Sashe 43
A Garin Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Baki Sultan ya sake kawai ya na mamaki, ya na namiji amma ana so a masa auren dole, to ba ma wannan ba, in an masa auren dole ya hakura tunda dama baida budurwar da ta kwanta masa ga rai, to ita sultana da ke son Lawwali fa?
"Hajiya na amince ku aura min duk wadda kuka so, amma fa ba zan amince ku aura wa sultana mutunin da bata qauna ba"
"To Uban mu, mun jiya, in an tashi auren sai ka hana,...dalla fita ka ban waje, yau so kuke sai kun batan duk wani farin ciki da nake ciki na ga alama"
Daddy ne ya shiga dakin bakin nan kamar gonar audiga, cikin, farin ciki ya ce ma Sultan,
"Ku shirya kai da qaunar ka gobe akwai party, around 1am, kwana za a yi ana murnar samun nasara, diyoyin gwamnoni ne suka partyn a Abuja, na san za ku buqaci kudi sosai, dan kusan kowa a wajen ya na taqama da uba nai, ga wannan, ku dauki duk nawa ya muku"
Wani dan kati ya miqa masa,wanda yake a matsayin makullin ma'ajiyar kudin Gwamnan, kallo kawai Sultan ya bisu da shi,ya kasa cewa komai, da kyar ya bude baki ya ce,
"Yaushe ku ka zama haka? Yaushe kuka dena damuwa da abinda muke so sai wanda kuke so? Yaushe za ku saki duniya, ku kama qiyama?"
Daddy bai fahimci ina Sultan ya dosa ba, ita da ta san akan me yake magana, tuni ta miqe, ta na son kawar da zancen Sultan ya sa kai ya bar dakin.
"Kwantar da hankalin ka ka jiya diyan ga in ka ce kabi nasu to fa ruwa ma sai an tauna musu an hadiye musu tsabar gata"
"Amma mi an kai mai ? Ban taba ganin Sultan ya yi hushi haka ba,mi kin kai mai? Ki hwadi min gaskiya ko inna bincika na gano kin masa wani abu ran ki zai ɓaci, ban hada d'iya na da kowa ba"
"Ni kuma ni na haihe su , har da ka ke hwadi min baka hada d'iyan ka da kowa ba, maganar wannan yaron driver ne taqi qarewa gidan ga, ya zo ya na wani hwadin magana yanda ya ga dama, to shi kan shi na sanar masa magana diyar Minister , shi na yake hushi "
Shiru ya yi bai ce komai ba, ya fita ya bar dakin, bai tsaya a ko ina ba sai dakin Sultana, ta na bathroom, ta na alwala, sai da ta gama ta fito taga wayar ta a hannun shi, ya na duddubawa, har ta isa gaban shi bai aje wayar ba sai da ya gama abinda yake.
"Sultana da dukkan alamu ki na son Lawwali, amma Sultana ki sani, ke baki san waye Lawwali ba, ni na san waye shi, ina mai baki shawara da ki hakura da shi, tun da wuri, tun lokaci bai qure miki ba"
"Daddy kenan, indai Hajiya ta ji ta gani, ta ke zaune da kai, banga dalilin da zai sa ni na kasa auren driver na ba"
Cikin rashin fahimta ya ce,
"Me ki ke nufi? Sultana yaushe kin ka hwara magana irin wannan? Me ki ke nufi da abinda kin ka hwadi yanzu?"
"Never mind Daddy, ina so nayi sallah, pls"
"Sultana ina son sanin damuwar ki, talk to ur Daddy Sulty Baby, ki sanar da ni mi ki ka so"
Cikin kuka ta ce,
"Daddy ka tambayi Hajiya, ta san komai, dan Allah ka barni na gana da Ubangiji na, shi ne kaɗai zai min maganin damuwa ta, Hajiya ta tabbatar min da ba zan samu me nake so wajen ku ba, yanzu ka tabbatar min da na hakura da farin ciki na, saboda bai muku ba, bai yi daidai da abinda kuke so ba, ni Auwal nike so, ba wani shugaban qasa ba,"
Daddyn su ne ya ja ta jikin shi ya na lallashi, a zuciyar shi kuwa ya na mamakin sanda ya yi sake Lawwali ya yi nasarar dasa soyayyar shi a zuciyar sultana haka, sai yanzu yake tunawa da alamomin da Hajiya ke sanar da shi, lallai ya yi sake, Lawwali na shirin yi masa babbar illa, indai har ta nan ya biyo.
"Ya isa kukan haka nan, zan yi tunani akan maganar, ki daina kuka"
Da sauri ta kalle shi, ta na son tabbtar da gaskiyar maganar shi, dan yanzu gaba daya ta cire yarda a tsakanin su, gani take komai nasu qarya ne.
