Sashe 54
A Garin Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Har goma da rabi na dare basu sake kira ba, ga kudi an hada su kawai ake jira, ranar haka gidaje biyun suka kwana cikin tashin hankali , Yayan Hansatu kuwa damuwa ta masa yawa, shi kadai ne a gidan ba mai lallashin shi, ran shi ya ɓaci, kuwa da rashin matar shi a kusa, cikin fushi ya dau waya ya dinga kiran ta, a so samun shi ya sake ta ya huta, tunda bai ga amfanin ta ba.
Cikin rashin sa'a bata daga wayar ba, haka ya hakura, ya dinga sintiri, daga daki zuwa parlour, zuwa dakin Hajiya, qarshe a dakin Hajiya ya kwanta, bacci mai dadi ya dauke shi.
Da misalin qarfe biyu na dare, wayar shi ta hau qara, ya na dubawa ya ga No masu garkuwa da mutanen ne, hannu na rawa ya dauka.
"Ina ta kiran ku ba ta shiga, na hada kuddin tun dazu gasu"
"Tauu ka hito ka kawo su daidai inda kun ka samu motar Hajiyan zan karba, in ka yi gangancin zuwa da jami'an tsaro ina mai tabbatar maka, na bada umarnin in na qara minti uku ban koma ba su kashe ta"
Jiki na rawa ya dauki jakar da kudin suke waya na kunnen shi ya fita daga gidan a qafa,
"Ba zan zo da kowa ba, gani nan zuwa, da qafa, ita ko Hajiya yau she za ta dawowa?"
"Kai dai ka kawo kuddi, ai ni na maka alqawarin zata dawo lahiya ko?"
"Tau gani zuwa"
Tafe yake ya na nishi, saboda ba laifi ya na da dan jiki, gashi bai saba da motsa jiki ba, duk inda za shi sai a mota,sai waige yake ko zai ga wanda yake waya da shi .
Har ya isa wajen da aka ce ya aje kudin ya tafi bai ga kowa ba, ya na ajiye wa kuwa ya juya dan komawa gida.
Bai sake waigawa ba sai da ya yi nisa sosai, duk da wajen da dan duhu, bai hana shi ganin wani mutum ya dauki jakar ba ya tafi, a can nesa da wajen mota ce kunne ta na jiran mutumin, ya na zuwa ya shiga suka bar wajen, wani irin kukan takaici ne ya zo wa Yayan Hansatu, ina aka kai musu Hajiyan su, a wanne hali take?
Dama Hajiya ita ce ke tada shi sallar asuba, to yanzu bata nan, baccin shi yake ta sha, musamman dama bai samu kwantawa da wuri ba.
Buga qofar shiga gidan ya ji ana yi da qarfi kamar za a balle qofar, a gigice ya tashi cikin magagin bacci, ya nufi qofar ya na fadin
"Wane na?"
"Alhaji Hajiya ta taddawo,bude qohwa"
Ai ya na jin Muryar mai gadi kuma ya ji an ce Hajiya ce ta dawo, da sauri ya bude qofar, shi ya kamo ta suka shiga ciki, kwana ɗaya ta yi ba a gida ba, amma duk ta fada, bakin nan ya bushe, su ko dan ruwa ba su san su bawa mutum ba, (ashe gwanda su Oga Lawwali ma).
Ruwa mai dumi Hajiya ta haɗa ta fara yin wanka, kafin masu aikin gidan su zo da safe ta samarwa kan ta abinda za ta ci, dan kuwa wata baqar yunwa take ji, da misalin bakwai na safe, ta kira Hansatu ta sanar da ita, Allah ya dawo da ita gida lafiya.
Murna da godiya ga Allah Hansatu ta yi ta yi, ta ce za ta je duba Hajiyan,Hajiya ta ce ah ah ta bari ba yanzu ba, domin ta kula ko ma wa ke kidnapping din nan idon shi na kan su ne, saboda an ga su na da azziqi, hira suka sha sosai, Hajiya na bata labarin yanayin yanda aka dauke ta, da wajen da aka aje ta, Hansatu ta tausaya ma mahaifiyar ta, sannan ta mata fatan Allah ya kiyaye gaba, Allah kuma ya ninka musu arzikin su da suka rasa.
