← Book details A Garin Mu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 59 OF 93

Sashe 59

A Garin Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Dan Allah ka na bani tsoro, ka sanar da ni me ke hwaruwa, na ji na amince a kowanne yanayi, a kowanne hali, kuma ko kai wane ne zan zauna da kai,zan ci gaba da son ka,na maka alqawari, Sultana ba ta alqawari ta karya ka san da haka"

Hannun ta ya kama, ya zaunar da ita a saman cinyar shi, sannan ya ce,

"Ki shirya, akwai inda nake so na kai ki, ni ma na maki alqawalin duk abinda zan hwada maki ba zan hwadi qarya ba,na miki alqawalin ba zan riqe ki ki zauna da ni akan dole ba, daga lokacin da kin ka ce baki yin aure na, a lokacin zan sauw....."

Hawaye ne ke gudu a saman fuskar Sultana sosai, dan ta tabbata duk abinda za ta ji anan gaba ba mai dad'i bane, dan haka ba zata bari kalmar sauwakewa ko rabuwa ta hau saman labban shi ba, ta yarda da shi,ta san ba zai mata qarya ba.

"Ki shirya kayan ki a akwati, duk abinda ki ka son anhwani da shi naku na mata, ko akwati nawa zaki hada ki hada,daga nan zuwa dare, ko qarhe nawa zaki kai, kar ki damu,zan kai ki wani waje, nan gidan ba nawa ba ne, sultana ina so ki bar qungiyar ki hannun ma'aikatan ki, saboda tahiya ce za mu yi mai nisa"

Tsoro ya fara shigar ta ainun, amma abu daya ta sani,shi ne, ta yarda da shi, ta amince ba zai cutar da ita ba, cikin sanyin jiki ta tashi zata sauka daga jikin shi, ya kama hannun ta ta koma, fuskar ta ya qurawa ido, ya ga yanda take cikin damuwa da tsoro, a hankali ya ke share mata hawayen ta, ya na shafa bayan ta, irin yanda ake lallashin yaro in ana so ya bar kuka.

Bai barta ba, sai da ya tabbatar ta samu nutsuwa, sannan ya daga ta, ya raka ta har dakin,shi ma had'a kayan shi ya fara, ganin haka sai ita ma ta fara hada nata,su na yi su na hira sama sama.

Laptop din ta da wasu abubuwan ta hade waje guda,Lawwali ya kalle ta ya ce,

"Ki ajiye su a gefe, ga wasu can a can dakin na sawo maki, ki yi anhwani da su,ki maida komai naki cikin su, wadannan ki goge komai ki bar su nan"

Kallon shi ta yi kamar zata masa tambaya sai ta fasa, ta yi duk yanda ya ce.

Basu suka kammala duk abinda suke ba sai qarfe takwas da rabi na dare.

Suna gamawa Lawwali ya yi waya, sai ga qofar parlour ta bude, wasu zaratan matasa Sultana ta gani na shiga, sai da ta gudu bayan Lawwali ta buya, saboda tsoron da suka bata, janta ya yi jikin shi ya rungume ya na buga bayan ta, da alamar lallashi.

Sai da aka kwashe kayan nan tasss aka zuba a bus guda biyu, sannan Lawwali ya kama hannun Sultana da ke sanye da doguwar rigar ta, da mayafin kayan.

Su na fita ta ga motoci Bus uku, qarama guda daya.

Cikin qaramar suka shiga ita da Lawwali, da kan shi ya ke jan motar, sauran kuma yaran shi ne a ciki.

Sun wuce qofar gidan Gwamna Halliru sai ta ji kamar a tsaya ta ga mutanen gidan su, amma ba hali, ta na ji ta na gani suka wuce gidan iyayen ta, suka dauki babban titi.

Tun ta na gane unguwanni, da qauyukan da suke wuce wa, har ta dena gane wa,tsoro da tashin hankali sun fara shigar ta, ba dan itan ta na son abun duniya ba, ah ah tsoron irin qauye da rayuwar qauye da zata fara take, bayan bata taɓa yi ba.

Gani ta yi sun shiga daji ba gida gaba, ba gida baya, waje ne daji sosai , ta bude baki za ta yi magana, Lawwali ya dora yatsan shi a labban shi, shiru ta yi, ta na tsiyayar da hawaye.

Ina ne nan?
Me suke yi anan?
Wajen wa suka zo?
Shin a irin wannan dajin za su ci gaba da rayuwa?

Wadannan su ne tambayoyin da Sultana ke ta yi wa zuciyar ta,amsar ta bata samu ba sai da suka share awanni biyu da mintuna su na keta dajin, sannan ta hango wasu fitulu masu kama da na solar, dan kuwa a dajin nan zai wahala a samu wutar lantarki.

Kade kade ta dinga ji ya na tashi, da ganguna, ana waqoqi irin na kai amarya a qauye dinnan, bata san sanda murmushi ya kubuce mata ba,  a ran ta ta ayyana cewar,

'Ashe ma qauyan su ya kawo ni, duk na bi na damu,'

Sun tsaya a harabar wajen da ake ta kade kaden da raye raye, nan da nan murnar ta ta koma ciki, sakamakon ganin matasa mata da maza dauke da makamai, da bindigogi.

