Sashe 19
A Garin Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Dafa kan ta ya yi, sannan ya rungume ta kadan, Sultana da ke kallon su cikin sha'awa da burgewa ce tai saurin daukan su a hoto ta na murmushi, hannu Lawwali ya zira aljihu ya bata dari biyar,sannan ya koma mota, ta na ta daga nasa hannu shi da Sultana ,sultana ma hannu ta daga mata, dauke da murmushi, zai tada motar kenan aka fita break, dan tsayawa ya so yi ya ga shigar Mubaraka, sai kuma ya fasa, ya bata ma Sultana lokaci matuqa ba tare da ya yi tunani Ba, sai a wannan lokacin ya ga tsaurin idon shi .
Hakuri ya dinga bawa Sultana, har sai da ta masa shiru, tunda ta ce ba komai, amma yaqi ya dena bata hakuri.
"Ran ki shi dade kin yi shiru, ko dai ba a yafe min laifi na bane?"
"Wa ya ce maka ka yi lehi? Ai kai lambar yabo ya kamata a baka, a matsayin ka na yayan da ya fi kowanne yaya so da qauna tare da kulawa ga qauna tai, ina ganin soyayya da kusanci na da Sultan amma naku, ya burge ni sosai"
"Koh Ran ki shi dade?ina godiya da yabawa, yabon ki ya fi duk wata lambar yabo ko girma da za a bani, "
Murmushi ta samu kan ta da yi, ba ta sake magana ba har suka isa, shi kuwa leqen ta ta madubi, shi ne ya zama aikin shi .
Bude mata qofar yayi, sannan ya take mata baya har office din ta, akwai mutanen da ta kula da su a jiya da ta ke bada taimakon nan, yau ma sun zo, su na ganin ta suka taso, fess da su,da alama mutane ne masu ilimi.
Har office suka je, Lawwali ne ya gabatar mata da su, domin ya san su, suma 'yan gwagwarmayar siyasar mahaifin ta ne, amma su mutane ne masu gaskiya da amana, gwamna na amfani da su in ya na son isar da saqon addini, ko kuma saqo wajen mutanen kirki, dan ya siye zuciyar mutane a ce shi din na Allah ne.
Ya rasa dama aikin da zai basu tun kafuwar gwamnatin shi, kullum suka je neman aiki hakuri yake basu, bude wannan NGO ya taimake shi sosai, dan haka ya ce su zo su taya sultana aikin.
Sultana ta ji dadin ganin su sosai , dan haka ba bata lokaci ta tattauna da su, ta kuma zabawa kowa bangaren da ya dace da shi .
Da taimakon su ta fara kasafin yanda zata gudanar da qungiyar, aiki ya sha kanta, da wannan damar Lawwali ya samu, ya tafi gida ba tare da sanin ta ba.
Ko da ya isa ya wuce Yabbuga a qofar gidan Asshibi, ta qurawa motar shi ido ta na son tai gulma dan bata gane motar waye ba,idon su karaf ya fada a na junan su, rakubewa ta yi a jikin ginin gidan Asshibi ta na salatin da ko iyawa ba ta gama yi ba,
Lawwali da ya san yanda Yabbuga ke mugun tsoron shi ne ya ci wani wawan burki dan nesa da su, ta na ganin haka, sai ta yi zaton baya ze yi ya je wajen su, bangaje Asshibi ta yi, ta afka gidan ta, ta na salati, ko ina na jikin ta rawa yake, Lawwali kuwa me zai banda dariya,qarasa wa ya yi gidan su,ya bude ya shige .
Lamishi na ta baccin ta hankali kwance.
A tsaye ya tsaya mata, ya ce
"Lamishi...Lamishi, shin kwana ki kai ko mi?"
Bude ido ta yi, tare da qanqance su, tsaki ta doka sannan ta ce,
"Sannu uba na, nicce sannu ubana, lalatacce tambadadde fado min a kai za ka yi? Ka tsaya min a ka kamar za ka hwado?"
"Ba wannan ya kawo ni ba, Barakana ba zata yi bautar gidan Gwauna ba,in ki na bari har ki ji sauqi tau, in baki bari ki hakura da aikin, ai dama kun tsufa barin ku kawai sun kai dan an saba, amma me kuke in kun tai?"
