahi, haba haba Auwal, ka dena kalar wannan tunanin, rahamar Allah mai yalwa ce, Allah ba so ya ke ya sanya bayin shi a wuta ba, Allah so yake bayin shi masu zunubi su tuba domin ya yafe musu, ya lullube su da rahamar shi komai laifin su, wanda ma ya yi shirka ga Allah in ya tuba kan ya mutu Allah na yafe masa ballantana kai, da baka taba duqawa gaban boka ko malam ba, sannan baka sani ba, ni din da ka ke wa kallon zan shiga aljannah wataqila Allah ya sanya ka a aljannah din mu zauna tare saboda ni din, sannan Allah zai iya jarabta ta da wani abun, ni kuma na yi wasa da shi na aikata zunubin da zai kai ni wuta, hadisi ne fa guda, akwai mutanen da za su yi ta aikata ayyuka irin na 'yan aljannah, saura kad' an su shiga aljannar, amma se su aikata aiki irin na 'yan wuta, se Allah ya sanya su a wutar, sannan akwai mutanen da za su yi ta aiki irin na' yan wuta, sauran kad'an su shiga wutar se kawai su yi aiki irin na 'yan aljannah, sai Allah ya kare su ya sanya su a aljannah, ka gani? Allah ba ta inda baya wanzar da rahama da ikon shi"
"Sultana ban taba shirka ba, amma ina taimaka wa masu yi, duk abinda mahaifin ki ya buqata da sauran 'Yan siyasa a baya ko mene shi ina samar musu shi, duk da na san tsafi za a yi da abun"
Hawayen ta ne suka qaru, jin cewar har da mahaifin ta a aikata shirka,
"Ka yi istigfar Allah zai amsa, ka yi da kyayyawar niya, Allah zai yafe maka"
"Allah na tuba ka yahe min, Allah ka yahe min manya da qananan zunubbai na, Allah ka yi min rahama, ka cika min buri na,"
"Ameen,"
Kafin bacci ya ɗebe su, sun tattauna akan abubuwa da dama, sun kuma tsara duk wani abu da ya kamata su aikata a gaba, a haka bacci ya dauke su suna manne da junan su.
***************************
Kamar yanda Isah ya yi alqawari, ya siyi goro mai yawan gaske, dan tafiya Makka, wanan karon dubu hamsin casss ya cake wa Hansatu, amma bata ci su a banza ba, sai da ya mori jikin ta da kyau da kyau, dan duk girman ta, da jarumtar ta, sai da ta dinga shiga ruwan zafi, Ita dai ta sawa ran ta, ba zai sake ganin wani rawar kan son shi awajen ta ba, tunda ta yi a baya bai mata amfani ba, sannan ba zai sake ganin murmushin ta ba, tunda a baya sai da ta ce wa audiga bata iya murmushi ba,ta fita iyawa, duk bata samu ribar murmushin ba,hakan kuwa na matuqar damun Isah, kula da cewar ko sau nawa zai neme ta ba zata qi ba,shi ya sa ya ke fanshe haushin rashin sakewar a jikin ta.
Hajiyar Hansatu da Yaya Musa sun yi qoqari sosai wajen ba Isah wasu kudin da zai qara akan jarin shi, sai da ya musu sallama sannan aka bada mota kamar wancan karon aka kai shi airport, wannan karon ko kwalla Hansatu bata yi ba, balle ta koka, Isah kuwa ya ji haushi matuqa, sannan ta ce ba zata yi rakiya ba, a fusace ya fad'a mota, aka tafi kai shi,ko da takoma sai ta ce wa Hajiya ita bata so ta ga ya tafi ya barta, kuka za tai, kuma bata so ta daga masa hankali,dan haka Hajiya bata ce komai ba, sai suka ci gaba da hirar su.
Isah sun isa airport, ya sauke kayan shi da komai, cikin dabarar da suke yi kar a gane goro ne, ya na tsaye wani mutum fari ya tsaya gefen shi, sallama ya masa shi ma ya amsa, sai ya ji maganar kamar ta Inyamuri ko bayerabe,
Mutumin ya fara yi wa Isah magana da turanci, Isah ba turanci, fuska ta muzanta da kunya, sai bawan Allahn ya gane Isah fa wala ingilishi, cikin gurbatacciyar Hausar shi ya ke tambayar Isah, Makka zai je ko Madina in sun isa Saudiya?
"Makka zani"
"Masha Allah, ni ma can nake da zama, ina da gida da iyali a can, kai fa ina ka ke zama?"
