Sashe 67
A Garin Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Murmushi kawai Isah ke zubawa, cikin sunkuyar da kai ya ce,
"Hajiya ai ni ke da godiya, ba abinda zan ce da Hansatu sai Allah ya mata albarka, Allah kuma ya haɗa ta da dukkan alkhairi duniya da lahira"
Farin cikin da Hajiya ta shiga ba mai faduwa bane,kowacce uwa zata so jin wadannan kalaman a bakin surukin ta, to gashi ita Allah ya jiyar da ita, tun da sauran rayuwar ta.
"Ban ga Yaya ba, ko dai ba shi nan na?"
"Eh shi na office, ai sai yamma zai dawo, wan mata tai yak-kirai tun sahe akwai abinda suke yi"
"Allah Sarki, Allah ya bada sa'a, Allah ya jiqan Alhaji, har na tuna sanda muke tafiya, tun sahe sai dare, ba ya bari na da yunwa, komi yaci shi zai ban, haka zai wuni aiki, rayuwa kenan"
Hira ce sosai ta shaquwa da sabo ke gudana tsakanin Isah da surukar shi, tun sanda ya bar gida nan ya nufa, ya ke ta Suratu, hankalin shi gaba daya ya tattara ya koma gida wajen Hansatu, amma ya fi so sai ta huce ya koma, dan ya san ba ta iya fushi da shi, kamar daga sama ya ji maganar Hajiya ta ce,
"Ai shawarar da kabban ita na bi, ana nan ana binciken mutanen da sun ka yi kidnapping di na, kuma da alama ana nan ana samun nasara, dan har jami'an tsaro sun Kama yaro guda da an ka had'a baki da shi an ka swace ni"
Wani irin tari Isah yake sakamakon kwarewa da ya yi da lemon da ya daga glass cup ya na korawa, sannu Hajiya ta dinga zuba masa, miqewa ya yi, cikin yaqe, ya ce,
"Allah dai shi tona ma koma waye asiri, bari na tai na ga ta na ta yi min flashing, wataqila suna bidar wani abu"
Murmushi Hajiya ta yi, ta ce ya jira ta kawo masa saqo ya kai mata, ji ya yi kamar ya gudu kan ta dawo, kuka ne kawai Isah be ba, saboda jimawar da Hajiya ta yi.
Kwalin madarar ruwa ta kai masa da galan din zuma, ta ce ya kai ma Hanstu, godiya ya dinga yi, ya na sauri ya bar gidan, mai gadi na gaida shi ko kula shi be ba, da da ne kuwa sai ya tsaya ya masa kurin shi surukin gidan ne.
Ya na fita titi sosai ya lalubi No Laminu, bai dauka ba, ji ya yi kamar ya fashe da kuka dan takaici, in asirin shi ya tonu ai ya kade.
Bari ma, saudiyar nan zai koma zaman Nija be kama shi ba........
*Yayah Isah namu na mudunci😂*
💅🏻 *A GARIN MU* 💅🏻
BY HAERMEEBRAERH
PAGE 50:
A cikin daren Isah ya je gidan Laminu, Asshibi na ta mitar an hana su sakewa da mijin ta, ya fita tun safe, sai daren ya dawo, hakuri Laminu ya bata ya sanya rigar shi ya bude gate ya fita, Isah ya gani tsaye cikin tsananin damuwa, da tashin hankali, murmushi ya yi, ya ce wa Isah,
"Na san me ya kawo ka, kwantar da hankalin ka, magana ta qare dazu da rana, na aika wani yaro da maganin kusa (bera) an sa mishi ga abincin da an ka kai, ya ci ya mutu, sai in ga me bada shaida"
Wata iriyar ajiyar zuciya Isah ya sauke, tare da sakin kwalin madarar a qasa, ya rungume Laminu, ya na murna,
"Kai sake ni menene haka, sai an gan mu a ce 'yan iska muke, kai jaye"
Tura Isah baya Laminu ya yi, ya na waige waige, cikin jin dad'i Isah ke bawa Laminu labarin yanda ya san an kama yaron nasu, Laminu ya ce,
"To rudewar da kayi na yasa bata idasa baka labari ba, da ta baka, da ka gane cewar an kashe shi , ko kuma ba a sanar da ita ya mace ba"
"Kaiii Laminu amma kai shege ne"
"Ahafff hauka nike da zan bari asiri na shi tonu? Kai fa ba dan garin nan bane ba, ka na iya guduwa ko baka da iyaye a Kano ,ni kuwa uwaye na da uwayen matata nan suke"
Hira suka dan taba Laminu ya ce shi zai shiga matar shi na can na jiran shi, Isah ma murmushin da bai taba kalar shi ba a rayuwar shi ya yi, tare da cewa,
"Ni ma tun dazu take min waya, bari na je gida"
Sallama suka yi, kowa ya kama hanyar shi.