Kofin da ke gefen ta ta dauka ta maka masa a guiwa, ko gezau be ba, yo wace wahala ce shi be sha ba,
"Ka hwa rammin Lawwali, (ka fa raina ni Lawwali) in ce ga abinda za ai ka ce ah ah? Za ta dawo ta samen tunda ta kai qarata wajen ubana"
"Ni dai na fada maki, bata koma zuwa aiki wani gida, sai da son ran ta"
"Ka san bana jin magana, se ka buga zan gane me ka ke cewa ubana...kuma wane irin kaya ne na gani jikin ka? Jahili dai ka ke balle in ce ko aiki ka samu na taimakon qasa"
Ran shi ya yi mummunan baci da kalmar Jahili data jefe shi da ita, ba dan ya na musun shi din jahili bane, amma su waye silar zaman shi Jahilin?
Wani mugun kallo ya wurga mata, sannan ya sa kai ya bar gidan.
Zagin dai da ta saba, wanda shi ne ya dauki kaso saba'in na lalacewar shi, shi ta dinga qunduma masa, ta na maimaitawa, tare da fadin Mubaraka za ta same ta, su a dole qungiyar 'yan hadin kai, to duk abin su ita ta haife su, sai ta so kowa ya zauna lafiya, da sauran kalamai munana marasa dad'in saurara.
Da misalin qarfe uku na rana suka koma gida, Sultana ta so lokacin tashin su Mubaraka bai wuce ba su dauko ta, haka nan take jin son yarinyar, ta alaqanta hakan da ilimin da ta kula Mubaraka na da shi.
Sun isa gida sun tarar da Mubaraka ta kwaso wankin kayan sultana daga ɓangaren wanki na gidan, za ta mayar cikin gida.
Ko a fuska ran Lawwali bai ɓaci ba, tunda Mubaraka ma bata da damuwa akan hakan, shi dai ko ma mene zatai ya zama ta na son abun, da kuma dukkan alama ta na jin dadin aikin, ba bacin rai a fuskar ta, sai ma walwala.
Da hanzari ta aje kayan ta nufe shi, tare da yi musu sannu da zuwa baki dayan su, jakar Sultana ta amsa, sai sultana ta riqe, cikin murmushi ta ce,
"Na gode, na hutar da ke, kar gatan ya min yawa, ga wanki kin debo, a ina za ki riqe jaka? In yau kin kai min gobe wa zai kai min?"
"Ko Ni Kin kai wa izini har ciki sai in kai miki, ballantana Mubaraka,"
Kallon Lawwali Sultana ta yi, tare da sakin murmushi mai kyau, ta wuce ciki, ta na shiga suka tafa,
"Yah Auwal da alama Aunty Sultana na yin ka hwa, ka ga wani murmushi da tayyi maka?"
"Allah ya sa, wannan murmushi halayyar ta ne, kowa ma yi mishi ta kai, Allah shi nuna min ta yi min irin wanda ni kai mata,....ke ci abinci?"
"Ameeen Yah Auwal, eh na ci abinci ,kafin Mama(Mai Buruji) ta tafi gida ta ban abinci, nima na kusan gamawa, wankin sultana kawai zan je in isuwa"
"Tau ya yi, In ke qare ki yi min magana, zan jira ki can garka, mu tai gidana, da kai na zan maishe ki gida, dazu na tai gida ai"
Nan ya bata labarin me ya faru tsakanin shi da Lamishi, idanun ta ne suka kawo ruwa ta ce,
"Ni dai dama baka tai ba wallah, yanzu ta na iya gwada min bone kan haka da kai, ya kamata ka rage kulawa da ni, tunda bata son haka nan"
Wani kallon baki da hankali ya mata, sannan ya duqa ya dauki kwandon wankin, ya dora Mata akai, ya tallabe qeyar ta cikin wasa, yar qara ta saki, ya mata gwalo ya tafi, tare da sanar da ita yana jiran ta, sultana da ke tsaye jikin window'n dakin ta ne,ta saki labule, ta na murmushi, su na burge ta sosai.
Har dakin sultana Mubaraka ta shiga, bayan ta yi sallama, ta bata izinin shiga, ita ta jera mata kayan inda ya dace ,sannan ta tambaye ta ko da abinda zata mata?
"Babu komai, amma ina so na tambaye ki,"
"Allah ya sa na sani"
"Inshaa Allah, kin ma sani, Ni kuwa na ce, ke da Auwal maman ku daya Abban ku daya?"
