Sashe 14
A Garin Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da wani ne ya fadi haka ba Mubaraka ba, da ya d'and'ani azabar Lawwali, d'an had'iye bacin ran shi ya yi, ya ce,
"Baraka na ki min addu'a ke baiwar Allah ce, ba ki da laifuka a wajen Allah kamar Ni, ki roqe shi y sanya mata so na, kamar yanda nake son ta,....Baraka kin san matsalar da za a samu ma kuwa?"
Girgiza kai ta yi, zama ya yi a gefen ta, ya ce,
"A binciken da na yi kwanakin baya na gano cewa ba fa wani fita ma take sosai ba,sai ta bushi iska ne ta ce zata siyayya, to yau she zamu zanka haduwa?"
"Inshaa Allahu kar ka damu, ka riqe Allah, ka maida hankali Yah Auwal ka yi tuba na tsakani da Allah, Allah zai taimake ka"
"Amma baraka.."
"Yah Auwal kamar yanda ka yarda in ka loda harsashi a bindigar ka, ka harba ba abinda zai hana harsashin huda abinda ka harba, to amsa addu'ar Allah a wajen bawan shi da ya yi imani da shi, ya amince Allah ne me yi tafi harsashin bindigar ka"
"To baraka zan dage da roqon Allah"
"Yah Auwal ni na san rabon ka da sallah yanzu an jima, domin sallah na sanya fuskar mumini haske da kyalli, babu wannan a tare da kai, to ta ya ka ke ganin za ta gan ka ta ji ta kamu da son ka? A yanda na ji labari kai din masanin qur'ani ne kafin Lamishi ta kashe maka guiwa ka fara harkar nan, me zai sa ba za ka koma ma abinda ka bari ba?"
Shiru Lawwali ya yi, tunanin baya ya yi, a da kaf makarantar allon Malam Hadi ba ya shi, gashi yanzu ko a hanya in ya je unguwar ba ya gaishe da malam Hadi.
"Baraka dare na yi, muje Mu aje ki gida ko?"
Tashi ta yi, suka fita parlour, tunawa ya yi ko dan ruwa bai ba ta ba, leda ya samu ya cika mata da juices kala kala, da kayan marmari, da dangin biscuits, ya bawa No 1 ya riqe, suka fita .
Har gida suka aje ta za su koma, ta ce,
"Yah Auwal ba za ka sanar da su Baba ci gaban da aka samu ba?"
"Bassu kawai, kuddi kawai suke so ko? To ana kawo masu, ba su damu da me na ke ba, ke kad'ai ce ki ka damu da rayuwa ta, shi ya sa na bawa rayuwar ki mahimmanci kema"
Ya na gama fadi ya daga wa No 1 hannu, ya bashi umarni suka ja suka tafi.
Ta na shiga kuwa ta tadda masifar Lamishi na jiran ta,
"Sannu tinkiya, uwar tinbele, ke san gidan ku amma sai an nemo ki, ina ki ka tafi tun azzufur ba ki gidan ga sai yanzu zaki dawo?"
"Umma Yah Auwal ne fa ya dauken mun ka tai gidan da an ka sai mai, ya nuna min"
"Ga ki uwar shi ko? Shi yasa nake qara tsanar yarinyar nan fa, d'an nawa guda tilo kin zame mai kamar uwar shi, ni be kai Ni ba, se ke, bani nan"
Amshe ledar hannun Mubaraka ta yi, ta bubbude, ta ga lemuka da kayan marmari.
"Uhumm uwar kwad'ayi, wanga lemon wahala da ya had'o ki da shi fa? Ina lehin yar kaza ko balangu, ah ah, an hada mu da kayan ruwa mu sha mu yi ta hitsarin wahala ko?"
Dariya Jameelu ya kece da ita, dan shi a duniya fadan Lamishi na bashi dariya,
"Jameelu ka kiyaye ni, ina fada kana dariya zan yanka maka mari se kayi hitsarin wahala"
Haba me Jameelu zai yi ba dariya ba, a guje ya bar gidan, dan ta na iya yan ka masa marin wahalar da ta furta .
Juyawa ta yi kan Mubaraka ta ɗora daga inda ta tsaya ta ga wayam.
Ci gaba tai da masifa, ta na bude robar lemukan ta na kurba, ta na ware masu tsami a gefe, masu zaqin a gefe.