Ko da Isah ya isa gidan, ya tarar da shi kamar kullum, a share, a tsaftace, abincin shi na wajen da aka saba aje masa, har da sabuwar tabarma.
Komai da yake buqata ya same shi har da qari ma, amma fa Hansatu ce kawai bai gani ba kamar yanda ta saba, ko qarfe nawa ze kai a waje, ta na nan ta na jiran shi.
Ko daya leqa dakin da kyau kwance ya gan ta, sanye da wata iriyar rigar bacci mai daukan hankali, sake leqa wa ya yi shin Hansatu ce ko wace ce? Kafff rayuwar su bata taɓa sanya rigar bacci ba, tunda ya aure ta ba ko lefe, balle ya ce ya saka a ciki.
Baccin ta take cikin kwanciyar hankali da nutsuwa, Isah kuwa hankalin shi in ya fi cikin unguwar ya tashi.
Cike da damuwa ya zauna bakin gadon, ya kai hannu zai tashe ta, da sauri ya janye, dan bai san da me zata farka ba, rashin sanin meye a zuciyar ta na sa Isah damuwa, da dakatar da shi akan abinda ya so aikatawa.
Ya kai qarfe goma da minti sha daya ya na ta kai komo, tsakanin daki da parlour, motsin shi ya yi yawa, har ya hana ta bacci, da wata iriyar miqa ta tashi, wadda ta sanya Isah kai mata runguma, turashi baya ta yi, sannan ta ce,
"Meye haka? Bacci fa ni kai, duk ka ishen da motsi, mi ka ke bid'a wanda ban aje maka ba? Ko kuwa kwanan da nikai ka ke baqin ciki na yi duk da wuni da na yi aiki?"
Zama Isah ya yi a bakin gadon, ya na kama wandon shi, jijiyoyin kan shi har sun bayyana rud'u rud'u,
"Dan Allah Hansatu ki taimaka min, ni ba ni buqatar komi sai ke, na qoshi da abincin ma ni, ki taimaka min"
Tashi ta yi, ta na wata iriyar tafiya da ni kaina sai da na yi mamakin shin anya Hansatun Isah ce? Ko kuwa Hafsatun Hajiya ce?
Hijabin ta ta zira ta fita waje, fitsari ta yi, ta wanke bakin ta, dan ta yi bacci ta ji ya sauya mata, sai da ta wanke fuskar ta sannan ta koma d'akin, Isah ta gani cikin mawuyacin halin da ba zata iya kauda kai ba, ko ba dan shi ba, dan tsoron fushin da Allah da Mala'iku za su yi da ita, ta sani duk matar da mijin ta ya neme ta a shimfida komai fushin da take da shi, haramun ne matar nan ta qaurace wa mijin, in ta qaurace masa direct, ta ce ba zata ba, ko ta dinga yin wasu abubuwa indirectly har ya gaji da jiran ta ya yi bacci, to fa ta na cikin tsinuwar Allah da mala'ikun shi, har gari ya waye.
"Ni da kai akwai banbanci, domin kuwa na san Allah, na san dokokin da ya gindaya akan aure, kuma ina qoqarin kare kai na da take su, sai dai in da rashin sani, amma ka san wani abu, daga yanzu ba zan sake kwanciya da kai ba ba tare daka yi wanka ba, ba tare da ka wanke bakin ka da kyau ba, ba zan kwanta da kai ba ni ina cutuwa kai ka na mora ta ba wallah, an wuce wannan lokacin, in ka na buqata ta, ka tai zuwa wanka,in ka dawo ka wanke bakin ka, ban cuce ka ba na daina bari ka na cuta min wallah"
Komawa ta yi, ta yi wata iriyar kwanciya mai daukan hankali,a sukwane Isah ya bar dakin, ya shiga wanka, ya jima ya na dirzawa da cud'a jikin shi, sai da ya tabbata ya fita fess sannan ya dauraye jikin shi ya fita, abun ya bashi mamaki, da ya ga brush da toothpaste a ajiye a saman buta a qofar bayin, bai tsaya dogon bincike ba ya dauka ya wanke bakin shi tass, sannan ya koma dakin.
