Sashe 41
A Garin Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Shin da gaske yake iyayen ta ba za su bari ya aure ta ba? Me ye dalili? A duniya mutum na iya auren duk wanda yake so, se wanda musulunci ya hana, misali mace ta auri mace, ko namiji ya auri namiji, ko mutum ya auri wata dabba ko wata halitta, ko musulmi ya auri kafuri,ko muharramai su auri junan su, amma Indai akwai so da qauna kowanne namiji zai iya auren macen da yake so, haka ma mace za ta iya auren namijin da take so, to me ya sa ita zata zama daban a cikin mutane? Saboda kawai shi din driver ne?
Da wannan tunanin bacci mai cike da rudanin tunani ya dauke ta.
*************************
Duk abinda aka sanyawa rana, wannan ranar zata zagayo, ko ayi abun, ko kuma a fasa shi .
Yau ce ranar zabe, gwamna da iyalin shi tun asuba suka shirya suka je wajen yin zaɓe, sun dangwala nasu sun koma government house, yau har da sultana aka tafi, ta na can ne kawai, amma hankalin ta baya tare da ita, rashin ganin Auwal na damun ta, tun randa suka yi waya, yau kwana hudu, ta ji shi shiru, shin ko dai ya rabu da ita ne saboda tunanin Hajiya ba zata yarda ba, daddy ma ba zai amince ba? Amma ai bai ce zai rabu da ita ba.
Wannan tunanin sun ma ƙwaƙwalwar ta yawa, har ya fara sanya ta zance a fili, cikin rashin fahimtar me ta fada Sultan ya ce,
"Mi kin ka ce? Wa ye zai bar ki?"
Da sauri ta hau yaqe ta na barin wajen, tare da sanar da shi ,
"Ba kowa, ba komai, kar ka damu, ina zuwa"
Tafiya kawai take a tankamemen gidan da ya cika da mutane kala kala, duk ta gama ratsa su ta wuce wani building, ba abinda ke tashi a hanyar wajen se karar takalmin ta, wayar ta ta tsaya cak ta na latsawa, sama sama ta ke jin muryoyin su,
"......ka tabbata dai ka saka a kawo takardun zaben da aka dangwala ko? Na hwadi maka in banda aikin da Sultana ka yi a gari, sai d'an wanda munka hwara shekarar ga, walle ba mai zabar mu,"
"Ki kwantar da hankalin ki Hajiya, na gama komai, akwai taqadarin yaro na da ka yi min aiki ko wanne iri na, shi da yara nai, ke ko batar da mutum nicce ayi, ba shi koma second d'aya raye indai yaron nan na saka, ke duk wasu abubuwa da ki kaga ina yi da shi ni ka taqama, dan haka zabe kamar na ci na gama ne,"
Wata iriyar dariya suka sanya a tare, suka ci gaba da hira, Gwamna na bawa Hajiya Ikee labarin Lawwali, ba tare da ya sanar da ita sunan shi ba, sai jin dad'i take ta na addu'a Allah ya sa su zarce.
Qoqarin komawa cikin mutane suke, cikin sauri Sultana da ta daskare a wajen ta cire takalmin ta a hannu, ta fad'a wata qofa da ta gani a dan bude ta b'uya, Hajiya Ikee ce da Gwamna Halliru suka fito, cikin farin ciki, sun sha ado na alfarma, sai walqiya suke, da qamshi.
Su na wuce wa sultana ta sanya wani irin kuka mai ban tausayi, mahaifan ta ashe basu da imani? Kuma a haka suke neman su ci gaba da jagorantar al'umma?...........
*Ni Ko nace iya abinda ki ka sani ma kenan 'yannan, ba ki san kalar tsafin da gyatumi ke yi ba*
💅🏻 *A GARIN MU* 💅🏻
BY HAERMEEBRAERH
PAGE 33:
Lokuta da dama idan farin ciki, ko baqin ciki ya dami mutum, akwai mutum na farko dake zuwa zuciyar wannan mutumin, walau wanda ya yarda da shi ko da ba 'yan uwantaka ta jini a tsakanin su,ko kuma wanda ke da alhaki akan halin da mutum ya shiga, masoyi shine mutum na farko da ke fara zuwar wa mutum a rai, mace ko namiji, qawa ko saurayi, miji ko mata, ko kuma iyaye.
