Sashe 79
A Garin Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tashi ta yi ta tura ni waje, ta rufe musu qofar su, cikin jin haushin Sultana, na bar wajen ban tsaya a ko ina ba sai d'akin Mubaraka, ta na zaune, ta na shan ice cream, Taheer ya yi sallama, d'aga kai ta yi, ta kalle shi, dan ya riga ya shiga tun kafin ta amsa masa sallamar shi, balle ya jira ta bashi izinin shiga,
"Yah Taheer lafiya dai ko?"
"Lahiya qalou Mubaraka, sai dai abinda na ke tahe da shi, shi na iya jaddada zaman lahiya ko samar da rashin ta"
Cike da mamakin kalaman shi ta miqe ta daura zani a saman qaramin wandon dake jikin ta, Taheer kuwa ko irin d'an kauda kan nan, ta na gama daurawa ta zauna a bakin katifar dakin, ta bashi dukkan nutswar ta, dan sauraran abinda ya ke tafe da shi,
"Mubaraka, kin sani, na dauke ki kamar qauna ta ko?"
Daga kan ta tayi, cikin gasgata maganar shi,
"Mubaraka son da ni kai miki a matsayin qauna, ya rikid'e ya koma soyayyar da na ke hwatan ta kai mu ga yin aure, amma har sai kin amince, zan sanar da Oga da Fateema, amma in ki ka tabbatar min da baki so na, gobe zan koma Kano, na hakura da ke har abada"
Wani irin nauyi ta ji Taheer ya dora Mata akai, wanda ta rasa ma na mene ne, shin kunyar shi take ji, ko ganin rashin dacewa ya ce ya na son ta ne ya sa ta jin nauyin shi? Bakin ta na so ya fadi abinda ke zuciyar ta amma ya kasa furta komai, gyara zaman ta tayi,cikin sanya jarumta a Muryar ta ta ce,
"Yah Taheer, ba zan boye maka komai ba, dan in na boye maka ban kyauta ba, saboda matsayin da na baka na yaya na, Yah Taheer ina matuqar Son ka amma a matsayin yaya na, da ace ba Aunty Fateema ko ba na maka so irin na soyayya, zan aure ka, saboda ban ga wani abun kushewa a tare da kai ba, amma ba zan taba iya auren mijin auty Fateema ba, ana barin halal dan kunya in ji bahaushe, jin ta ni kai kamar uwa daya Uba daya muke da ita, dan Allah Yah Taheer ka yi hankuri, wannan maganar ba mai yiwa bace"
Kalaman ta sun masa zafi a zuciya, amma ya fuskanci abinda take nufi, ta kuma fad'a masa iyakar gaskiyar ta, ba boye boye, ya ji dad'in yanda suka fahimci juna shi da ita, ko ba komai magana bata je wajen Oga ba, ballanta zumuncin da aka fara ya rushe, ko kuma ya qara kulluwa.
"Na fahimce ki, kuma na gode da hwada min gaskiya da kin ka yi, baki boye ba,amma dai ke san ya zama dole ki hidda miji ko? Dan kuwa girma d'ai ki kai, bai kamata ace har yanzu ba ki da wanda ki ke so ba"
Rufe fuskar ta tayi, shi kuma ya na kallon ta, da wani irin yanayin da bai san ya zai fassara shi ba, ya sani ba hurumin shi bane, amma tunda shi be samu ba, bari ya taya Sultan campaign,
"Ya kin ka ruhe huska? Ki dauke ni kamar Aunty Fateema, ki sanar da ni ,ko dai can Kano mun yi suruki na?"
Da sauri ta bude ido ta na kada kai alamar ah ah.
"To a ina ne?"
"Yah Taheer ni kunya nake ji"
Sake rufe fuskar ta tayi, sannan ta juya bayan ta,
"To ko na kira maki fateema ne sai ki sanar da ita, ko kuma na kira Oga shi kenan ma bari na kira Oga"
Miqewa ya yi kamar zai fita, da sauri ta juya ta ce,
"Yah Sultan na ke so"
Taheer ji ya yi kamar ta soka masa wuqa a qahon zuciya, ya jima a tsaye bai juya ba,ita ma ta na can tsaye ta rufe fuska cikin jin kunya, Taheer kuwa cikin ran shi ya ce,
'shegen yaro ya yi nasarar sace Mata zuciya ba tare da ya sha wahala ba,'
A zahiri kuwa cewa ya yi,
"Lallai na taya ki murnar samun saurayi nagari, amma kina ganin shi ya na son ki?"