"Shin wai da ka taho ba alwala, ka yi sallar Isha'i halan?"
"Hansatu ba na jin sallah ta tana amsuwa innayi ta haka nan, dan Allah ki taimaka min"
"Watakam za ka iya yin wanka da brush dan biyan buqatar ka, amma ba zaka iya yin Sallah ba, dan cika umarnin Allah, lallai baka tashi kwana ba wallah"
Juyi ta sake, cike da kwarewa, sai da na dauki Style din juyin (lols) ta koma ta kwantar da kan ta a pillow, hankalin ta kwance.
Isah kuwa kuka ne kawai bai yi ba dan takaici, Gashi yanzu yanda ya ke hango rashin jin tsoron shi a idanun Hansatu, ba ya jin ko fada ya tsaya yi da ita zai samu riba.
Sallah ya je ya yi, a gurguje, ya koma dakin, gani ya yi ta kashe wutar dakin, a cikin duhun ya qarasa gadon......
Hansatu ta bawa Isah mamaki matuqa, ta shayar da shi zumar da ya dinga tunanin anya duk duniya akwai wadda ta fi Hanstun shi kuwa? Maqale ta ya yi gam da jikin shi, kamar ya na tsoron wani zai janye ta.
Ita kuwa kwace jikin ta tayi, ta tafi ta yi wanka, ta yi nafila raka'a biyu, tare da addu'ar Allah ya qara kawo mata zaman lafiya da kwanciyar hankali a gidan ta, sannan ta haye gado ta kwanta, kusa da Isah da ke ta sheqa munshari.
Da safe kuwa haka Isah ya debo kayan da ya samo a Makka wanda Larabawa suke bayarwa, sadaka, ya dinga bawa Hansatu ya na zuba mata qarya, ya na kurin shi ya siyo mata da kudin shi.
Ita kuwa fuskar ta ba walwala, ba fara'a take furta
"Na gode, Allah shi biya"
"Hajiya ai ni ke da godiya, ba abinda zan ce da Hansatu sai Allah ya mata albarka, Allah kuma ya haɗa ta da dukkan alkhairi duniya da lahira"
Farin cikin da Hajiya ta shiga ba mai faduwa bane,kowacce uwa zata so jin wadannan kalaman a bakin surukin ta, to gashi ita Allah ya jiyar da ita, tun da sauran rayuwar ta.
"Ban ga Yaya ba, ko dai ba shi nan na?"
"Eh shi na office, ai sai yamma zai dawo, wan mata tai yak-kirai tun sahe akwai abinda suke yi"
"Allah Sarki, Allah ya bada sa'a, Allah ya jiqan Alhaji, har na tuna sanda muke tafiya, tun sahe sai dare, ba ya bari na da yunwa, komi yaci shi zai ban, haka zai wuni aiki, rayuwa kenan"
Hira ce sosai ta shaquwa da sabo ke gudana tsakanin Isah da surukar shi, tun sanda ya bar gida nan ya nufa, ya ke ta Suratu, hankalin shi gaba daya ya tattara ya koma gida wajen Hansatu, amma ya fi so sai ta huce ya koma, dan ya san ba ta iya fushi da shi, kamar daga sama ya ji maganar Hajiya ta ce,
"Ai shawarar da kabban ita na bi, ana nan ana binciken mutanen da sun ka yi kidnapping di na, kuma da alama ana nan ana samun nasara, dan har jami'an tsaro sun Kama yaro guda da an ka had'a baki da shi an ka swace ni"
Wani irin tari Isah yake sakamakon kwarewa da ya yi da lemon da ya daga glass cup ya na korawa, sannu Hajiya ta dinga zuba masa, miqewa ya yi, cikin yaqe, ya ce,
"Allah dai shi tona ma koma waye asiri, bari na tai na ga ta na ta yi min flashing, wataqila suna bidar wani abu"
Murmushi Hajiya ta yi, ta ce ya jira ta kawo masa saqo ya kai mata, ji ya yi kamar ya gudu kan ta dawo, kuka ne kawai Isah be ba, saboda jimawar da Hajiya ta yi.