A baya Sultana ba ta da wanda ya wuce Sultan a wajen ta, saboda shaquwa irin ta yaya da qanwa da ke a tsakanin su, komai nata shi take sanarwa, to amma tunda shi Allah bai sa har yanzu ya gano asalin mummunanan dabi'un mahaifan nasu ba, ba ta so ya sani, kamar yanda suka so ya yi rayuwa haka yake yi, ba ya saba umarnin su, ya kai a ce ya ajiye iyali, amma rayuwar shi abar juyawa ce a hannayen su, gwanda ita sun bata 'yanci, wanda a wajen ta ba 'yanci bane, sun yi amfani da abinda suke kira 'yancin su na biyan buqatar su ta son zuciya da shi.
Lawwali ne babban wanda za ta iya wannan maganar sirrin da shi, (to wai ma makaranta mu dan tattauna wani abu mana, shin daidai ne kawai daga yin saurayi, dan ki na jin kin yarda dashi, dari bisa dari, sai ki ta fada masa sirrin ki? Musamman wannan babban sirrin? 'yan mata da dama su na shirme, da yarinta, kawai yanda ke ki ke jin ki na son namiji, To haka ki ke dauka shima haka yake son ki, kuma yanda kk yarda da shi shima haka ya yarda da ke, wallahi ba haka bane, maza kala kala ne,kashi kashi ne,akwai wanda zai so ki kamar ran shi, amma ba sirri, nashi sirrin ma be riqe ba balle na wani, kuma zai iya rufe ido ya manta da son da yake maki, ya kafta maki uba uban rashin mutunci, daga baya in kun shirya ya baki hakuri, ke kuma ya wuce, anjima ma in wani abu ya taso se kin fada masa. Akwai namijin da zai so ki, kuma zai saurare ki, zai taya ki warware matsalar ki da damuwar ki,zai shiga lamarin ki kamar nashi, kuma ze riqe miki sirrin ki,amma ki sani 'yar uwa irin su basu da yawa a wannan zamanin, wani ma Allah Allah yake yaji maganar ki ya fadawa yan uwan shi da abokan shi, ki na nan tanyare bude a faranti kowa ya san sirrin ki da na 'yan gidan ku, a kiyaye, a dena makahon so)
Wayar shi take ta nema, ana fada mata busy, cikin bacin rai, da sharar hawaye ta bar taron, iyayen nata basu son video ko camera su hau kan ta, ganin yanayin da take ciki, dan haka suka basar sukai ta harkokin su, direct motar ta ta nufa,ta na qoqarin shiga, wani murdadden namiji da baqaqen kaya, da baqin gilashi ya tsaya a gefen ta ya ce,
"Ran ki shi dade, Excellency ya ce kar a bar ki ki hita yanzu,sai an fadi sakamakon zabe gari ya lafa,sannan za ku fita,yanzu ki tai zuwa sashen ku,"
"Saqo ka ke bani ko umarni?"
"Ran ki shi dade, ba umarni bane, dan Allah ki taimake mu ki koma, abincin mu na nan, ke mai tausayi ce, kar ki fita ya zama sanadin barin mu aiki"
Kallon shi tayi, ta gan shi rusheshe, ko a ka aka ce ya maida ta sashen, cikin qiftawar ido ya na iyawa, amma ya gwammaci ya yi amfani da kalamai masu taushi a gare ta, cike da baqin cikin ci gaba da zama a gidan Gwamnatin ta shiga gaba, ya na take mata baya, har bangaren su, ta na shiga ta rufe da qarfi ta saki wani irin kuka, mai matuqar kuna.
"Anya su Daddy za su hadu da rahamar Allah kuwa? Ashe duk abinda Daddy ke aikatawa, Hajiya ta yi kamar bata sani ba ita ka zuga shi aikata wasu munanan aikin? Anya iyayen ga namu su na da imani kuwa? Sun san Allah kuwa?"
Kuka take ta na surutai ita kadai,ga wayar Lawwali ta qi samuwa, se gwadawa take.