Da kallo Mubaraka ta bi Sultana........
Kallon da ya gajiyar da ni burutu😂😂
A GARIN MU
WRITTEN BY HAERMEEBRAERH
PAGE 19:
"Yaya na ne, uwar mu guda uban mu guda da shi, amma ya girme ni sosai, mu na da wasu qannen maza ne su, guda biyu,"
Ajiyar zuciya sulatana ta sauke, sannan ta yi murmushin ta da ke qawata kyaun fuskar ta ta ce,
"Masha Allah, makarantar ku guda da qannen naki?"
"Ai su Jameelu ba su zuwa makaranta,yawon su kawai suke a unguwa, duk gidan mu ni kadai ta ka zuwa makaranta"
Gyara zama Sultana ta yi, cikin rashin fahimta ta ke kallon Mubaraka da ke mata bayani,
"Yah Auwal ya yi karatun allo, har ya kai ga sauke qur'ani, kamar yanda na ji labari, amma ban taba jin labarin ya yi boko ba, zama da masu ilimi na ya sanya shi koyon karatu da rubutu, sannan ya iya turanci kad'an, amma bai je makaranta ba, ni kuma kin ga wadda karatun nawa shi ke, yau in an bar ni na tai, gobe ba zani ba,su Jameelu kuwa ba su ko son zuwa makarantar Allah balle ta bature"
"Ikon Allah, zan so zuwa shiyyar ku niga wadda take, watarana"
"Kai ka kaiii, lallai ko da mun ji dad'i mara misali, ace ke da kan ki kin tai shiyyar mu,ko ba dan matsayin da ki ke da shi ba ma, domin kyawun halin ki da kullum Umman mu ke fad'a a shiyyar mu"
"Mubaraka kenan, to ni din wata ce daban? Ni ma mutum ce kamar kowa na duniya, a duniya babu wanda ya fi wani, sai wanda ya fi tsoron Allah, yawan dukiya, matsayi, muqami duk ba su na mutum ba, tsoron Allahn da bawa shike da shi, da kuma kyakkyawar mu'amala su ka yin mutum, ke gane?"
Daga kai Mubaraka ta yi, sannan ta ce,
"Aunty in tambaye ki? Dan Allah kar ran ki ya ɓaci da tambaya ta"
Kada kai Sultana ta yi, sannan ta bada hankalin ta ga kallon Mubaraka.
"Aunty yaushe na zaki aure?"
Hakuri ya dinga bawa Sultana, har sai da ta masa shiru, tunda ta ce ba komai, amma yaqi ya dena bata hakuri.
"Ran ki shi dade kin yi shiru, ko dai ba a yafe min laifi na bane?"
"Wa ya ce maka ka yi lehi? Ai kai lambar yabo ya kamata a baka, a matsayin ka na yayan da ya fi kowanne yaya so da qauna tare da kulawa ga qauna tai, ina ganin soyayya da kusanci na da Sultan amma naku, ya burge ni sosai"
"Koh Ran ki shi dade?ina godiya da yabawa, yabon ki ya fi duk wata lambar yabo ko girma da za a bani, "
Murmushi ta samu kan ta da yi, ba ta sake magana ba har suka isa, shi kuwa leqen ta ta madubi, shi ne ya zama aikin shi .
Bude mata qofar yayi, sannan ya take mata baya har office din ta, akwai mutanen da ta kula da su a jiya da ta ke bada taimakon nan, yau ma sun zo, su na ganin ta suka taso, fess da su,da alama mutane ne masu ilimi.
Har office suka je, Lawwali ne ya gabatar mata da su, domin ya san su, suma 'yan gwagwarmayar siyasar mahaifin ta ne, amma su mutane ne masu gaskiya da amana, gwamna na amfani da su in ya na son isar da saqon addini, ko kuma saqo wajen mutanen kirki, dan ya siye zuciyar mutane a ce shi din na Allah ne.
Ya rasa dama aikin da zai basu tun kafuwar gwamnatin shi, kullum suka je neman aiki hakuri yake basu, bude wannan NGO ya taimake shi sosai, dan haka ya ce su zo su taya sultana aikin.
Sultana ta ji dadin ganin su sosai , dan haka ba bata lokaci ta tattauna da su, ta kuma zabawa kowa bangaren da ya dace da shi .