Cikin ta ne ya bada wata iriyar qara, sai da ta damqe shi ta ɗan duqa.

Lawwali ne ya d'aga hannayen shi sama ya na rawa,wajen kuwa aka dauki ihuuu, ana ci gaba da kid'a da waqa.

Sai da ya yi rawa sosai ya gaji, sannan ya kama hannun Sultana da ke tsaye a tsorace ya yi alamar a yi shiru, ko tari ba wanda ya sake yi a wajen kuwa, hakan ba qaramin sake firgita Sultana ya yi ba, ta kalle shi, ta ga ba alamar wasa a fuskar shi, sai dai wani kwarjini, da izza da ta gani kwance a fuskar shi.

"Ga amarya ta na kawo cikin mu, ina fatan za ku girmama ta, a mata duk wani abu da take so, kamar yanda za a yi min, sannan ina fatan za ku kiyaye dokoki na, dan mu zauna lahiya, ba cutaaaa???"

"Ba cutarwa, ba cin amana, ba karya alqawali"

"Da kyau, a ci gaba da shan shagali"

Kafin ya gama rufe bakin shi an dauki kade kade da raye raye, masu shaye shaye na yi, masu zinace zinace na jan abokan su suna barin wajen, kamilallun mutanen da aka kamo aka ajiye wanda suke da burin komawa gidajen su watarana na gefe, su na kallon masu rawa, a ranar zuqatan su sun taya Oga farin cikin kawo matar shi, domin ko ba komai, sun san ba ruwan shi da neman matan wajen, su na girmama yanayin yanda yake gudanar da wajen, ba yunwa, ba qishirwa, in baka so a kusance ka, ba mai maka dole wadan da aka wa dole ma a baya, yanzu sun wattsake, sun maida wajen kamar gida.

Babban abun takacin shi ne, ba ibada a wajen, duk da ba a hana mai so ya yi ba, amma fiye da rabin wajen basu damu da bautar Allah ba, basu damu da kiyaye duk wasu dokokin Allah ba, shaye shaye da zinace zinace sun yawaita.

(Ta yaya za a rabo ka da ga gidan iyayen ka, ko cikin iyalan ka a kai ka wata rayuwa mara 'yanci sannan ka dinga ganin an kyauta maka? Yau ko a wahale ka ke a rayuwa sace mutum ba abu ne mai kyau ba, Allah na sane da yanda ya aje dikkan bayin shi, dan haka sace mutane ko ta wacce fuska ce me kyau ko mara kyau ba daidai bane, Ya Ubangiji Allah, masu satar mutanen nan bayin ka ne suma da ka ke so, ka halicce su ka sanya su daga cikin halittu mad'aukaka, Allah ka basu ikon gane d'aukakar da ka yi musu su sauya rayuwar da suke kai zuwa wadda ka ke so Ameen)

************

Kayan su Lawwali an gama jere su a dakin su, akwatuna ne sun kai takwas, dakin babba ne, an qayata shi da kayan more rayuwa, sak dakin amarya, Lawwali duk ya ɗebe giya da duk wani kayan maye dake dakin, an maye gurbin wajen da lemuka manya irin masu tsadar nan,Sultana ta gaji da yin shiru, gaban shi ta tsaya, ta na hawaye, ta ce,

"Dan Allah ka warware min wannan qullin da ke cikin kai na da zuciya ta, kar ya matse ni na rasa raina "

"Ba zaki rasa ran ki ba Ran ki shi dade...auuu Sultana, taho nan ki zauna,abinda zan nuna maki, ba zaki iya kallon shi a tsaye ba"

Kwace hannun ta tayi, ta had'e su a qirjin ta, ta na jiran ya nuna mata duk ma me yake son nuna mata, ta gaji da yin shiru,

Murmushi ya yi, ya kwalawa No 5 Kira, ya shiga a guje, ya miqawa Lawwali wata baqar Laptop qirar Lenovo .

Ajiye ta ya yi, a saman wani dan table, ya kunna, ya shiga wani file, ya kunna wani video, nan da nan kuwa ya fara playing , abubuwan da Sultana ta fara gani, sun sanya mata jin jiri.

Jikin ta na rawa ta samu waje ta zube a qasa, ragwab a gaban laptop din, hannun ta ta sanya a bakin ta, ta na kuka, ta na jin wani irin sanyi na shigar ta,

Duk wasu kashe kashe da qone qonen garuruwan bayin Allah da akai, yau ta ga su waye ke yi, da kuma mutanen da ke sanya su yi din, duk wani tsafi, da fyaden yara qanana maza da mata, ta ga masu aikatawa, da masu kai musu yaran a aikata din, duk wani sabo da aka aikata da littafin Allah, ta ga wanda ya aikata dan kawai mulki, da son duniya.

Sultana kam qarshe numfashin ta ne ya dauke,ta zube a wajen.

Lawwali ya san za ayi haka, dan haka a shirye yake, yar locker da ke wajen, da yake ajiye ruwan gorar shi ya bude ya dauko, ya watsa mata, sannan ya dauke ta cakkk ya ajiye a saman gado,ya fita, dan ya bata waje, ta yi nazari akan abinda ta gani,ya san yanzu in ya yi magana ma ba zata fahimce shi ba, har sai ta dawo dadai .
Chapter 59 · 0% Book details