***********************
Mota ce madaidaiciya a qofar gidan Isa, driver na zaune ya na jira, Hansatu kuwa na ciki ta rikice, ta rasa ma kayan da za ta sanyawa yaran ta, kowanne ta dakko ya na da matsala ,ba ta san kayan yaran ta sun lalace ba haka sai yau, ita kan ta atampar da ke jikin ta ta ji jiki, wata baiwar Allah ce a nan layin nasu take bata tsofaffin kayan ta da na yaran ta, ita ta bata atampar ta kusan shekara biyu ta na dirzar ta.
Cire tunanin komai ta yi aran ta, ta saka masu jemammun kayan suka fita, kallon Isa ta yi, cike da mamaki, tun da Isan na da kaya masu kyau,amma ya saka wasu tsofaffin kayan shi sun kode kwarai, musamman ta saman bayan shi ,
"Kun shirya? Mu je mun bar bawan Allah na ta jira"
Kalaman shi ma na yau abun mamaki ne,
A gaban mota Isa ya zauna, Hansatu da yara suka shiga baya.
Driver tuqa mota ya yi, suka fara tafiya .
Yabbuga na zaune a qasan bishiyar su ita da matar Yahai, sun ga wucewar su Hansatu.
"Ke ji Isa wani kaya da ya saka"
Dariya suka kece da ita, Matar Yahai ta ce,
"Ina za su haka?"
"Jiya da dare na ji Isa na fadin sai sun je, ko ta na so ko bata so, ita ko ta na ta magiya akan kar su tai, tau qarshe sai da ya buga ke san jakki ba shi jin dumi sai bugu"(kin san jaki baya jin magana se an dake shi)
Dariya suka sake sanyawa, Dan jumma ne ya fita daga gida za shi masallaci, ran nan baqiqqirin, ya na gida ta fita zaman gulma, ko abinci da kan shi ya diba a tukunya, tsabar gulma na cin ta, ta gama girkin bata kwashe ba ta bari a tukunya, dik ya danqare.
"In kin gama dumin sai a tai zuwa sallah ko?"
Gaba ya yi bai jira ta cewar ta ba.
**********************
A gaban kantamemen gate din na gidan su Hansatu motar ta tsaya,wani irin kuka ne mai tuquqi ya tasowa Hansatu ,rabon ta da gidan tun wani zuwa da su Amina suka yi, ta je dakko su, lokacin Ahmad na qarami sosai,ba kalar wulaqancin da masu gadi ba su mata ba, saboda sabbi ne ba su san ta ba, kuma yayan ta da ya fita a wulaqance ya kora yaran, ko ciki ba a bari ta shiga ba.
"Ah ah hito mana"
Fita ta yi, ta na share hawaye, an sauya fentin gidan, gidan ya sauya kamar ba shi ba, kalle kalle ta fara, qofar shiga gidan ta kalla, hawaye ne suka zuba mata tunawa da mahaifin ta da ta yi.
A kunne ya rada mata,
"Ki na barin wannan iskancin ko sai na ci maki mutunci"
Da sauri ta hau goge idanun ta, yayan ta da ya fito kuwa a zaton shi wata kalma mai dadi aka fada mata, ta daina kuka.
Ciki suka shiga............
A GARIN MU
WRITTEN BY HAERMEEBRAEH
PAGE 15
Masha Allah, shi ne kawai abinda Musulmin kwarai zai ce in ya ga abinda ya masa kyau, ko ba mutum bane, ko da waje ne, ko tufafi, ko abun hawa, indai ya maka kyau ,to ka ce masha Allah, shi ne abinda Hansatu ta fadi a qasan ran ta, an gyara gidan su sosai ,ya yi kyau kamar ba shi ba.