Ya fadi haka ne dan ya ji me za ta ce,zama ta yi ta tankwashe qafar ta, ta tura baki, cikin shagwaba ta ce,
"Yah Taheer ba zai taba so na ba, ni na sani, kar ka manta hwa ni diyan tallaka nike, shi kuwa mahaifan shi manya na,sannan yarinya nike qarama, kuma ka san dai yanda ya waye, ya yi karatu a qasar waje ba zai auri baqar mace kamar ni ba, shi ya sa ma tun sanda na fara ganin shi, na ji ina son shi nake addu'a Allah ya zaba min abinda shike alkhairi"
"Ba zan so sanar dake wani sirri ba, amma ina maki hwatan alkhairi, sannan ina miki albishir da samun kyakkyawar kyauta kahin ta riske ki"
Cikin rudanin da ya jefa ta da kalaman shi ta kalle shi, ta ce,
"Yah Taheer mi ka ke nuhi?"
"Babu komi, lokaci zai sanar dake komai, bari na tai na hwara shiri, gobe zan koma"
Sabo turken wawa, tabbas Mubaraka ta ji dad'in zama da su Taheer,dan haka sai ta ji wata kewar shi mai girma ta mamaye zuciyar ta, nan da nan idanun ta suka fara zubar da hawaye,
"Yah Taheer ba na so ka koma ka barmu, dama ka dawo da su Aunty Fateema nan garin,"
"Ki dena kuka dan Allah, yanzu Oga yaggane ki ki na kuka ai bone ya ci ni,kar ki damu kuma, za mu zanka zuwa akai akai,ga waya, duk dai, ai ba a rabu ba, bari in tai na sanar da oga batun tahiya ta gobe"
"To Yah Taheer, Allah ya kaimu goben, bari na hada maka saqo ka kaiwa yarana"
"To shi kenan, sai da swahe,"
"Allah shi kai mu"
Daga nan dakin Oga ya je ya kwankwasa ya jima tsaye kafin a bude, a nan ya sanar da Oga duk tattaunawar da sukai da Mubaraka, amma bai fada masa maganar ta na son Sultan ba,sannan ya sanar da shi tafiyar shi a gobe,Lawwali ma ya so a ce ta amince da Taheer, dan ya na son Taheer a duk yaran shi,amma tunda mubaraka ta ce bata yi, ba zai tursasa ta ba, duk abinda take so shi ma shi yake so.
Daga nan dakin Sultan ya nufa, zaune ya gan shi saman sallaya, da alama sallah ya idar, ko kuma karatun Alkur'ani, sallama suka yi wa junan su, sannan Taheer ya samu waje ya zauna.
"Sultan ni hwa gobe zan koma Kano, saboda na gabatar da kai na wajen Mubaraka, ta ce bata yi,ban ga ta zama ba, zan koma ga iyali na,na zo ne na maka sallama, kuma na baka shawara, ka gaggauta sanar da Mubaraka soyayyar ka, dan kuwa yarinya ce, daga sanda kun ka bar dajin ga ta shiga gari, ta samu wani, sai dai na zo maka Jaje,"
Siririyar dariya Sultan ya yi, sannan ya ce,
"Kar ka damu, in shaa Allahu ka na daga cikin manyan abokan ango, na gode da shawarar ka, Allah kuma ya sa haka shi ne yafi alkhairi, Allah shi maida ka gida lahiya"
"Ameen, na gode, sai da swahe"
"Allah ya tashe mu lahiya"
Bayan fitar Taheer daki ya koma, ya gyara kayan shi,Sultan kuwa kasa kwanciya ya yi, ya rasa ta ya zai ya tunkari Mubaraka da maganar soyayya, shi dai be taba budurwa ba, bai san ya ze yi ba, ko Sultana zai sa ta sanar da ita? Kaiii inaa, ko Lawwali zai gaya wa direct??