"Ni a hotel kawai nake sauka, banda gidan zama,"
"Allah Sarki, ka fad'a min inda ka ke sauka in na samu natsuwa zan neme ka, se ka dawo gida na da zama, tunda duk qasar mu d'aya, in a foreign land in ka ga d'an qasar ku ji ka ke kamar d'an uwanka ne"
Sunan hotel din da yake sauka ya sanar da bawan Allahn nan ya na ta murna, a qalla ba shi ba biyan kudin hotel, zama suka yi tare, suna ta hira, kamar abokan juna, duk inda CCTV camera yake a wajen bawan Allahn nan ya sani, kuma daidai gwargwado juya bayan shi yake, ba ya bari fuskar shi ta hasku, ya yi shiga irin ta larabawa ya saka face mask, se surutu yake wa Isah da gurbatacciyar hausar shi, Isah kuwa banda washe baki ba abinda yake.
Sai da aka shiga jirgi ne suka rabu, saboda wajen zaman su ba daya bane.
Tafiya ta miqa zuwa Saudiya, Isah ba abinda ya ke banda tunanin Hansatu, wannan karon ji yake kamar ya bar wani bangare na jikin shi, qudirtawa ya yi in Allah ya sauke shi lafiya, ita zai fara kira su gaisa.
**********************
A hanyar su ta zuwa garin na Zamfara duk wani motsi na Mubaraka na kan idon Taheer, zuciyar shi kuwa na ta kakkaryewa zuwa qananan pieces ,ya yi zurfi akan son ta ba tare da ya sani ba, wataqila dalilin gano ya na son nata, rabuwar da ta zo musu ba tare da shiri bane, da ya kula ya na son ta tun da, da ya yad'a manufar shi a wajen ta, gashi yanzu lokaci ya qure masa.
Mubaraka ce ta yi qarfin halin yi masa magana, ta ce,
"Yah Taheer akwai damuwa ne?"
Da sauri ya sanya murmushin yaqe ya ci gaba da tuqi, bai ce komai ba, tafiya suke kamar ba zai magana ba, can kamar wanda aka shaqe ya ce,
"Yanzu in kin tafi shikenan? Mantawa zakiyi da mu ko? Ga yaran ki can kin bar su suna ta kuka, ke kad'ai ka lallashin su in su na rikici, sun hi sabawa da ke,gashi zaki tafi ki bar su"
"Yah Taheer ku din wani bangare ne mai girma a rayuwa ta, ba zan taba manta wa da ku ba, ka sani na jima ban ga yayana ba, ina kewar shi sosai, amma in na je na gan su, ai zan koma wajen ku, in Allah ya yarda"
Wani irin murmushi Taheer ya sake, har da sosa kai, murmushin shi ya bawa Mubaraka mamaki, sai ita ma ta fara murmushin, cikin daurewar kai, dan ta kasa fahimtar inda Yah Taheer din ya dosa da wannan bayyanannen farin cikin................
*Allah kai ku lahiya ke dai, mu ai mun gane murmishin meye😂😂*
💅🏻 *A GARIN MU* 💅🏻
BY HAERMEEBRAERH
PAGE 53:
"Sultyna ki dena kukan ga, ya na karyar min da zuciya, na ji kamar na faasa abinda na ke da niyya, ke dai san quduri na da yasa na ke abinda nake a yanzu, ki bani goyon baya komi zai wuce,in shaa Allahu"
"Allah ya yarda, ina son ka miji na"
Wani irin dad'i ne ya lullube Lawwali, kalmar da ba wanda ya taba furta masa bayan qanwar shi sai Kuma ita, amma a bakin Mubaraka kad'ai ya fara jin wannan kalma, se ga shi ya samu matar dake yawan furta masa, yi ya yi kamar bai ji ba ya ɗan had'e gira ya ce,
"Na'am mi ki ka ce??"
Murmushi tayi dan ta gane me yake nufi, so yake ta maimaita masa, tashi tayi ta haye jikin shi, ta kwantar da shi a saman gadon sosai, ta yanda suke fuskantar junan su, sai da ta sumbace shi sosai sannan ta kalli kwayar idon shi ta ce,
"Cewa nayi....ina son hancin ka, da idon ka, da nan wajen..(ta nuna lips din shi) ina son kowacce gaba da ke jikin ka...ina son ka, ko da ace ni makauniya ce, kuma kurma ce, sannan bebiya ce, zan qirqiri kowacce hanya ce dan sanar da kai ni Sultana ina son ka Auwal, ba zan taba dena son ka a raina ba, har sai sanda na dena numfashi a duniya, ina maka son da ban taba yi wa wani ba, kai ne na farko a cikin zuciya ta, kuma kai ne na qarshe"
Wani irin numfashi mai sauti Lawwali ke saukewa ya rasa kalar dad'in da Sultana ke sanya shi ji a wanan lokaci, rungume ta ya yi sosai a jikin shi, har sai da ta saki wata siririyar qara, sannan ya sake ta ya na murmushi.