Bayan sun kashe wayar take sanar da Asshibi, Asshibi ta taya ta murna sosai, sannan kuma ta mata fatan alkhairi, yara ma sai murna suke kakar su ta dawo lafiya.
A ranar Isah da abokin sheqe ayar shi suka raba kudin su daidai, kowa na ta farin ciki da murna.
Ya tafi yawon bude ido a cikin garin Makka Hajiya ta kira shi, kamar ba zai dauka ba, ya daga cikin bata rai, ya yi sallama, bayan ta amsa sun gaisa ne ta ke tambayar shi, ya taji Muryar shi qasa qasa?
"Ban da lafiya ne, yanzu ma asibiti zani, zazzaɓi ya kama ni, ina so na ga likita"
"Subhanallahi, Allah shi baka lahiya, ni ma jiya ina zaune an ka kire ni an ka ce Hansatu ba lahiya ta na asibiti, na hita ni d'ai dan na duba jikin ta,ina hita a mota an ka samu wasu marassa imanin sun ka sace ni, sai da an ka biya million goma da subahi sun ka maido ni gida"
"Innalillahi wa inna'ilaihirraji'un, ya Salam, subhanallahi, Hajiya ke da kan ki aka sace, ince dai ba abinda ya samu lafiyar ki? Dan ta kudi ai mai sauqi ne, Indai lafiya bata tabu ba,"
Yanda ya rude sai ya sanya Hajiya ganin rashin kyautawar ta, da ta sanar da shi, musamman labarin tunda ya ce ba shi da lafiya, ya na ma asibiti.
"Kar ka daga hankalin ka dan Allah, ina nan lafiya qlou, ai Hansatu nacewa zata zo duba ni, nace dan Allah ta zauna, masu satar nan, da dukkan alamu sun san ko mu su waye"
"Tabbas kuwa Hajiya, ya kamata kuma a tsananta bincike,abun ya yi yawa haka nan"
"Inshaa Allahu, bincike kam za a yi shi, yanzu haka magana na ga hukuma"
Wani yawu Isah ya hadiya mai qulle wuya, sai ga tari, ba qaqqautawa, sannu Hajiya tai ta masa tare da yin sallama da shi, ta kira Yayan Hansatu ta na ta masa fada akan ya dawo da matar shi .
***************************
Soyayya tsakanin Sultana da Lawwali ta bunqasa, ta girmama, ta yanda Sultana ba ta iya kwana ɗaya bata gan shi ba, shi kuma ya na sane watarana zai fashi ya qi zuwa, da kan ta take sanya driver ya aje ta gidan Lawwali ta duba shi, kafin ta wuce.
Lawwali yanzu ba shi da burin da ya wuce na ya ga ya mallaki Sultana a matsayin matar shi,duk da ya rasa dalilin jin hakan, amma abu daya ya sani, zai aure ta ne dan daukan fansa, Itan ma bata da burin da ya wuce na ta auri Auwal,babban burin ta kenan yanzu a duniya, ta ga ta zama mata a wajen Auwal din ta.
Lawwali ne ke kulle gidan shi, ya shiga motar shi, sai gidan Gwamna Halliru, dan ya na sane da cewar bai je ko ina ba, ya na da masu leqen asiri a gidan Gwamnan ba tare da kowa ya sani ba, duk wani bayanai da ya ke da buqatar sani ana sanar da shi, kafin ma ya tambaya.
Har cikin gidan ya shigar da motar shi, a dadai wannan lokacin Sultana na NGO, sun rabu da shi akan ba shi da lafiya, ba zai samu damar zuwa ba.
Har parlour ya shiga ba tare da ya sanar da kowa zuwan shi ba, da Sultan suka fara haduwa ya shirya tsaf zai fita wajen abokin shi, bayan sun gaisa ne ya ke sanar da shi ya zo wajen su Hajiya ne, Sultan ne ya sanar da su zuwan Lawwali, sannan suka sake gaisa wa ya tafi, Lawwali na zaune harde da qafa daya kan daya kamar ya na a gidan shi, Hajiya Ikee da Gwamna Halliru suka fito a tare.
Cikin daure fuska tamau Lawwali ya miqe tsaye, ya na wasa da glass din shi, sannan ya ce,
"Ba na son jira ka hi kowa sanin haka Excellency ,me yasa ka ke bari na yin jira?"