Da taimakon su ta fara kasafin yanda zata gudanar da qungiyar, aiki ya sha kanta, da wannan damar Lawwali ya samu, ya tafi gida ba tare da sanin ta ba.
Ko da ya isa ya wuce Yabbuga a qofar gidan Asshibi, ta qurawa motar shi ido ta na son tai gulma dan bata gane motar waye ba,idon su karaf ya fada a na junan su, rakubewa ta yi a jikin ginin gidan Asshibi ta na salatin da ko iyawa ba ta gama yi ba,
Lawwali da ya san yanda Yabbuga ke mugun tsoron shi ne ya ci wani wawan burki dan nesa da su, ta na ganin haka, sai ta yi zaton baya ze yi ya je wajen su, bangaje Asshibi ta yi, ta afka gidan ta, ta na salati, ko ina na jikin ta rawa yake, Lawwali kuwa me zai banda dariya,qarasa wa ya yi gidan su,ya bude ya shige .
Lamishi na ta baccin ta hankali kwance.
A tsaye ya tsaya mata, ya ce
"Lamishi...Lamishi, shin kwana ki kai ko mi?"
Bude ido ta yi, tare da qanqance su, tsaki ta doka sannan ta ce,
"Sannu uba na, nicce sannu ubana, lalatacce tambadadde fado min a kai za ka yi? Ka tsaya min a ka kamar za ka hwado?"
"Ba wannan ya kawo ni ba, Barakana ba zata yi bautar gidan Gwauna ba,in ki na bari har ki ji sauqi tau, in baki bari ki hakura da aikin, ai dama kun tsufa barin ku kawai sun kai dan an saba, amma me kuke in kun tai?"
Kofin da ke gefen ta ta dauka ta maka masa a guiwa, ko gezau be ba, yo wace wahala ce shi be sha ba,
"Ka hwa rammin Lawwali, (ka fa raina ni Lawwali) in ce ga abinda za ai ka ce ah ah? Za ta dawo ta samen tunda ta kai qarata wajen ubana"
"Ni dai na fada maki, bata koma zuwa aiki wani gida, sai da son ran ta"
"Ka san bana jin magana, se ka buga zan gane me ka ke cewa ubana...kuma wane irin kaya ne na gani jikin ka? Jahili dai ka ke balle in ce ko aiki ka samu na taimakon qasa"
Ran shi ya yi mummunan baci da kalmar Jahili data jefe shi da ita, ba dan ya na musun shi din jahili bane, amma su waye silar zaman shi Jahilin?
Wani mugun kallo ya wurga mata, sannan ya sa kai ya bar gidan.
Zagin dai da ta saba, wanda shi ne ya dauki kaso saba'in na lalacewar shi, shi ta dinga qunduma masa, ta na maimaitawa, tare da fadin Mubaraka za ta same ta, su a dole qungiyar 'yan hadin kai, to duk abin su ita ta haife su, sai ta so kowa ya zauna lafiya, da sauran kalamai munana marasa dad'in saurara.
Da misalin qarfe uku na rana suka koma gida, Sultana ta so lokacin tashin su Mubaraka bai wuce ba su dauko ta, haka nan take jin son yarinyar, ta alaqanta hakan da ilimin da ta kula Mubaraka na da shi.
Sun isa gida sun tarar da Mubaraka ta kwaso wankin kayan sultana daga ɓangaren wanki na gidan, za ta mayar cikin gida.
Ko a fuska ran Lawwali bai ɓaci ba, tunda Mubaraka ma bata da damuwa akan hakan, shi dai ko ma mene zatai ya zama ta na son abun, da kuma dukkan alama ta na jin dadin aikin, ba bacin rai a fuskar ta, sai ma walwala.
Da hanzari ta aje kayan ta nufe shi, tare da yi musu sannu da zuwa baki dayan su, jakar Sultana ta amsa, sai sultana ta riqe, cikin murmushi ta ce,
"Na gode, na hutar da ke, kar gatan ya min yawa, ga wanki kin debo, a ina za ki riqe jaka? In yau kin kai min gobe wa zai kai min?"