"Yi hankuri Sultyna, ji nikai kamar na bude fata da tsokar jiki na, na balle qashin da ya yi wa zuciya ta rumfa na ajiye ki a can ciki ki zauna daram, saboda yanda nake jin...."
Shiru ya yi bai furta ba, a hankali ta daga kan ta, cikin wani kallo mai kashe jiki, ta na lasar leben ta na qasa ta ce,
"Me ka ke ji?"
"Ina jin son ki Sultana, ina jin qaunar ki sultana, ba na son rabuwa da ke har bayan mutuwa ta, amma na san zai wahala mu had'u, saboda kowa makomar shi d...."
Ba tare data shirya ba ta ji saukar wasu hawaye Masu zafi, a kuncin ta, dan kuwa ta fuskanci me yake so ya fada,
"Subhanallahi, haba haba Auwal, ka dena kalar wannan tunanin, rahamar Allah mai yalwa ce, Allah ba so ya ke ya sanya bayin shi a wuta ba, Allah so yake bayin shi masu zunubi su tuba domin ya yafe musu, ya lullube su da rahamar shi komai laifin su, wanda ma ya yi shirka ga Allah in ya tuba kan ya mutu Allah na yafe masa ballantana kai, da baka taba duqawa gaban boka ko malam ba, sannan baka sani ba, ni din da ka ke wa kallon zan shiga aljannah wataqila Allah ya sanya ka a aljannah din mu zauna tare saboda ni din, sannan Allah zai iya jarabta ta da wani abun, ni kuma na yi wasa da shi na aikata zunubin da zai kai ni wuta, hadisi ne fa guda, akwai mutanen da za su yi ta aikata ayyuka irin na 'yan aljannah, saura kad' an su shiga aljannar, amma se su aikata aiki irin na 'yan wuta, se Allah ya sanya su a wutar, sannan akwai mutanen da za su yi ta aiki irin na' yan wuta, sauran kad'an su shiga wutar se kawai su yi aiki irin na 'yan aljannah, sai Allah ya kare su ya sanya su a aljannah, ka gani? Allah ba ta inda baya wanzar da rahama da ikon shi"
"Sultana ban taba shirka ba, amma ina taimaka wa masu yi, duk abinda mahaifin ki ya buqata da sauran 'Yan siyasa a baya ko mene shi ina samar musu shi, duk da na san tsafi za a yi da abun"
Hawayen ta ne suka qaru, jin cewar har da mahaifin ta a aikata shirka,
"Ka yi istigfar Allah zai amsa, ka yi da kyayyawar niya, Allah zai yafe maka"
"Allah na tuba ka yahe min, Allah ka yahe min manya da qananan zunubbai na, Allah ka yi min rahama, ka cika min buri na,"
"Ameen,"
Kafin bacci ya ɗebe su, sun tattauna akan abubuwa da dama, sun kuma tsara duk wani abu da ya kamata su aikata a gaba, a haka bacci ya dauke su suna manne da junan su.
***************************
Kamar yanda Isah ya yi alqawari, ya siyi goro mai yawan gaske, dan tafiya Makka, wanan karon dubu hamsin casss ya cake wa Hansatu, amma bata ci su a banza ba, sai da ya mori jikin ta da kyau da kyau, dan duk girman ta, da jarumtar ta, sai da ta dinga shiga ruwan zafi, Ita dai ta sawa ran ta, ba zai sake ganin wani rawar kan son shi awajen ta ba, tunda ta yi a baya bai mata amfani ba, sannan ba zai sake ganin murmushin ta ba, tunda a baya sai da ta ce wa audiga bata iya murmushi ba,ta fita iyawa, duk bata samu ribar murmushin ba,hakan kuwa na matuqar damun Isah, kula da cewar ko sau nawa zai neme ta ba zata qi ba,shi ya sa ya ke fanshe haushin rashin sakewar a jikin ta.