"Lawwali har yanzu ina da tantama akan baka d'iya...."
A zafafe Lawwali ya juya ya kalli Gwamna ya ce,
"Tantama? Tantama hwa kacce, ka na da wani zabi ne da ya wuce ka aura min ita, ko ku na so ko ba ku so,na ga alama kun zaci ba zan aikata abinda na hwadi ba ko? Ka san ni, ka san wane ne ni, ka san mi zan iya da wanda ba zan iya ba, kar ka bari raina shi fi haka ɓaci, abin ba zai mana kyawu ba"
Cikin hura hanci Hajiya Ikee ta ce,
"Yaro yaro ne bai san wuta ba sai ya taka, in ka na da abinda ka ke ganin za ka yi, ka je ka yi, diya ta bata auren dan iska irin ka, lalatacce d'ebabbe"
Abu kamar sihiri, kafin ta rufe labban ta Lawwali ne a gaban ta, ya sa hannun shi guda daya ya shaqe mata wuya, ya sanya bakin bindigar shi cikin bakin ta, jijiyoyin kan shi, da hannayen shi sun fito rudu rudu, idanun nan kamar an watsa masa barkono, leban shi na qasa ya ciza sai da jini ya fito,Gwamna ne ya isa gaban shi ya fara qoqarin kwace Hajiya Ikee da ke fitar da numfashi a wahalce, idanun ta na ta tsiyayar da hawaye, sai miqawa gwamna hannu take, wata tsawa Lawwali ya daka mata, akan ta dena wannan motsi da kukan da take, diffff ta hadiye kukan nata, ido ya fito ya mata gulu gulu.
"Me ki ka ce, yaro bai san wuta ba sai ya taka? Waye yaro? Na ce waye yaro? A duniya akwai lalatattu d'ebabbu Sama da ku ne? Har ni zaki kalla ki wa zagin d'iban albarka, ke ba dan ina da burika masu yawa ba kin isa na bar ki ki kai gobe, (subhaballah kamar ran a hannun shi yake)"
Ba damar magana bindiga na baki, ga wuya ya sha shaqa,
Da qarfi ya wurga ta qasa ta fad'i, a gigice take neman iskar shaqa, tsabar azabar da take ciki, dishi dishi take gani, Gwamna ne ya duqa gaban ta, ya na taimaka mata wajen daidaita numfashin ta.
Cikin rashin sa'a bata daga wayar ba, haka ya hakura, ya dinga sintiri, daga daki zuwa parlour, zuwa dakin Hajiya, qarshe a dakin Hajiya ya kwanta, bacci mai dadi ya dauke shi.
Da misalin qarfe biyu na dare, wayar shi ta hau qara, ya na dubawa ya ga No masu garkuwa da mutanen ne, hannu na rawa ya dauka.
"Ina ta kiran ku ba ta shiga, na hada kuddin tun dazu gasu"
"Tauu ka hito ka kawo su daidai inda kun ka samu motar Hajiyan zan karba, in ka yi gangancin zuwa da jami'an tsaro ina mai tabbatar maka, na bada umarnin in na qara minti uku ban koma ba su kashe ta"
Jiki na rawa ya dauki jakar da kudin suke waya na kunnen shi ya fita daga gidan a qafa,
"Ba zan zo da kowa ba, gani nan zuwa, da qafa, ita ko Hajiya yau she za ta dawowa?"
"Kai dai ka kawo kuddi, ai ni na maka alqawarin zata dawo lahiya ko?"
"Tau gani zuwa"
Tafe yake ya na nishi, saboda ba laifi ya na da dan jiki, gashi bai saba da motsa jiki ba, duk inda za shi sai a mota,sai waige yake ko zai ga wanda yake waya da shi .
Har ya isa wajen da aka ce ya aje kudin ya tafi bai ga kowa ba, ya na ajiye wa kuwa ya juya dan komawa gida.
Bai sake waigawa ba sai da ya yi nisa sosai, duk da wajen da dan duhu, bai hana shi ganin wani mutum ya dauki jakar ba ya tafi, a can nesa da wajen mota ce kunne ta na jiran mutumin, ya na zuwa ya shiga suka bar wajen, wani irin kukan takaici ne ya zo wa Yayan Hansatu, ina aka kai musu Hajiyan su, a wanne hali take?