Mahaifiyar ta na zaune a daya daga cikin kujeru na alfarma, ganin su Hansatu ne ya sanya ta miqewa tsaye, ta na murmishi, hannu ta bude mata, Hansatu kuwa ta na isa sai ta durqusa a qasa ta hau kuka, kuka ne da duk mai raunin zuciya ya kalla sai ya koka, mahaifiyar ta ma kan ta hawaye ta ke,
"Hajiya ku yafe min, na aikata babban kuskure akan so, na qi bin umarnin ku, Hajiya dan Allah ki yafe min, daga yanzu ba zan sake tsallake maganar ku ba"
"Hafsat ta shi kin ga yaran ki na kuka, tashi na yafe maku , da ke da mijin ki, qaddarar samun wadannan kyawawan yaran ne ta raba ki da mu, mun godewa Allah da ya sanya ta hanyar aure kuka same su, ba ta hanyar banza ba, mu ma muna da laifi, da mun hakura mun bi me kuke so da haka bata faru ba, da ace ke din baki samu kyakkyawar tarbiyya ba, da lalacewa zaki, tunda ki ka tafi ban qara yin lafiya ba, hawan jini ya kama Ni, saboda yawan tunani, amma alhamdu lilLAAH daga ranar da na je na gan ki, zuwa yanzu n fara samun lafiya a jiki na, dan haka daga yanzu ke da iyalin ki, ba mu yi muku shamaki da ko ina ba na gidan nan"
Isa ne ya zube guiwa bibbiyu ya na godiya, tare da matso kwallar dole,
"Hajiya mun gode da yafe mana da kuka yi, Allah ya qara girma da daukaka, Allah ya qara arziki, mun gode"
Murmushi Hajiya ta yi, Yayah'n Hansatu ne ya daga Isa daga durquson da ya yi, shi kuma ya na ta wani sunne kai, kamar na Allah, yaran shi na ta bin shi da kallon mamaki.
"Mun zama daya yanzu, ka daina godiyar nan haka"
Kwalawa matar shi kira ya yi, mai suna Aziza, ta kuwa taho cikin izza da mulki, kamar wata sarauniyar gaske, sai buda hanci take, ta na rufewa, ita a dole ga matar mai kuddi.
"Haba Baby wanga wane irin kira na? Me ne ne?"
"Qauna ta Hafsat da na ke fada maki? Ita ce ta zo,"
Wani kallo ta bi Hansatu da shi daga sama har qasa, tabbas ga kamanni nan, amma wannan wacce irin shiga ce a jikin ta? "
"Wagga d'in ita ce qaunar ka?"
"Eh ita ce, tai ki sa a kawo masu abincii da an ka tanada domin su"
"Ni fa na mance ban ce a yi wani abinci na musamman ba, amma dai an yi na dare, a wajen su kuwa na san zai zama kamar na ranar sallah, ina zuwa"
"Baraka na ki min addu'a ke baiwar Allah ce, ba ki da laifuka a wajen Allah kamar Ni, ki roqe shi y sanya mata so na, kamar yanda nake son ta,....Baraka kin san matsalar da za a samu ma kuwa?"
Girgiza kai ta yi, zama ya yi a gefen ta, ya ce,
"A binciken da na yi kwanakin baya na gano cewa ba fa wani fita ma take sosai ba,sai ta bushi iska ne ta ce zata siyayya, to yau she zamu zanka haduwa?"
"Inshaa Allahu kar ka damu, ka riqe Allah, ka maida hankali Yah Auwal ka yi tuba na tsakani da Allah, Allah zai taimake ka"
"Amma baraka.."
"Yah Auwal kamar yanda ka yarda in ka loda harsashi a bindigar ka, ka harba ba abinda zai hana harsashin huda abinda ka harba, to amsa addu'ar Allah a wajen bawan shi da ya yi imani da shi, ya amince Allah ne me yi tafi harsashin bindigar ka"
"To baraka zan dage da roqon Allah"
"Yah Auwal ni na san rabon ka da sallah yanzu an jima, domin sallah na sanya fuskar mumini haske da kyalli, babu wannan a tare da kai, to ta ya ka ke ganin za ta gan ka ta ji ta kamu da son ka? A yanda na ji labari kai din masanin qur'ani ne kafin Lamishi ta kashe maka guiwa ka fara harkar nan, me zai sa ba za ka koma ma abinda ka bari ba?"
Shiru Lawwali ya yi, tunanin baya ya yi, a da kaf makarantar allon Malam Hadi ba ya shi, gashi yanzu ko a hanya in ya je unguwar ba ya gaishe da malam Hadi.
"Baraka dare na yi, muje Mu aje ki gida ko?"
Tashi ta yi, suka fita parlour, tunawa ya yi ko dan ruwa bai ba ta ba, leda ya samu ya cika mata da juices kala kala, da kayan marmari, da dangin biscuits, ya bawa No 1 ya riqe, suka fita .