Hajiyar Hansatu da Yaya Musa sun yi qoqari sosai wajen ba Isah wasu kudin da zai qara akan jarin shi, sai da ya musu sallama sannan aka bada mota kamar wancan karon aka kai shi airport, wannan karon ko kwalla Hansatu bata yi ba, balle ta koka, Isah kuwa ya ji haushi matuqa, sannan ta ce ba zata yi rakiya ba, a fusace ya fad'a mota, aka tafi kai shi,ko da takoma sai ta ce wa Hajiya ita bata so ta ga ya tafi ya barta, kuka za tai, kuma bata so ta daga masa hankali,dan haka Hajiya bata ce komai ba, sai suka ci gaba da hirar su.
Isah sun isa airport, ya sauke kayan shi da komai, cikin dabarar da suke yi kar a gane goro ne, ya na tsaye wani mutum fari ya tsaya gefen shi, sallama ya masa shi ma ya amsa, sai ya ji maganar kamar ta Inyamuri ko bayerabe,
Mutumin ya fara yi wa Isah magana da turanci, Isah ba turanci, fuska ta muzanta da kunya, sai bawan Allahn ya gane Isah fa wala ingilishi, cikin gurbatacciyar Hausar shi ya ke tambayar Isah, Makka zai je ko Madina in sun isa Saudiya?
"Makka zani"
"Masha Allah, ni ma can nake da zama, ina da gida da iyali a can, kai fa ina ka ke zama?"
"Ni a hotel kawai nake sauka, banda gidan zama,"
"Allah Sarki, ka fad'a min inda ka ke sauka in na samu natsuwa zan neme ka, se ka dawo gida na da zama, tunda duk qasar mu d'aya, in a foreign land in ka ga d'an qasar ku ji ka ke kamar d'an uwanka ne"
Sunan hotel din da yake sauka ya sanar da bawan Allahn nan ya na ta murna, a qalla ba shi ba biyan kudin hotel, zama suka yi tare, suna ta hira, kamar abokan juna, duk inda CCTV camera yake a wajen bawan Allahn nan ya sani, kuma daidai gwargwado juya bayan shi yake, ba ya bari fuskar shi ta hasku, ya yi shiga irin ta larabawa ya saka face mask, se surutu yake wa Isah da gurbatacciyar hausar shi, Isah kuwa banda washe baki ba abinda yake.
Sai da aka shiga jirgi ne suka rabu, saboda wajen zaman su ba daya bane.
Tafiya ta miqa zuwa Saudiya, Isah ba abinda ya ke banda tunanin Hansatu, wannan karon ji yake kamar ya bar wani bangare na jikin shi, qudirtawa ya yi in Allah ya sauke shi lafiya, ita zai fara kira su gaisa.
**********************
A hanyar su ta zuwa garin na Zamfara duk wani motsi na Mubaraka na kan idon Taheer, zuciyar shi kuwa na ta kakkaryewa zuwa qananan pieces ,ya yi zurfi akan son ta ba tare da ya sani ba, wataqila dalilin gano ya na son nata, rabuwar da ta zo musu ba tare da shiri bane, da ya kula ya na son ta tun da, da ya yad'a manufar shi a wajen ta, gashi yanzu lokaci ya qure masa.
Mubaraka ce ta yi qarfin halin yi masa magana, ta ce,
"Yah Taheer akwai damuwa ne?"
Da sauri ya sanya murmushin yaqe ya ci gaba da tuqi, bai ce komai ba, tafiya suke kamar ba zai magana ba, can kamar wanda aka shaqe ya ce,
"Yanzu in kin tafi shikenan? Mantawa zakiyi da mu ko? Ga yaran ki can kin bar su suna ta kuka, ke kad'ai ka lallashin su in su na rikici, sun hi sabawa da ke,gashi zaki tafi ki bar su"
"Yah Taheer ku din wani bangare ne mai girma a rayuwa ta, ba zan taba manta wa da ku ba, ka sani na jima ban ga yayana ba, ina kewar shi sosai, amma in na je na gan su, ai zan koma wajen ku, in Allah ya yarda"
Wani irin murmushi Taheer ya sake, har da sosa kai, murmushin shi ya bawa Mubaraka mamaki, sai ita ma ta fara murmushin, cikin daurewar kai, dan ta kasa fahimtar inda Yah Taheer din ya dosa da wannan bayyanannen farin cikin................
*Allah kai ku lahiya ke dai, mu ai mun gane murmishin meye😂😂*
💅🏻 *A GARIN MU* 💅🏻
BY HAERMEEBRAERH
PAGE 53: