Sashe 90
A Garin Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ya na nan tsaye likita ke sanar da shi, sun samu numfashin ta ya daidaita, cikin farin ciki, ya shiga, ta na kwance ta na bacci, dan kuwa allurar bacci akai mata, saboda zuciyar ta ta samu hutu.
Wayar Sultan ke ta ringing, ko da ya duba, sunan Sultana ne a jiki, bai san sanda ya fashe da wani irin kuka ba.
"Allah mun gode maka, duk abinda ka yi shi ne daidai, ba ka barin wani a duniya dan wani ya ji dadi, da ka na barin wani a duniya dan wani ya ji dadi,da ka barwa Annabi Muhammad Nana Khadeejah, da ka barwa Nana A'isha Annabi Muhammad, da baka raba Nana Fadeema da Annabi Muhammad ba a duniya, da ka bar mana shi mu al'ummar shi mun ji dadi, duk abinda ka tsara shi ne daidai, Allah ina roqon ka da ka kawo mana komai da sauqi, ka sanyaya zuqatan mu, ka bamu hakuri da juriya da danganar rashin makusantan mu"
Ringing din wayar ne ya sake maida shi cikin hankalin shi, dauka ya yi cikin sanyin murya, sallamar Hajiya ya ji, ta na tambayar shi me ya faru, ya fita a firgice.
"Hajiya ki na ina ne?"
"Gani tare da su Sultana, a bangaren Daddyn ku"
"Ok Hajiya ki sauka qasa za mu yi magana , dan Allah kar ki daga murya har sultana ta ji, ke dai san ta na da juna biyu ko?"
Gaban Hajiya Ikee ne ya dinga bugawa, a sukwane ta sauka qasa, dan jin me yake faruwa, ta na zuwa qasa parlourn manyan baqi ta wuce, ba kowa a wajen, ya ma kwana biyu ba a shiga ba.
Ta na shiga ta sanar da shi ta sauka qasan, cikin raunin murya Sultan ya sanar da ita abinda ke faruwa, salati ta dinga yi,jikin ta na matuqar rawa, nan take ta dinga hango Lawwali, kallon wajen da ya taba shaqe ta tayi, da kalaman shi, tunawa da irin girmama ta da kulawa da ita da sultana da yake yi a yanzu ta yi, nan da nan hawaye suka dinga rige rigen sauka daga idanun ta.
Sultan na ta magana bata jin shi, dan haka ya kashe, sai da Hajiya Ikee ta ci kukan ta a wajen, sanan ta miqe, ta bar parlourn, dakin Sultana na da ta shiga ta wanke fuskar ta, sannan ta koma wajen su Sultanan, ganin sultana ta yi a zaune ta dafe kan ta, cikin tausaya wa Hajiya Ikee ta je wajen ta, ta dafa ta, daga kai sultana ta yi a hankali ta kalli Hajiyan, ta ce,
"Hajiya kai na ciyo ya kai min, ga abinda ke ciki na na ta naushi na, motsin da yake min yau ban taba jin irin shi ba, dama in ciki ya kai wata bakwai haka ya ke yi?"
"kar ki damu juyi shi kai, kunga yanzu dai ya kamata mu je mu kwanta shad'ai ta yi, bai kamata mu zauna zaman jiran su ba, tunda dai ba mu za a kawo wa amarya ba"
Dariya cousins din shi suka yi, suka miqe,tare da yi wa su Sultana sai da safe.
Hajiya Ikee cikin dabara ta kashe wayar Sultana, ta boye.
Sun yi shirin bacci gaba dayan su,sun kwanta, Hajiya ta kasa bacci, Sultana ma idanun ta biyu, ta rasa dalilin da ya sa Lawwali be kira ta ba, gashi har sha biyu na dare ta gota.
Jin motsin Hajiya ya yi yawa ne ya sa ta tabbatar da cewa Hajiya ba bacci take ba,
"Hajiya ina waya ta?"
Shiru Hajiya ta yi, kamar mai bacci, sultana ma shiru ta yi, daga baya ta sauka ta hau duba wayar ta.
Bata gan ta ba, sai kawai ta dauki ta Hajiya,ta nemo No Lawwalin, ta Kira.
Ko da ta kira ta jima ta na ringing ba a daga ba, sai daga baya,dan sandan da ke riqe da wayar Lawwali ne ya ga an rubuta,
'Hajiya'
A jikin wayar, dauka ya yi, tare da yin sallama,
"Hajiya har yanzu su na asibiti ba a bada gawar shi ba, akwai wasu 'yan bincike da muke so mu gudanar"
Daga can gefe ta ji ana ma mutumin da take magana da shi fad'a,kuma an kashe wayar.
"Gawar wa za a bada?"
Kit ta ji an kashe wayar, kafin a kashe ta ji ana Wa wanda ya amsa wayar fada,akan me ya sa bai kashe wayar ba duka har sai an gama bincike.
Cikin jikin ta ne ya harba da qarfi, sai da ta duqa a wajen, ta jima ta na cije leben ta, Hajiya Ikee kuwa na kwance hawayen tausayin yar ta na zuba mata, yau 'yar ta za ta fara dandana azabar rabuwa da miji, azabar rabuwa da miji daban ce a rayuwa.
Murya can qasa ta ce,
"Hajiya, Hajiya, ciki na,....Hajiya na kira wayar Auwal an ce ba a bada gawa ba, gawar wa za a basuwa?"
Shiru Hajiya Ikee ta yi, Sultana na nan a duqe ta juya ta kalli Hajiya ta ga alamar idon ta biyu, amma ba ta amsa ba.
Tashi ta yi ta na duqawa da kyar ta zauna a bakin gadon, ta fara buga cinyar Hajiya ta na tashin ta, kuka take so ta yi, amma ta kasa, saboda fargabar da ta cika zuciyar ta, fatan ta Allah ya sa ba gawar mijin ta ake magana akai ba.
Hajiya dai shiru ya qare, dole ta tashi ta zauna, kukan da Sultana ta ga Hajiya na yi ne ya sanya ta gyara zama da kyau,
"Hajiya dan girman Allah ki min magana, wam-mutu?"(wa ye ya mutu)
Kuka mai qarfi Hajiya ta fashe da shi, sannan ta ce,
"Sultana dukkan mai rai mamaci ne, mu yi fatan mu ma qarshen mu ya yi kyau, amma wanda Allah ya kira zuwa ga kushewa ba shi jinkiri, Sultana ki sawa kan ki salama,da dangana, ko...."
"Dan Allah Hajiya ki dena wanga dogon jawabi, ki sanar dani gawar wa za a basuwa? ina Auwal yake? me yah Sultan ya ce miki da ki ka kire shi dazu?"
"Sultana Ki yi hankuri, Allah ya bawa zucciyar ki hankuri, shi sanya maki juriya"
Idanun Sultana sun cika da hawaye, har bata gani, cikin daga murya ta ce,
"Wai waye ya mutu ne?"
Hajiya Ikee ka sa fada ta yi, ta na ta kuka,
"Auwal di na ne ya mutu Hajiya? Ki na so ki sanar da ni Auwal d'i na ne ya mutu? Inaaa ba gaskiya na ba wallah, ban yarda ba, ba gaskiya na ba, bari ki ga na kwanta sai da sahe, gobe zan koma gida na, tunda fatan mutuwa ki ke wa miji na"
Juyawa ta yi hawaye na zuba a idanun ta, ta kwanta, kasa kwanciyar ta yi, ta miqe tsaye, Hajiya Ikee ma miqewa ta yi, ta taro ta, saboda qoqarin faduwa da take,
"Ina zaki?"
"Gida za ni in ga ko ya na can ya na kwana,"
Riqe ta Hajiya ta yi, ta na kuka ta ce.
"Sultana kar ki zama mara tawakkali ga Allah mana, tunda ke san gaskiya Auwal ya rasu ki nutsu ki hwara yi mai addu'a,yanzu ita ya hi buqata, rasuwar mahaifin ku, mun yi aiki da jahilci mun biyewa kidimewar mutuwa mun dimauce, wannan karon bai kamata mu manta da Allah ba, bai kamata mu yi aiki irin na jahillai ba"
Shiru Hajiya Ikee ta ji Sultana ta yi, jikin ta ya sake, komawa gado ta yi da ita, ta kwantar da ita, ta na maimaita
"Hasbunallahu wa ni'imal wakeel, Innalillahi wa inna ilaihirraji'un"
Duk da ba daidai ta ke fada ba, amma dai ta koma ga Allah, (a yanzu fa abun ya zama ruwan dare, ka ji babbar mata ko qarama ba su iya fadin wasu kalmomi na tasbihi ga Allah ba, amma magana mai amfani da mara amfani fal harshen su, kalmomi na tasbihi kuwa na shan baqar wahala a harsunan su)
Ruwa ta yayyafa wa Sultana, ta farfado, ta tafi ta debo mata mai kyau, dan ta bata ta sha.
Ko da ta dawo, zaune ta ga sultanan ta yi shiru, ta na kallon waje guda, ta yi tayi ta bata ruwan ta qi qarba, kuma ta qi magana, sun jima a haka, har qarfe biyu da rabi na dare,
Sultana mai yawan ibada ce, kallon lokaci ta yi, ta ga be kai lokacin tashin ta ba, cikin dauriya ta miqe, ta fada bayi, har ta yi tsarki ta daura alwala ta gama bata zubar da hawaye ba ko d'igo, sai da ta yi kabbara sallah ne, ta gan ta tsaye a gaban mahaliccin ta, kawai sai ta fashe da kuka.
Daga farkon sallar nan zuwa qarshen ta, ta yi ta ne cike da qasqantar da kan ta ga mahaliccin ta, ta na nemawa mijin ta, da mahaifin ta gafara, da rahamar Allah.
Ganin haka ne ya sa Hajiya Ikee ma yin alwala ta hau nafila, duk da cewa ba ta saba ba.
Washegari da safe kuwa.............
*Allah ya kai mu washegarin, dan Allh ku yi min hakuri akan mutuwar Lawwali, na san ba za ku so hakan ba, amma dukkan mai rai lokacin shi na zuwa, lokacin Lawwali ne ya yi, shima, namu muke jira Allah ya kyautata qarshen mu*
💅🏻 *A GARIN MU* 💅🏻
BY HAERMEEBRAERH
PAGE 65:
Washegari kuwa tun asuba Sultana ta ce wa Hajiya ta bata wayar ta, dan ta gano ita ga boye dan kar ta ji wannan mummunan labarin, Hajiya Ikee ba musu ta duqa qasan gado ta zaro waya, dake da qafa ta tura ta, santsin wajen ya sa ta shige can ciki, sai da ta wahala ta samu fiddo da wayar.
Ana bata ta kunna, ta kira Sultan, da fari bacci ya samu, a zaune a gefen gadon da Mubaraka ke kwance, ta na kira qarar wayar ta tashe shi, ya duba sai ya ga sultana ce, da sauri ya shafe idanun shi, ya qara dubawa, ya so ya qi dagawa, sai ya ga message din ta ya shiga wayar shi,
'Yah Sultan na san komai, ka sanar da ni inda kuke, gamu nan zuwa'
Wayar Sultan ke ta ringing, ko da ya duba, sunan Sultana ne a jiki, bai san sanda ya fashe da wani irin kuka ba.
"Allah mun gode maka, duk abinda ka yi shi ne daidai, ba ka barin wani a duniya dan wani ya ji dadi, da ka na barin wani a duniya dan wani ya ji dadi,da ka barwa Annabi Muhammad Nana Khadeejah, da ka barwa Nana A'isha Annabi Muhammad, da baka raba Nana Fadeema da Annabi Muhammad ba a duniya, da ka bar mana shi mu al'ummar shi mun ji dadi, duk abinda ka tsara shi ne daidai, Allah ina roqon ka da ka kawo mana komai da sauqi, ka sanyaya zuqatan mu, ka bamu hakuri da juriya da danganar rashin makusantan mu"
Ringing din wayar ne ya sake maida shi cikin hankalin shi, dauka ya yi cikin sanyin murya, sallamar Hajiya ya ji, ta na tambayar shi me ya faru, ya fita a firgice.
"Hajiya ki na ina ne?"
"Gani tare da su Sultana, a bangaren Daddyn ku"
"Ok Hajiya ki sauka qasa za mu yi magana , dan Allah kar ki daga murya har sultana ta ji, ke dai san ta na da juna biyu ko?"
Gaban Hajiya Ikee ne ya dinga bugawa, a sukwane ta sauka qasa, dan jin me yake faruwa, ta na zuwa qasa parlourn manyan baqi ta wuce, ba kowa a wajen, ya ma kwana biyu ba a shiga ba.
Ta na shiga ta sanar da shi ta sauka qasan, cikin raunin murya Sultan ya sanar da ita abinda ke faruwa, salati ta dinga yi,jikin ta na matuqar rawa, nan take ta dinga hango Lawwali, kallon wajen da ya taba shaqe ta tayi, da kalaman shi, tunawa da irin girmama ta da kulawa da ita da sultana da yake yi a yanzu ta yi, nan da nan hawaye suka dinga rige rigen sauka daga idanun ta.
Sultan na ta magana bata jin shi, dan haka ya kashe, sai da Hajiya Ikee ta ci kukan ta a wajen, sanan ta miqe, ta bar parlourn, dakin Sultana na da ta shiga ta wanke fuskar ta, sannan ta koma wajen su Sultanan, ganin sultana ta yi a zaune ta dafe kan ta, cikin tausaya wa Hajiya Ikee ta je wajen ta, ta dafa ta, daga kai sultana ta yi a hankali ta kalli Hajiyan, ta ce,
"Hajiya kai na ciyo ya kai min, ga abinda ke ciki na na ta naushi na, motsin da yake min yau ban taba jin irin shi ba, dama in ciki ya kai wata bakwai haka ya ke yi?"
"kar ki damu juyi shi kai, kunga yanzu dai ya kamata mu je mu kwanta shad'ai ta yi, bai kamata mu zauna zaman jiran su ba, tunda dai ba mu za a kawo wa amarya ba"
Dariya cousins din shi suka yi, suka miqe,tare da yi wa su Sultana sai da safe.
Hajiya Ikee cikin dabara ta kashe wayar Sultana, ta boye.
Sun yi shirin bacci gaba dayan su,sun kwanta, Hajiya ta kasa bacci, Sultana ma idanun ta biyu, ta rasa dalilin da ya sa Lawwali be kira ta ba, gashi har sha biyu na dare ta gota.
Jin motsin Hajiya ya yi yawa ne ya sa ta tabbatar da cewa Hajiya ba bacci take ba,
"Hajiya ina waya ta?"
Shiru Hajiya ta yi, kamar mai bacci, sultana ma shiru ta yi, daga baya ta sauka ta hau duba wayar ta.
Bata gan ta ba, sai kawai ta dauki ta Hajiya,ta nemo No Lawwalin, ta Kira.
Ko da ta kira ta jima ta na ringing ba a daga ba, sai daga baya,dan sandan da ke riqe da wayar Lawwali ne ya ga an rubuta,
'Hajiya'
A jikin wayar, dauka ya yi, tare da yin sallama,
"Hajiya har yanzu su na asibiti ba a bada gawar shi ba, akwai wasu 'yan bincike da muke so mu gudanar"
Daga can gefe ta ji ana ma mutumin da take magana da shi fad'a,kuma an kashe wayar.
"Gawar wa za a bada?"
Kit ta ji an kashe wayar, kafin a kashe ta ji ana Wa wanda ya amsa wayar fada,akan me ya sa bai kashe wayar ba duka har sai an gama bincike.
Cikin jikin ta ne ya harba da qarfi, sai da ta duqa a wajen, ta jima ta na cije leben ta, Hajiya Ikee kuwa na kwance hawayen tausayin yar ta na zuba mata, yau 'yar ta za ta fara dandana azabar rabuwa da miji, azabar rabuwa da miji daban ce a rayuwa.
Murya can qasa ta ce,
"Hajiya, Hajiya, ciki na,....Hajiya na kira wayar Auwal an ce ba a bada gawa ba, gawar wa za a basuwa?"
Shiru Hajiya Ikee ta yi, Sultana na nan a duqe ta juya ta kalli Hajiya ta ga alamar idon ta biyu, amma ba ta amsa ba.
Tashi ta yi ta na duqawa da kyar ta zauna a bakin gadon, ta fara buga cinyar Hajiya ta na tashin ta, kuka take so ta yi, amma ta kasa, saboda fargabar da ta cika zuciyar ta, fatan ta Allah ya sa ba gawar mijin ta ake magana akai ba.
Hajiya dai shiru ya qare, dole ta tashi ta zauna, kukan da Sultana ta ga Hajiya na yi ne ya sanya ta gyara zama da kyau,
"Hajiya dan girman Allah ki min magana, wam-mutu?"(wa ye ya mutu)
Kuka mai qarfi Hajiya ta fashe da shi, sannan ta ce,
"Sultana dukkan mai rai mamaci ne, mu yi fatan mu ma qarshen mu ya yi kyau, amma wanda Allah ya kira zuwa ga kushewa ba shi jinkiri, Sultana ki sawa kan ki salama,da dangana, ko...."
"Dan Allah Hajiya ki dena wanga dogon jawabi, ki sanar dani gawar wa za a basuwa? ina Auwal yake? me yah Sultan ya ce miki da ki ka kire shi dazu?"