Kwalin madarar ruwa ta kai masa da galan din zuma, ta ce ya kai ma Hanstu, godiya ya dinga yi, ya na sauri ya bar gidan, mai gadi na gaida shi ko kula shi be ba, da da ne kuwa sai ya tsaya ya masa kurin shi surukin gidan ne.
Ya na fita titi sosai ya lalubi No Laminu, bai dauka ba, ji ya yi kamar ya fashe da kuka dan takaici, in asirin shi ya tonu ai ya kade.
Bari ma, saudiyar nan zai koma zaman Nija be kama shi ba........
*Yayah Isah namu na mudunci😂*
💅🏻 *A GARIN MU* 💅🏻
BY HAERMEEBRAERH
PAGE 50:
A cikin daren Isah ya je gidan Laminu, Asshibi na ta mitar an hana su sakewa da mijin ta, ya fita tun safe, sai daren ya dawo, hakuri Laminu ya bata ya sanya rigar shi ya bude gate ya fita, Isah ya gani tsaye cikin tsananin damuwa, da tashin hankali, murmushi ya yi, ya ce wa Isah,
"Na san me ya kawo ka, kwantar da hankalin ka, magana ta qare dazu da rana, na aika wani yaro da maganin kusa (bera) an sa mishi ga abincin da an ka kai, ya ci ya mutu, sai in ga me bada shaida"
Wata iriyar ajiyar zuciya Isah ya sauke, tare da sakin kwalin madarar a qasa, ya rungume Laminu, ya na murna,
"Kai sake ni menene haka, sai an gan mu a ce 'yan iska muke, kai jaye"
Tura Isah baya Laminu ya yi, ya na waige waige, cikin jin dad'i Isah ke bawa Laminu labarin yanda ya san an kama yaron nasu, Laminu ya ce,
"To rudewar da kayi na yasa bata idasa baka labari ba, da ta baka, da ka gane cewar an kashe shi , ko kuma ba a sanar da ita ya mace ba"
"Kaiii Laminu amma kai shege ne"
"Ahafff hauka nike da zan bari asiri na shi tonu? Kai fa ba dan garin nan bane ba, ka na iya guduwa ko baka da iyaye a Kano ,ni kuwa uwaye na da uwayen matata nan suke"
Hira suka dan taba Laminu ya ce shi zai shiga matar shi na can na jiran shi, Isah ma murmushin da bai taba kalar shi ba a rayuwar shi ya yi, tare da cewa,
"Ni ma tun dazu take min waya, bari na je gida"
Sallama suka yi, kowa ya kama hanyar shi.
Ko da Isah ya isa gidan, ya tarar da shi kamar kullum, a share, a tsaftace, abincin shi na wajen da aka saba aje masa, har da sabuwar tabarma.
Komai da yake buqata ya same shi har da qari ma, amma fa Hansatu ce kawai bai gani ba kamar yanda ta saba, ko qarfe nawa ze kai a waje, ta na nan ta na jiran shi.
Ko daya leqa dakin da kyau kwance ya gan ta, sanye da wata iriyar rigar bacci mai daukan hankali, sake leqa wa ya yi shin Hansatu ce ko wace ce? Kafff rayuwar su bata taɓa sanya rigar bacci ba, tunda ya aure ta ba ko lefe, balle ya ce ya saka a ciki.
Baccin ta take cikin kwanciyar hankali da nutsuwa, Isah kuwa hankalin shi in ya fi cikin unguwar ya tashi.
Cike da damuwa ya zauna bakin gadon, ya kai hannu zai tashe ta, da sauri ya janye, dan bai san da me zata farka ba, rashin sanin meye a zuciyar ta na sa Isah damuwa, da dakatar da shi akan abinda ya so aikatawa.
Ya kai qarfe goma da minti sha daya ya na ta kai komo, tsakanin daki da parlour, motsin shi ya yi yawa, har ya hana ta bacci, da wata iriyar miqa ta tashi, wadda ta sanya Isah kai mata runguma, turashi baya ta yi, sannan ta ce,
"Meye haka? Bacci fa ni kai, duk ka ishen da motsi, mi ka ke bid'a wanda ban aje maka ba? Ko kuwa kwanan da nikai ka ke baqin ciki na yi duk da wuni da na yi aiki?"