Har gida suka aje ta za su koma, ta ce,
"Yah Auwal ba za ka sanar da su Baba ci gaban da aka samu ba?"
"Bassu kawai, kuddi kawai suke so ko? To ana kawo masu, ba su damu da me na ke ba, ke kad'ai ce ki ka damu da rayuwa ta, shi ya sa na bawa rayuwar ki mahimmanci kema"
Ya na gama fadi ya daga wa No 1 hannu, ya bashi umarni suka ja suka tafi.
Ta na shiga kuwa ta tadda masifar Lamishi na jiran ta,
"Sannu tinkiya, uwar tinbele, ke san gidan ku amma sai an nemo ki, ina ki ka tafi tun azzufur ba ki gidan ga sai yanzu zaki dawo?"
"Umma Yah Auwal ne fa ya dauken mun ka tai gidan da an ka sai mai, ya nuna min"
"Ga ki uwar shi ko? Shi yasa nake qara tsanar yarinyar nan fa, d'an nawa guda tilo kin zame mai kamar uwar shi, ni be kai Ni ba, se ke, bani nan"
Amshe ledar hannun Mubaraka ta yi, ta bubbude, ta ga lemuka da kayan marmari.
"Uhumm uwar kwad'ayi, wanga lemon wahala da ya had'o ki da shi fa? Ina lehin yar kaza ko balangu, ah ah, an hada mu da kayan ruwa mu sha mu yi ta hitsarin wahala ko?"
Dariya Jameelu ya kece da ita, dan shi a duniya fadan Lamishi na bashi dariya,
"Jameelu ka kiyaye ni, ina fada kana dariya zan yanka maka mari se kayi hitsarin wahala"
Haba me Jameelu zai yi ba dariya ba, a guje ya bar gidan, dan ta na iya yan ka masa marin wahalar da ta furta .
Juyawa ta yi kan Mubaraka ta ɗora daga inda ta tsaya ta ga wayam.
Ci gaba tai da masifa, ta na bude robar lemukan ta na kurba, ta na ware masu tsami a gefe, masu zaqin a gefe.
***********************
Mota ce madaidaiciya a qofar gidan Isa, driver na zaune ya na jira, Hansatu kuwa na ciki ta rikice, ta rasa ma kayan da za ta sanyawa yaran ta, kowanne ta dakko ya na da matsala ,ba ta san kayan yaran ta sun lalace ba haka sai yau, ita kan ta atampar da ke jikin ta ta ji jiki, wata baiwar Allah ce a nan layin nasu take bata tsofaffin kayan ta da na yaran ta, ita ta bata atampar ta kusan shekara biyu ta na dirzar ta.
Cire tunanin komai ta yi aran ta, ta saka masu jemammun kayan suka fita, kallon Isa ta yi, cike da mamaki, tun da Isan na da kaya masu kyau,amma ya saka wasu tsofaffin kayan shi sun kode kwarai, musamman ta saman bayan shi ,
"Kun shirya? Mu je mun bar bawan Allah na ta jira"
Kalaman shi ma na yau abun mamaki ne,
A gaban mota Isa ya zauna, Hansatu da yara suka shiga baya.
Driver tuqa mota ya yi, suka fara tafiya .
Yabbuga na zaune a qasan bishiyar su ita da matar Yahai, sun ga wucewar su Hansatu.
"Ke ji Isa wani kaya da ya saka"
Dariya suka kece da ita, Matar Yahai ta ce,
"Ina za su haka?"
"Jiya da dare na ji Isa na fadin sai sun je, ko ta na so ko bata so, ita ko ta na ta magiya akan kar su tai, tau qarshe sai da ya buga ke san jakki ba shi jin dumi sai bugu"(kin san jaki baya jin magana se an dake shi)
Dariya suka sake sanyawa, Dan jumma ne ya fita daga gida za shi masallaci, ran nan baqiqqirin, ya na gida ta fita zaman gulma, ko abinci da kan shi ya diba a tukunya, tsabar gulma na cin ta, ta gama girkin bata kwashe ba ta bari a tukunya, dik ya danqare.
"In kin gama dumin sai a tai zuwa sallah ko?"
Gaba ya yi bai jira ta cewar ta ba.