Mubaraka ita ma da tunanin Sultan ta kwana cikin ran ta, tun daga ranar da suka fara zuwa ta ɗora idon ta akan shi, ta ga ya qara haske, da kwarjini, akan sanin da ta masa a baya, sai ta ji qaunar shi ta kama ta, amma haka ta daure bata nuna ba, kasancewar ta sa wa ran ta cewa ya fi qarfin ta.
Amma daga baya ta ga wasu alamu da ke mata nuni da cewa wataqila shi ma ya na son ta, duk da dai ba ta tabbatar ba.
********
Washegari kuwa Sultana da Murna ta tashi, da asuba ta yi wanka, ta shirya, Lawwali na ganin zumudin da take ya kira ta, ta je gaban shi, ta na dariya, zama yayi ya na nannade hannun rigar shi, wanda hakan ya zamar masa kamar wata al'ada,
"Shin ba ki bari a d'aura auren su Barira sannan ku tai?"
Dafe goshin ta ta yi, sannan ta ce,
"Kashhh, ka ko ga na mance wallah, qarhe goma kacce limaman da kun ka samo za a kawo su ko? To wa zai tsaya a matsayin waliyyin su Bariran?"
"Wai yaran ga sun ce ni suka so, ni Ko ban san wad-da ake ba, kunya suke son bani cikin mutane"
Dariya sosai Sultana ke yi, saboda yanda ta ga damuwa sosai a fuskar shi, to shi daurin auren wata ibada ce me wahala? An bayar na karba ne fa, tsokanar shi ta dinga yi, ya na daure fuska, dan shi da gaske yake bai san ya ake yi ba.
Da misalin bakwai daidai, matasan suka shiga gari, dan shigo da Limamai guda biyar da suka roqa arziki, za su daura musu aure, cikin rashin sanin ina za a je limaman suka amince, sai da aka dakko hanya suka ga ana nausawa daji hankulan su ya tashi.
Wasu masu raunin zuciyar har da kuka.
Ko da aka iso, suka ga waje masha Allah, an gyare shi, ya yi tass, kowa cikin kwalliya mazan da matan, ga abinci da abun sha, sai hankula su ya fara kwanciya, amma sun dasa wa zuqatan su ayar tambayar me ya kawo mutane cikin wannan surquqin daji?
Kamar yanda Lawwali ya ce, da misalin qarfe goma na safiya, aka daura auren mutum goma sha huɗu,a kan sadaki dubu talatin talatin.
"Yah Taheer lafiya dai ko?"
"Lahiya qalou Mubaraka, sai dai abinda na ke tahe da shi, shi na iya jaddada zaman lahiya ko samar da rashin ta"
Cike da mamakin kalaman shi ta miqe ta daura zani a saman qaramin wandon dake jikin ta, Taheer kuwa ko irin d'an kauda kan nan, ta na gama daurawa ta zauna a bakin katifar dakin, ta bashi dukkan nutswar ta, dan sauraran abinda ya ke tafe da shi,
"Mubaraka, kin sani, na dauke ki kamar qauna ta ko?"
Daga kan ta tayi, cikin gasgata maganar shi,
"Mubaraka son da ni kai miki a matsayin qauna, ya rikid'e ya koma soyayyar da na ke hwatan ta kai mu ga yin aure, amma har sai kin amince, zan sanar da Oga da Fateema, amma in ki ka tabbatar min da baki so na, gobe zan koma Kano, na hakura da ke har abada"
Wani irin nauyi ta ji Taheer ya dora Mata akai, wanda ta rasa ma na mene ne, shin kunyar shi take ji, ko ganin rashin dacewa ya ce ya na son ta ne ya sa ta jin nauyin shi? Bakin ta na so ya fadi abinda ke zuciyar ta amma ya kasa furta komai, gyara zaman ta tayi,cikin sanya jarumta a Muryar ta ta ce,
"Yah Taheer, ba zan boye maka komai ba, dan in na boye maka ban kyauta ba, saboda matsayin da na baka na yaya na, Yah Taheer ina matuqar Son ka amma a matsayin yaya na, da ace ba Aunty Fateema ko ba na maka so irin na soyayya, zan aure ka, saboda ban ga wani abun kushewa a tare da kai ba, amma ba zan taba iya auren mijin auty Fateema ba, ana barin halal dan kunya in ji bahaushe, jin ta ni kai kamar uwa daya Uba daya muke da ita, dan Allah Yah Taheer ka yi hankuri, wannan maganar ba mai yiwa bace"
Kalaman ta sun masa zafi a zuciya, amma ya fuskanci abinda take nufi, ta kuma fad'a masa iyakar gaskiyar ta, ba boye boye, ya ji dad'in yanda suka fahimci juna shi da ita, ko ba komai magana bata je wajen Oga ba, ballanta zumuncin da aka fara ya rushe, ko kuma ya qara kulluwa.