"Sultana Ki yi hankuri, Allah ya bawa zucciyar ki hankuri, shi sanya maki juriya"
Idanun Sultana sun cika da hawaye, har bata gani, cikin daga murya ta ce,
"Wai waye ya mutu ne?"
Hajiya Ikee ka sa fada ta yi, ta na ta kuka,
"Auwal di na ne ya mutu Hajiya? Ki na so ki sanar da ni Auwal d'i na ne ya mutu? Inaaa ba gaskiya na ba wallah, ban yarda ba, ba gaskiya na ba, bari ki ga na kwanta sai da sahe, gobe zan koma gida na, tunda fatan mutuwa ki ke wa miji na"
Juyawa ta yi hawaye na zuba a idanun ta, ta kwanta, kasa kwanciyar ta yi, ta miqe tsaye, Hajiya Ikee ma miqewa ta yi, ta taro ta, saboda qoqarin faduwa da take,
"Ina zaki?"
"Gida za ni in ga ko ya na can ya na kwana,"
Riqe ta Hajiya ta yi, ta na kuka ta ce.
"Sultana kar ki zama mara tawakkali ga Allah mana, tunda ke san gaskiya Auwal ya rasu ki nutsu ki hwara yi mai addu'a,yanzu ita ya hi buqata, rasuwar mahaifin ku, mun yi aiki da jahilci mun biyewa kidimewar mutuwa mun dimauce, wannan karon bai kamata mu manta da Allah ba, bai kamata mu yi aiki irin na jahillai ba"
Shiru Hajiya Ikee ta ji Sultana ta yi, jikin ta ya sake, komawa gado ta yi da ita, ta kwantar da ita, ta na maimaita
"Hasbunallahu wa ni'imal wakeel, Innalillahi wa inna ilaihirraji'un"
Duk da ba daidai ta ke fada ba, amma dai ta koma ga Allah, (a yanzu fa abun ya zama ruwan dare, ka ji babbar mata ko qarama ba su iya fadin wasu kalmomi na tasbihi ga Allah ba, amma magana mai amfani da mara amfani fal harshen su, kalmomi na tasbihi kuwa na shan baqar wahala a harsunan su)
Ruwa ta yayyafa wa Sultana, ta farfado, ta tafi ta debo mata mai kyau, dan ta bata ta sha.
Ko da ta dawo, zaune ta ga sultanan ta yi shiru, ta na kallon waje guda, ta yi tayi ta bata ruwan ta qi qarba, kuma ta qi magana, sun jima a haka, har qarfe biyu da rabi na dare,
Sultana mai yawan ibada ce, kallon lokaci ta yi, ta ga be kai lokacin tashin ta ba, cikin dauriya ta miqe, ta fada bayi, har ta yi tsarki ta daura alwala ta gama bata zubar da hawaye ba ko d'igo, sai da ta yi kabbara sallah ne, ta gan ta tsaye a gaban mahaliccin ta, kawai sai ta fashe da kuka.
Daga farkon sallar nan zuwa qarshen ta, ta yi ta ne cike da qasqantar da kan ta ga mahaliccin ta, ta na nemawa mijin ta, da mahaifin ta gafara, da rahamar Allah.
Ganin haka ne ya sa Hajiya Ikee ma yin alwala ta hau nafila, duk da cewa ba ta saba ba.
Washegari da safe kuwa.............
*Allah ya kai mu washegarin, dan Allh ku yi min hakuri akan mutuwar Lawwali, na san ba za ku so hakan ba, amma dukkan mai rai lokacin shi na zuwa, lokacin Lawwali ne ya yi, shima, namu muke jira Allah ya kyautata qarshen mu*
💅🏻 *A GARIN MU* 💅🏻
BY HAERMEEBRAERH
PAGE 65:
Washegari kuwa tun asuba Sultana ta ce wa Hajiya ta bata wayar ta, dan ta gano ita ga boye dan kar ta ji wannan mummunan labarin, Hajiya Ikee ba musu ta duqa qasan gado ta zaro waya, dake da qafa ta tura ta, santsin wajen ya sa ta shige can ciki, sai da ta wahala ta samu fiddo da wayar.
Ana bata ta kunna, ta kira Sultan, da fari bacci ya samu, a zaune a gefen gadon da Mubaraka ke kwance, ta na kira qarar wayar ta tashe shi, ya duba sai ya ga sultana ce, da sauri ya shafe idanun shi, ya qara dubawa, ya so ya qi dagawa, sai ya ga message din ta ya shiga wayar shi,
'Yah Sultan na san komai, ka sanar da ni inda kuke, gamu nan zuwa'