"Ko Ni Kin kai wa izini har ciki sai in kai miki, ballantana Mubaraka,"
Kallon Lawwali Sultana ta yi, tare da sakin murmushi mai kyau, ta wuce ciki, ta na shiga suka tafa,
"Yah Auwal da alama Aunty Sultana na yin ka hwa, ka ga wani murmushi da tayyi maka?"
"Allah ya sa, wannan murmushi halayyar ta ne, kowa ma yi mishi ta kai, Allah shi nuna min ta yi min irin wanda ni kai mata,....ke ci abinci?"
"Ameeen Yah Auwal, eh na ci abinci ,kafin Mama(Mai Buruji) ta tafi gida ta ban abinci, nima na kusan gamawa, wankin sultana kawai zan je in isuwa"
"Tau ya yi, In ke qare ki yi min magana, zan jira ki can garka, mu tai gidana, da kai na zan maishe ki gida, dazu na tai gida ai"
Nan ya bata labarin me ya faru tsakanin shi da Lamishi, idanun ta ne suka kawo ruwa ta ce,
"Ni dai dama baka tai ba wallah, yanzu ta na iya gwada min bone kan haka da kai, ya kamata ka rage kulawa da ni, tunda bata son haka nan"
Wani kallon baki da hankali ya mata, sannan ya duqa ya dauki kwandon wankin, ya dora Mata akai, ya tallabe qeyar ta cikin wasa, yar qara ta saki, ya mata gwalo ya tafi, tare da sanar da ita yana jiran ta, sultana da ke tsaye jikin window'n dakin ta ne,ta saki labule, ta na murmushi, su na burge ta sosai.
Har dakin sultana Mubaraka ta shiga, bayan ta yi sallama, ta bata izinin shiga, ita ta jera mata kayan inda ya dace ,sannan ta tambaye ta ko da abinda zata mata?
"Babu komai, amma ina so na tambaye ki,"
"Allah ya sa na sani"
"Inshaa Allah, kin ma sani, Ni kuwa na ce, ke da Auwal maman ku daya Abban ku daya?"
Da kallo Mubaraka ta bi Sultana........
Kallon da ya gajiyar da ni burutu😂😂
A GARIN MU
WRITTEN BY HAERMEEBRAERH
PAGE 19:
"Yaya na ne, uwar mu guda uban mu guda da shi, amma ya girme ni sosai, mu na da wasu qannen maza ne su, guda biyu,"
Ajiyar zuciya sulatana ta sauke, sannan ta yi murmushin ta da ke qawata kyaun fuskar ta ta ce,
"Masha Allah, makarantar ku guda da qannen naki?"
"Ai su Jameelu ba su zuwa makaranta,yawon su kawai suke a unguwa, duk gidan mu ni kadai ta ka zuwa makaranta"
Gyara zama Sultana ta yi, cikin rashin fahimta ta ke kallon Mubaraka da ke mata bayani,
"Yah Auwal ya yi karatun allo, har ya kai ga sauke qur'ani, kamar yanda na ji labari, amma ban taba jin labarin ya yi boko ba, zama da masu ilimi na ya sanya shi koyon karatu da rubutu, sannan ya iya turanci kad'an, amma bai je makaranta ba, ni kuma kin ga wadda karatun nawa shi ke, yau in an bar ni na tai, gobe ba zani ba,su Jameelu kuwa ba su ko son zuwa makarantar Allah balle ta bature"
"Ikon Allah, zan so zuwa shiyyar ku niga wadda take, watarana"
"Kai ka kaiii, lallai ko da mun ji dad'i mara misali, ace ke da kan ki kin tai shiyyar mu,ko ba dan matsayin da ki ke da shi ba ma, domin kyawun halin ki da kullum Umman mu ke fad'a a shiyyar mu"
"Mubaraka kenan, to ni din wata ce daban? Ni ma mutum ce kamar kowa na duniya, a duniya babu wanda ya fi wani, sai wanda ya fi tsoron Allah, yawan dukiya, matsayi, muqami duk ba su na mutum ba, tsoron Allahn da bawa shike da shi, da kuma kyakkyawar mu'amala su ka yin mutum, ke gane?"
Daga kai Mubaraka ta yi, sannan ta ce,
"Aunty in tambaye ki? Dan Allah kar ran ki ya ɓaci da tambaya ta"
Kada kai Sultana ta yi, sannan ta bada hankalin ta ga kallon Mubaraka.
"Aunty yaushe na zaki aure?"