Har aka yi azahar ta yi itama, ta kwanta Lawwali bai kira taba, ta fara hasala yanzu kam, amma ba yanda zata yi, gashi ba zata iya fushi da shi ba, saboda kalar son da take masa ma, ba zai bata damar fushi da shi ba.
Wayar ta ta sake laluba, ta shiga wajen rubuta saqo,ta hau rubutu kamar haka.
~Auwal dan Allah ka dauki kira na, zan iya rasa raina in har ban ji Muryar ka ba a yau, kai ne maganin quncin da zuciya ta ke ciki,kai ne farin ciki na,kasancewar ka tare da ni, shi ne cikar farin ciki na, pls ka kira ni, in ka ga saqo na, Ina son ka Auwal, and I really need u now, pls~
Abinci aka shigar mata da shi, ko daga kai ta kalla ma bata yi ba, ballantana su sanya ran za ta ci, duk magiya da roqo da mai aikin ta dinga yi, qarshe itama magiya da roqo, tare da kuka ta sanya wa matar, dole ta hakura ta barta.
Ita kadai ta san ya zuciyar ta take a yanzu, wani irin qunci da ciwo take mata, wace iriyar rayuwa take ciki? Ai da wannan azziqin gwanda talaucin da ba ze raba ka da imanin ka ba, akwai abubuwa da dama da suke zamewa bawa musiba, to ta tabbata wannan azziqin musiba ne a gare su, sai dai za ta yi ta addu'a Allah ya kare su daga fadawa halaka, duniya da lahira.
Abu kamar wasa, Lawwali bai kira Sultana ba, dik da cewa ya ga kiran ta, ya ga saqon ta, aiki ne ya mishi yawa, ga wajen da suke ba network sosai, yau kuwa tun cikin dare suka fita, suna ta kai takardun da aka riga aka dangwala wa yatsan zabe, mazabu kala kala.
A gajiye yake matuqa, ko ya kira ta be san me zai ce ba, ya san dole ta fuskanci gajiyar a Muryar shi, ba shi da abin kare kan shi, dan haka ya qi kiran ta, ya ci gaba da harkokin shi.
Wani sashe na zuciyar shi ya na jin ba dad'i , da bai kira ba, tunda ya san kalar yanda take son shi, ko Muryar shi taji ta na jin dadi a ran ta, kawar da tunanin ya yi, a fili ya furta,
"Gwanda ta ji zafin rashin kiran nawa ma ai, hakan ma wani punishment ne"
Da wannan tunanin bacci mai cike da rudanin tunani ya dauke ta.
*************************
Duk abinda aka sanyawa rana, wannan ranar zata zagayo, ko ayi abun, ko kuma a fasa shi .
Yau ce ranar zabe, gwamna da iyalin shi tun asuba suka shirya suka je wajen yin zaɓe, sun dangwala nasu sun koma government house, yau har da sultana aka tafi, ta na can ne kawai, amma hankalin ta baya tare da ita, rashin ganin Auwal na damun ta, tun randa suka yi waya, yau kwana hudu, ta ji shi shiru, shin ko dai ya rabu da ita ne saboda tunanin Hajiya ba zata yarda ba, daddy ma ba zai amince ba? Amma ai bai ce zai rabu da ita ba.
Wannan tunanin sun ma ƙwaƙwalwar ta yawa, har ya fara sanya ta zance a fili, cikin rashin fahimtar me ta fada Sultan ya ce,
"Mi kin ka ce? Wa ye zai bar ki?"
Da sauri ta hau yaqe ta na barin wajen, tare da sanar da shi ,
"Ba kowa, ba komai, kar ka damu, ina zuwa"
Tafiya kawai take a tankamemen gidan da ya cika da mutane kala kala, duk ta gama ratsa su ta wuce wani building, ba abinda ke tashi a hanyar wajen se karar takalmin ta, wayar ta ta tsaya cak ta na latsawa, sama sama ta ke jin muryoyin su,
"......ka tabbata dai ka saka a kawo takardun zaben da aka dangwala ko? Na hwadi maka in banda aikin da Sultana ka yi a gari, sai d'an wanda munka hwara shekarar ga, walle ba mai zabar mu,"
"Ki kwantar da hankalin ki Hajiya, na gama komai, akwai taqadarin yaro na da ka yi min aiki ko wanne iri na, shi da yara nai, ke ko batar da mutum nicce ayi, ba shi koma second d'aya raye indai yaron nan na saka, ke duk wasu abubuwa da ki kaga ina yi da shi ni ka taqama, dan haka zabe kamar na ci na gama ne,"
Wata iriyar dariya suka sanya a tare, suka ci gaba da hira, Gwamna na bawa Hajiya Ikee labarin Lawwali, ba tare da ya sanar da ita sunan shi ba, sai jin dad'i take ta na addu'a Allah ya sa su zarce.