Dama Hajiya ita ce ke tada shi sallar asuba, to yanzu bata nan, baccin shi yake ta sha, musamman dama bai samu kwantawa da wuri ba.
Buga qofar shiga gidan ya ji ana yi da qarfi kamar za a balle qofar, a gigice ya tashi cikin magagin bacci, ya nufi qofar ya na fadin
"Wane na?"
"Alhaji Hajiya ta taddawo,bude qohwa"
Ai ya na jin Muryar mai gadi kuma ya ji an ce Hajiya ce ta dawo, da sauri ya bude qofar, shi ya kamo ta suka shiga ciki, kwana ɗaya ta yi ba a gida ba, amma duk ta fada, bakin nan ya bushe, su ko dan ruwa ba su san su bawa mutum ba, (ashe gwanda su Oga Lawwali ma).
Ruwa mai dumi Hajiya ta haɗa ta fara yin wanka, kafin masu aikin gidan su zo da safe ta samarwa kan ta abinda za ta ci, dan kuwa wata baqar yunwa take ji, da misalin bakwai na safe, ta kira Hansatu ta sanar da ita, Allah ya dawo da ita gida lafiya.
Murna da godiya ga Allah Hansatu ta yi ta yi, ta ce za ta je duba Hajiyan,Hajiya ta ce ah ah ta bari ba yanzu ba, domin ta kula ko ma wa ke kidnapping din nan idon shi na kan su ne, saboda an ga su na da azziqi, hira suka sha sosai, Hajiya na bata labarin yanayin yanda aka dauke ta, da wajen da aka aje ta, Hansatu ta tausaya ma mahaifiyar ta, sannan ta mata fatan Allah ya kiyaye gaba, Allah kuma ya ninka musu arzikin su da suka rasa.
Bayan sun kashe wayar take sanar da Asshibi, Asshibi ta taya ta murna sosai, sannan kuma ta mata fatan alkhairi, yara ma sai murna suke kakar su ta dawo lafiya.
A ranar Isah da abokin sheqe ayar shi suka raba kudin su daidai, kowa na ta farin ciki da murna.
Ya tafi yawon bude ido a cikin garin Makka Hajiya ta kira shi, kamar ba zai dauka ba, ya daga cikin bata rai, ya yi sallama, bayan ta amsa sun gaisa ne ta ke tambayar shi, ya taji Muryar shi qasa qasa?
"Ban da lafiya ne, yanzu ma asibiti zani, zazzaɓi ya kama ni, ina so na ga likita"
"Subhanallahi, Allah shi baka lahiya, ni ma jiya ina zaune an ka kire ni an ka ce Hansatu ba lahiya ta na asibiti, na hita ni d'ai dan na duba jikin ta,ina hita a mota an ka samu wasu marassa imanin sun ka sace ni, sai da an ka biya million goma da subahi sun ka maido ni gida"
"Innalillahi wa inna'ilaihirraji'un, ya Salam, subhanallahi, Hajiya ke da kan ki aka sace, ince dai ba abinda ya samu lafiyar ki? Dan ta kudi ai mai sauqi ne, Indai lafiya bata tabu ba,"
Yanda ya rude sai ya sanya Hajiya ganin rashin kyautawar ta, da ta sanar da shi, musamman labarin tunda ya ce ba shi da lafiya, ya na ma asibiti.
"Kar ka daga hankalin ka dan Allah, ina nan lafiya qlou, ai Hansatu nacewa zata zo duba ni, nace dan Allah ta zauna, masu satar nan, da dukkan alamu sun san ko mu su waye"
"Tabbas kuwa Hajiya, ya kamata kuma a tsananta bincike,abun ya yi yawa haka nan"
"Inshaa Allahu, bincike kam za a yi shi, yanzu haka magana na ga hukuma"
Wani yawu Isah ya hadiya mai qulle wuya, sai ga tari, ba qaqqautawa, sannu Hajiya tai ta masa tare da yin sallama da shi, ta kira Yayan Hansatu ta na ta masa fada akan ya dawo da matar shi .