**********************
A gaban kantamemen gate din na gidan su Hansatu motar ta tsaya,wani irin kuka ne mai tuquqi ya tasowa Hansatu ,rabon ta da gidan tun wani zuwa da su Amina suka yi, ta je dakko su, lokacin Ahmad na qarami sosai,ba kalar wulaqancin da masu gadi ba su mata ba, saboda sabbi ne ba su san ta ba, kuma yayan ta da ya fita a wulaqance ya kora yaran, ko ciki ba a bari ta shiga ba.
"Ah ah hito mana"
Fita ta yi, ta na share hawaye, an sauya fentin gidan, gidan ya sauya kamar ba shi ba, kalle kalle ta fara, qofar shiga gidan ta kalla, hawaye ne suka zuba mata tunawa da mahaifin ta da ta yi.
A kunne ya rada mata,
"Ki na barin wannan iskancin ko sai na ci maki mutunci"
Da sauri ta hau goge idanun ta, yayan ta da ya fito kuwa a zaton shi wata kalma mai dadi aka fada mata, ta daina kuka.
Ciki suka shiga............
A GARIN MU
WRITTEN BY HAERMEEBRAEH
PAGE 15
Masha Allah, shi ne kawai abinda Musulmin kwarai zai ce in ya ga abinda ya masa kyau, ko ba mutum bane, ko da waje ne, ko tufafi, ko abun hawa, indai ya maka kyau ,to ka ce masha Allah, shi ne abinda Hansatu ta fadi a qasan ran ta, an gyara gidan su sosai ,ya yi kyau kamar ba shi ba.
Mahaifiyar ta na zaune a daya daga cikin kujeru na alfarma, ganin su Hansatu ne ya sanya ta miqewa tsaye, ta na murmishi, hannu ta bude mata, Hansatu kuwa ta na isa sai ta durqusa a qasa ta hau kuka, kuka ne da duk mai raunin zuciya ya kalla sai ya koka, mahaifiyar ta ma kan ta hawaye ta ke,
"Hajiya ku yafe min, na aikata babban kuskure akan so, na qi bin umarnin ku, Hajiya dan Allah ki yafe min, daga yanzu ba zan sake tsallake maganar ku ba"
"Hafsat ta shi kin ga yaran ki na kuka, tashi na yafe maku , da ke da mijin ki, qaddarar samun wadannan kyawawan yaran ne ta raba ki da mu, mun godewa Allah da ya sanya ta hanyar aure kuka same su, ba ta hanyar banza ba, mu ma muna da laifi, da mun hakura mun bi me kuke so da haka bata faru ba, da ace ke din baki samu kyakkyawar tarbiyya ba, da lalacewa zaki, tunda ki ka tafi ban qara yin lafiya ba, hawan jini ya kama Ni, saboda yawan tunani, amma alhamdu lilLAAH daga ranar da na je na gan ki, zuwa yanzu n fara samun lafiya a jiki na, dan haka daga yanzu ke da iyalin ki, ba mu yi muku shamaki da ko ina ba na gidan nan"
Isa ne ya zube guiwa bibbiyu ya na godiya, tare da matso kwallar dole,
"Hajiya mun gode da yafe mana da kuka yi, Allah ya qara girma da daukaka, Allah ya qara arziki, mun gode"
Murmushi Hajiya ta yi, Yayah'n Hansatu ne ya daga Isa daga durquson da ya yi, shi kuma ya na ta wani sunne kai, kamar na Allah, yaran shi na ta bin shi da kallon mamaki.
"Mun zama daya yanzu, ka daina godiyar nan haka"
Kwalawa matar shi kira ya yi, mai suna Aziza, ta kuwa taho cikin izza da mulki, kamar wata sarauniyar gaske, sai buda hanci take, ta na rufewa, ita a dole ga matar mai kuddi.
"Haba Baby wanga wane irin kira na? Me ne ne?"
"Qauna ta Hafsat da na ke fada maki? Ita ce ta zo,"
Wani kallo ta bi Hansatu da shi daga sama har qasa, tabbas ga kamanni nan, amma wannan wacce irin shiga ce a jikin ta? "
"Wagga d'in ita ce qaunar ka?"
"Eh ita ce, tai ki sa a kawo masu abincii da an ka tanada domin su"
"Ni fa na mance ban ce a yi wani abinci na musamman ba, amma dai an yi na dare, a wajen su kuwa na san zai zama kamar na ranar sallah, ina zuwa"