"Na fahimce ki, kuma na gode da hwada min gaskiya da kin ka yi, baki boye ba,amma dai ke san ya zama dole ki hidda miji ko? Dan kuwa girma d'ai ki kai, bai kamata ace har yanzu ba ki da wanda ki ke so ba"
Rufe fuskar ta tayi, shi kuma ya na kallon ta, da wani irin yanayin da bai san ya zai fassara shi ba, ya sani ba hurumin shi bane, amma tunda shi be samu ba, bari ya taya Sultan campaign,
"Ya kin ka ruhe huska? Ki dauke ni kamar Aunty Fateema, ki sanar da ni ,ko dai can Kano mun yi suruki na?"
Da sauri ta bude ido ta na kada kai alamar ah ah.
"To a ina ne?"
"Yah Taheer ni kunya nake ji"
Sake rufe fuskar ta tayi, sannan ta juya bayan ta,
"To ko na kira maki fateema ne sai ki sanar da ita, ko kuma na kira Oga shi kenan ma bari na kira Oga"
Miqewa ya yi kamar zai fita, da sauri ta juya ta ce,
"Yah Sultan na ke so"
Taheer ji ya yi kamar ta soka masa wuqa a qahon zuciya, ya jima a tsaye bai juya ba,ita ma ta na can tsaye ta rufe fuska cikin jin kunya, Taheer kuwa cikin ran shi ya ce,
'shegen yaro ya yi nasarar sace Mata zuciya ba tare da ya sha wahala ba,'
A zahiri kuwa cewa ya yi,
"Lallai na taya ki murnar samun saurayi nagari, amma kina ganin shi ya na son ki?"
Ya fadi haka ne dan ya ji me za ta ce,zama ta yi ta tankwashe qafar ta, ta tura baki, cikin shagwaba ta ce,
"Yah Taheer ba zai taba so na ba, ni na sani, kar ka manta hwa ni diyan tallaka nike, shi kuwa mahaifan shi manya na,sannan yarinya nike qarama, kuma ka san dai yanda ya waye, ya yi karatu a qasar waje ba zai auri baqar mace kamar ni ba, shi ya sa ma tun sanda na fara ganin shi, na ji ina son shi nake addu'a Allah ya zaba min abinda shike alkhairi"
"Ba zan so sanar dake wani sirri ba, amma ina maki hwatan alkhairi, sannan ina miki albishir da samun kyakkyawar kyauta kahin ta riske ki"
Cikin rudanin da ya jefa ta da kalaman shi ta kalle shi, ta ce,
"Yah Taheer mi ka ke nuhi?"
"Babu komi, lokaci zai sanar dake komai, bari na tai na hwara shiri, gobe zan koma"
Sabo turken wawa, tabbas Mubaraka ta ji dad'in zama da su Taheer,dan haka sai ta ji wata kewar shi mai girma ta mamaye zuciyar ta, nan da nan idanun ta suka fara zubar da hawaye,
"Yah Taheer ba na so ka koma ka barmu, dama ka dawo da su Aunty Fateema nan garin,"
"Ki dena kuka dan Allah, yanzu Oga yaggane ki ki na kuka ai bone ya ci ni,kar ki damu kuma, za mu zanka zuwa akai akai,ga waya, duk dai, ai ba a rabu ba, bari in tai na sanar da oga batun tahiya ta gobe"
"To Yah Taheer, Allah ya kaimu goben, bari na hada maka saqo ka kaiwa yarana"
"To shi kenan, sai da swahe,"
"Allah shi kai mu"
Daga nan dakin Oga ya je ya kwankwasa ya jima tsaye kafin a bude, a nan ya sanar da Oga duk tattaunawar da sukai da Mubaraka, amma bai fada masa maganar ta na son Sultan ba,sannan ya sanar da shi tafiyar shi a gobe,Lawwali ma ya so a ce ta amince da Taheer, dan ya na son Taheer a duk yaran shi,amma tunda mubaraka ta ce bata yi, ba zai tursasa ta ba, duk abinda take so shi ma shi yake so.