***************************
Soyayya tsakanin Sultana da Lawwali ta bunqasa, ta girmama, ta yanda Sultana ba ta iya kwana ɗaya bata gan shi ba, shi kuma ya na sane watarana zai fashi ya qi zuwa, da kan ta take sanya driver ya aje ta gidan Lawwali ta duba shi, kafin ta wuce.
Lawwali yanzu ba shi da burin da ya wuce na ya ga ya mallaki Sultana a matsayin matar shi,duk da ya rasa dalilin jin hakan, amma abu daya ya sani, zai aure ta ne dan daukan fansa, Itan ma bata da burin da ya wuce na ta auri Auwal,babban burin ta kenan yanzu a duniya, ta ga ta zama mata a wajen Auwal din ta.
Lawwali ne ke kulle gidan shi, ya shiga motar shi, sai gidan Gwamna Halliru, dan ya na sane da cewar bai je ko ina ba, ya na da masu leqen asiri a gidan Gwamnan ba tare da kowa ya sani ba, duk wani bayanai da ya ke da buqatar sani ana sanar da shi, kafin ma ya tambaya.
Har cikin gidan ya shigar da motar shi, a dadai wannan lokacin Sultana na NGO, sun rabu da shi akan ba shi da lafiya, ba zai samu damar zuwa ba.
Har parlour ya shiga ba tare da ya sanar da kowa zuwan shi ba, da Sultan suka fara haduwa ya shirya tsaf zai fita wajen abokin shi, bayan sun gaisa ne ya ke sanar da shi ya zo wajen su Hajiya ne, Sultan ne ya sanar da su zuwan Lawwali, sannan suka sake gaisa wa ya tafi, Lawwali na zaune harde da qafa daya kan daya kamar ya na a gidan shi, Hajiya Ikee da Gwamna Halliru suka fito a tare.
Cikin daure fuska tamau Lawwali ya miqe tsaye, ya na wasa da glass din shi, sannan ya ce,
"Ba na son jira ka hi kowa sanin haka Excellency ,me yasa ka ke bari na yin jira?"
"Lawwali har yanzu ina da tantama akan baka d'iya...."
A zafafe Lawwali ya juya ya kalli Gwamna ya ce,
"Tantama? Tantama hwa kacce, ka na da wani zabi ne da ya wuce ka aura min ita, ko ku na so ko ba ku so,na ga alama kun zaci ba zan aikata abinda na hwadi ba ko? Ka san ni, ka san wane ne ni, ka san mi zan iya da wanda ba zan iya ba, kar ka bari raina shi fi haka ɓaci, abin ba zai mana kyawu ba"
Cikin hura hanci Hajiya Ikee ta ce,
"Yaro yaro ne bai san wuta ba sai ya taka, in ka na da abinda ka ke ganin za ka yi, ka je ka yi, diya ta bata auren dan iska irin ka, lalatacce d'ebabbe"
Abu kamar sihiri, kafin ta rufe labban ta Lawwali ne a gaban ta, ya sa hannun shi guda daya ya shaqe mata wuya, ya sanya bakin bindigar shi cikin bakin ta, jijiyoyin kan shi, da hannayen shi sun fito rudu rudu, idanun nan kamar an watsa masa barkono, leban shi na qasa ya ciza sai da jini ya fito,Gwamna ne ya isa gaban shi ya fara qoqarin kwace Hajiya Ikee da ke fitar da numfashi a wahalce, idanun ta na ta tsiyayar da hawaye, sai miqawa gwamna hannu take, wata tsawa Lawwali ya daka mata, akan ta dena wannan motsi da kukan da take, diffff ta hadiye kukan nata, ido ya fito ya mata gulu gulu.
"Me ki ka ce, yaro bai san wuta ba sai ya taka? Waye yaro? Na ce waye yaro? A duniya akwai lalatattu d'ebabbu Sama da ku ne? Har ni zaki kalla ki wa zagin d'iban albarka, ke ba dan ina da burika masu yawa ba kin isa na bar ki ki kai gobe, (subhaballah kamar ran a hannun shi yake)"
Ba damar magana bindiga na baki, ga wuya ya sha shaqa,
Da qarfi ya wurga ta qasa ta fad'i, a gigice take neman iskar shaqa, tsabar azabar da take ciki, dishi dishi take gani, Gwamna ne ya duqa gaban ta, ya na taimaka mata wajen daidaita numfashin ta.