Zama Isah ya yi a bakin gadon, ya na kama wandon shi, jijiyoyin kan shi har sun bayyana rud'u rud'u,
"Dan Allah Hansatu ki taimaka min, ni ba ni buqatar komi sai ke, na qoshi da abincin ma ni, ki taimaka min"
Tashi ta yi, ta na wata iriyar tafiya da ni kaina sai da na yi mamakin shin anya Hansatun Isah ce? Ko kuwa Hafsatun Hajiya ce?
Hijabin ta ta zira ta fita waje, fitsari ta yi, ta wanke bakin ta, dan ta yi bacci ta ji ya sauya mata, sai da ta wanke fuskar ta sannan ta koma d'akin, Isah ta gani cikin mawuyacin halin da ba zata iya kauda kai ba, ko ba dan shi ba, dan tsoron fushin da Allah da Mala'iku za su yi da ita, ta sani duk matar da mijin ta ya neme ta a shimfida komai fushin da take da shi, haramun ne matar nan ta qaurace wa mijin, in ta qaurace masa direct, ta ce ba zata ba, ko ta dinga yin wasu abubuwa indirectly har ya gaji da jiran ta ya yi bacci, to fa ta na cikin tsinuwar Allah da mala'ikun shi, har gari ya waye.
"Ni da kai akwai banbanci, domin kuwa na san Allah, na san dokokin da ya gindaya akan aure, kuma ina qoqarin kare kai na da take su, sai dai in da rashin sani, amma ka san wani abu, daga yanzu ba zan sake kwanciya da kai ba ba tare daka yi wanka ba, ba tare da ka wanke bakin ka da kyau ba, ba zan kwanta da kai ba ni ina cutuwa kai ka na mora ta ba wallah, an wuce wannan lokacin, in ka na buqata ta, ka tai zuwa wanka,in ka dawo ka wanke bakin ka, ban cuce ka ba na daina bari ka na cuta min wallah"
Komawa ta yi, ta yi wata iriyar kwanciya mai daukan hankali,a sukwane Isah ya bar dakin, ya shiga wanka, ya jima ya na dirzawa da cud'a jikin shi, sai da ya tabbata ya fita fess sannan ya dauraye jikin shi ya fita, abun ya bashi mamaki, da ya ga brush da toothpaste a ajiye a saman buta a qofar bayin, bai tsaya dogon bincike ba ya dauka ya wanke bakin shi tass, sannan ya koma dakin.
"Shin wai da ka taho ba alwala, ka yi sallar Isha'i halan?"
"Hansatu ba na jin sallah ta tana amsuwa innayi ta haka nan, dan Allah ki taimaka min"
"Watakam za ka iya yin wanka da brush dan biyan buqatar ka, amma ba zaka iya yin Sallah ba, dan cika umarnin Allah, lallai baka tashi kwana ba wallah"
Juyi ta sake, cike da kwarewa, sai da na dauki Style din juyin (lols) ta koma ta kwantar da kan ta a pillow, hankalin ta kwance.
Isah kuwa kuka ne kawai bai yi ba dan takaici, Gashi yanzu yanda ya ke hango rashin jin tsoron shi a idanun Hansatu, ba ya jin ko fada ya tsaya yi da ita zai samu riba.
Sallah ya je ya yi, a gurguje, ya koma dakin, gani ya yi ta kashe wutar dakin, a cikin duhun ya qarasa gadon......
Hansatu ta bawa Isah mamaki matuqa, ta shayar da shi zumar da ya dinga tunanin anya duk duniya akwai wadda ta fi Hanstun shi kuwa? Maqale ta ya yi gam da jikin shi, kamar ya na tsoron wani zai janye ta.
Ita kuwa kwace jikin ta tayi, ta tafi ta yi wanka, ta yi nafila raka'a biyu, tare da addu'ar Allah ya qara kawo mata zaman lafiya da kwanciyar hankali a gidan ta, sannan ta haye gado ta kwanta, kusa da Isah da ke ta sheqa munshari.
Da safe kuwa haka Isah ya debo kayan da ya samo a Makka wanda Larabawa suke bayarwa, sadaka, ya dinga bawa Hansatu ya na zuba mata qarya, ya na kurin shi ya siyo mata da kudin shi.
Ita kuwa fuskar ta ba walwala, ba fara'a take furta
"Na gode, Allah shi biya"