Qoqarin komawa cikin mutane suke, cikin sauri Sultana da ta daskare a wajen ta cire takalmin ta a hannu, ta fad'a wata qofa da ta gani a dan bude ta b'uya, Hajiya Ikee ce da Gwamna Halliru suka fito, cikin farin ciki, sun sha ado na alfarma, sai walqiya suke, da qamshi.
Su na wuce wa sultana ta sanya wani irin kuka mai ban tausayi, mahaifan ta ashe basu da imani? Kuma a haka suke neman su ci gaba da jagorantar al'umma?...........
*Ni Ko nace iya abinda ki ka sani ma kenan 'yannan, ba ki san kalar tsafin da gyatumi ke yi ba*
💅🏻 *A GARIN MU* 💅🏻
BY HAERMEEBRAERH
PAGE 33:
Lokuta da dama idan farin ciki, ko baqin ciki ya dami mutum, akwai mutum na farko dake zuwa zuciyar wannan mutumin, walau wanda ya yarda da shi ko da ba 'yan uwantaka ta jini a tsakanin su,ko kuma wanda ke da alhaki akan halin da mutum ya shiga, masoyi shine mutum na farko da ke fara zuwar wa mutum a rai, mace ko namiji, qawa ko saurayi, miji ko mata, ko kuma iyaye.
A baya Sultana ba ta da wanda ya wuce Sultan a wajen ta, saboda shaquwa irin ta yaya da qanwa da ke a tsakanin su, komai nata shi take sanarwa, to amma tunda shi Allah bai sa har yanzu ya gano asalin mummunanan dabi'un mahaifan nasu ba, ba ta so ya sani, kamar yanda suka so ya yi rayuwa haka yake yi, ba ya saba umarnin su, ya kai a ce ya ajiye iyali, amma rayuwar shi abar juyawa ce a hannayen su, gwanda ita sun bata 'yanci, wanda a wajen ta ba 'yanci bane, sun yi amfani da abinda suke kira 'yancin su na biyan buqatar su ta son zuciya da shi.
Lawwali ne babban wanda za ta iya wannan maganar sirrin da shi, (to wai ma makaranta mu dan tattauna wani abu mana, shin daidai ne kawai daga yin saurayi, dan ki na jin kin yarda dashi, dari bisa dari, sai ki ta fada masa sirrin ki? Musamman wannan babban sirrin? 'yan mata da dama su na shirme, da yarinta, kawai yanda ke ki ke jin ki na son namiji, To haka ki ke dauka shima haka yake son ki, kuma yanda kk yarda da shi shima haka ya yarda da ke, wallahi ba haka bane, maza kala kala ne,kashi kashi ne,akwai wanda zai so ki kamar ran shi, amma ba sirri, nashi sirrin ma be riqe ba balle na wani, kuma zai iya rufe ido ya manta da son da yake maki, ya kafta maki uba uban rashin mutunci, daga baya in kun shirya ya baki hakuri, ke kuma ya wuce, anjima ma in wani abu ya taso se kin fada masa. Akwai namijin da zai so ki, kuma zai saurare ki, zai taya ki warware matsalar ki da damuwar ki,zai shiga lamarin ki kamar nashi, kuma ze riqe miki sirrin ki,amma ki sani 'yar uwa irin su basu da yawa a wannan zamanin, wani ma Allah Allah yake yaji maganar ki ya fadawa yan uwan shi da abokan shi, ki na nan tanyare bude a faranti kowa ya san sirrin ki da na 'yan gidan ku, a kiyaye, a dena makahon so)
Wayar shi take ta nema, ana fada mata busy, cikin bacin rai, da sharar hawaye ta bar taron, iyayen nata basu son video ko camera su hau kan ta, ganin yanayin da take ciki, dan haka suka basar sukai ta harkokin su, direct motar ta ta nufa,ta na qoqarin shiga, wani murdadden namiji da baqaqen kaya, da baqin gilashi ya tsaya a gefen ta ya ce,
"Ran ki shi dade, Excellency ya ce kar a bar ki ki hita yanzu,sai an fadi sakamakon zabe gari ya lafa,sannan za ku fita,yanzu ki tai zuwa sashen ku,"
"Saqo ka ke bani ko umarni?"