Daga nan dakin Sultan ya nufa, zaune ya gan shi saman sallaya, da alama sallah ya idar, ko kuma karatun Alkur'ani, sallama suka yi wa junan su, sannan Taheer ya samu waje ya zauna.
"Sultan ni hwa gobe zan koma Kano, saboda na gabatar da kai na wajen Mubaraka, ta ce bata yi,ban ga ta zama ba, zan koma ga iyali na,na zo ne na maka sallama, kuma na baka shawara, ka gaggauta sanar da Mubaraka soyayyar ka, dan kuwa yarinya ce, daga sanda kun ka bar dajin ga ta shiga gari, ta samu wani, sai dai na zo maka Jaje,"
Siririyar dariya Sultan ya yi, sannan ya ce,
"Kar ka damu, in shaa Allahu ka na daga cikin manyan abokan ango, na gode da shawarar ka, Allah kuma ya sa haka shi ne yafi alkhairi, Allah shi maida ka gida lahiya"
"Ameen, na gode, sai da swahe"
"Allah ya tashe mu lahiya"
Bayan fitar Taheer daki ya koma, ya gyara kayan shi,Sultan kuwa kasa kwanciya ya yi, ya rasa ta ya zai ya tunkari Mubaraka da maganar soyayya, shi dai be taba budurwa ba, bai san ya ze yi ba, ko Sultana zai sa ta sanar da ita? Kaiii inaa, ko Lawwali zai gaya wa direct??
Mubaraka ita ma da tunanin Sultan ta kwana cikin ran ta, tun daga ranar da suka fara zuwa ta ɗora idon ta akan shi, ta ga ya qara haske, da kwarjini, akan sanin da ta masa a baya, sai ta ji qaunar shi ta kama ta, amma haka ta daure bata nuna ba, kasancewar ta sa wa ran ta cewa ya fi qarfin ta.
Amma daga baya ta ga wasu alamu da ke mata nuni da cewa wataqila shi ma ya na son ta, duk da dai ba ta tabbatar ba.
********
Washegari kuwa Sultana da Murna ta tashi, da asuba ta yi wanka, ta shirya, Lawwali na ganin zumudin da take ya kira ta, ta je gaban shi, ta na dariya, zama yayi ya na nannade hannun rigar shi, wanda hakan ya zamar masa kamar wata al'ada,
"Shin ba ki bari a d'aura auren su Barira sannan ku tai?"
Dafe goshin ta ta yi, sannan ta ce,
"Kashhh, ka ko ga na mance wallah, qarhe goma kacce limaman da kun ka samo za a kawo su ko? To wa zai tsaya a matsayin waliyyin su Bariran?"
"Wai yaran ga sun ce ni suka so, ni Ko ban san wad-da ake ba, kunya suke son bani cikin mutane"
Dariya sosai Sultana ke yi, saboda yanda ta ga damuwa sosai a fuskar shi, to shi daurin auren wata ibada ce me wahala? An bayar na karba ne fa, tsokanar shi ta dinga yi, ya na daure fuska, dan shi da gaske yake bai san ya ake yi ba.
Da misalin bakwai daidai, matasan suka shiga gari, dan shigo da Limamai guda biyar da suka roqa arziki, za su daura musu aure, cikin rashin sanin ina za a je limaman suka amince, sai da aka dakko hanya suka ga ana nausawa daji hankulan su ya tashi.
Wasu masu raunin zuciyar har da kuka.
Ko da aka iso, suka ga waje masha Allah, an gyare shi, ya yi tass, kowa cikin kwalliya mazan da matan, ga abinci da abun sha, sai hankula su ya fara kwanciya, amma sun dasa wa zuqatan su ayar tambayar me ya kawo mutane cikin wannan surquqin daji?
Kamar yanda Lawwali ya ce, da misalin qarfe goma na safiya, aka daura auren mutum goma sha huɗu,a kan sadaki dubu talatin talatin.