"Ran ki shi dade, ba umarni bane, dan Allah ki taimake mu ki koma, abincin mu na nan, ke mai tausayi ce, kar ki fita ya zama sanadin barin mu aiki"
Kallon shi tayi, ta gan shi rusheshe, ko a ka aka ce ya maida ta sashen, cikin qiftawar ido ya na iyawa, amma ya gwammaci ya yi amfani da kalamai masu taushi a gare ta, cike da baqin cikin ci gaba da zama a gidan Gwamnatin ta shiga gaba, ya na take mata baya, har bangaren su, ta na shiga ta rufe da qarfi ta saki wani irin kuka, mai matuqar kuna.
"Anya su Daddy za su hadu da rahamar Allah kuwa? Ashe duk abinda Daddy ke aikatawa, Hajiya ta yi kamar bata sani ba ita ka zuga shi aikata wasu munanan aikin? Anya iyayen ga namu su na da imani kuwa? Sun san Allah kuwa?"
Kuka take ta na surutai ita kadai,ga wayar Lawwali ta qi samuwa, se gwadawa take.
Har aka yi azahar ta yi itama, ta kwanta Lawwali bai kira taba, ta fara hasala yanzu kam, amma ba yanda zata yi, gashi ba zata iya fushi da shi ba, saboda kalar son da take masa ma, ba zai bata damar fushi da shi ba.
Wayar ta ta sake laluba, ta shiga wajen rubuta saqo,ta hau rubutu kamar haka.
~Auwal dan Allah ka dauki kira na, zan iya rasa raina in har ban ji Muryar ka ba a yau, kai ne maganin quncin da zuciya ta ke ciki,kai ne farin ciki na,kasancewar ka tare da ni, shi ne cikar farin ciki na, pls ka kira ni, in ka ga saqo na, Ina son ka Auwal, and I really need u now, pls~
Abinci aka shigar mata da shi, ko daga kai ta kalla ma bata yi ba, ballantana su sanya ran za ta ci, duk magiya da roqo da mai aikin ta dinga yi, qarshe itama magiya da roqo, tare da kuka ta sanya wa matar, dole ta hakura ta barta.
Ita kadai ta san ya zuciyar ta take a yanzu, wani irin qunci da ciwo take mata, wace iriyar rayuwa take ciki? Ai da wannan azziqin gwanda talaucin da ba ze raba ka da imanin ka ba, akwai abubuwa da dama da suke zamewa bawa musiba, to ta tabbata wannan azziqin musiba ne a gare su, sai dai za ta yi ta addu'a Allah ya kare su daga fadawa halaka, duniya da lahira.
Abu kamar wasa, Lawwali bai kira Sultana ba, dik da cewa ya ga kiran ta, ya ga saqon ta, aiki ne ya mishi yawa, ga wajen da suke ba network sosai, yau kuwa tun cikin dare suka fita, suna ta kai takardun da aka riga aka dangwala wa yatsan zabe, mazabu kala kala.
A gajiye yake matuqa, ko ya kira ta be san me zai ce ba, ya san dole ta fuskanci gajiyar a Muryar shi, ba shi da abin kare kan shi, dan haka ya qi kiran ta, ya ci gaba da harkokin shi.
Wani sashe na zuciyar shi ya na jin ba dad'i , da bai kira ba, tunda ya san kalar yanda take son shi, ko Muryar shi taji ta na jin dadi a ran ta, kawar da tunanin ya yi, a fili ya furta,
"Gwanda ta ji zafin rashin kiran nawa ma ai, hakan ma wani punishment ne"