Sai da ya ga ta daina kukan ya bar dakin, wajen Hajiya Ikee ya koma, ta na zaune ta zabga uban tagumi ta na tunanin yanda za ta raba tsakanin Lawwali da sultana.
"Ki na da gaskiya ashe da kin ka ce na kori yaron nan daga gidan nan naqi ji, ashe ya min babbar illa ina zaune ba tare da na sani ba?"
Kamar an sosa mata inda ke mata qaiqayi haka ta miqe, kallon lokaci ta yi, ta ga ya tafi sosai, ta gaji tilis, kuma maganar nan na buqatar dogon nazari, ko kadan ba ta son batawa Sultana, amma dole ne ta raba tsakanin su da Lawwali.
"Wannan magana ta riga ta wuce, yanzu mafita za ka nemo mana, dan kuwa ba zan taba yarda diyar ciki na ta auri driver ba, yau ko min muqamin da za ka damqa masa a gwamnati walle ba ya hanawa a kire shi da driver, ba zan zama abin dariya cikin abukkai ba,dole ka dau mataki"
"Ba zaki gane ba, yanzu raba tsakanin sultana da Lawwali babbar musiba ce wallah, duk yanda zan miki bayanin yaron nan ba zaki gane ba, ni na san wane ne Lawwali,"
"Driver din? Me ye ba zan gane ba? Yau muke tare, ka kore shi kawai, shi bar gidan"
Bai ce mata komai ba ya fada bathroom.
Mita ta dunga yi tare da fadin ya sa yaron shi din nan da ke masa aiki, a sace Lawwalin ya bar doron qasa baki daya, Indai ze zame musu fitina akan dukkan tsarin su.
*************************
Sai guje guje suke abin su a katafaren tsakar gidan kakannin nasu, cike da nishad'i da jin dadi, ita kan ta Hajiyar Hansatu rabon ta da fitowa farfajiyar gidan haka ta manta, Hansatu na ta tuna yarintar ta, zaune suke a saman kujeru na qarfe masu matuqar kyau, gaban su table ne an aje fruits da abin sha, su na ta hira a tsakanin su, wanda ya san Hansatu sati Uku da suka wuce ya gan ta yanzu ba zai gane ta ba, ta ciko ta murmure, ga wani haske da ta yi, in ta saka riga da skirt sai ta cike su famm, ban taba zaton hansatu na da shape haka ba sai yanzu.
Hajiya ce ta kalle ta ta ce,
"Gaskiya ya kamata a sauya maki waya, yanzu da yar wayar nan ta zamani ake hira da miji, sai ku yi chatting din ku kamar ku na tare, haka naga Yayan ki na yi da waccan maras kunyar da ta qi dawowa, amma fa soyayya a waya kamar Juliet,"
"Hajiya wai mi an kai mata ne haka?"
"Wannan fa baki gane alqiblar ta, dan yanzu ko an ce mi yayi mata bata hwadi, ta na can qasar waje, da alama can taka so su koma da zama, tunda can ta yi rayuwar ta, ni kuwa ba me d'auke min yaro shi tai wata uwa duniya"
"Ohhh amma ko bata kyauta ba gaskiya, ai mace hankuri aka santa da shi a gidan miji, ba irin wanga hali ba"
"Haka ne, ita kam sam bata san wannan ba, komi so takai ayi yanda taka so, ba ko shi yiwa,"
"Allah to ya shirya ta, ya sa ta dawo su ci gaba da zaman su lahiya,"
"Ameen dai"
Su na tsaka da hira Hajiya ta dauki waya, ta kira Yayan Hansatu, tace ya aiko mata da waya mai kyau, kafin Hansatu ta wuce, amsawa ya yi, da toh, sanan suka yi sallama.
Hansatu bata koma gida ba kuwa sai da dalleliyar waya mai kyau, ba ta wani murna da wayar kawai dai ta nuna ta na murna ne, domin kuwa wanda ake mata kwadayin su yi hirar da shi, tunda ya tafi sai dai taji labari wajen Hajiya sun yi waya, amma baya kiran ta, balle ta samu No shi, kuma ita ba zata iya tambayar hajiyar ta No isah ba.
Ko a mota ajiye kwalin wayar kawai ta yi a cinyar ta ta na tunani, ga dai shi ya tafi, kuma ya fadawa Hajiya kasuwancin goro yayi albarka, amma ko sisi bai masu aike ba, bata san ranar dawowar shi ba.
A qofar gidan su motar ta tsaya, fitowa suka yi ita da yaran, kowa ya gan su ya ga jikokin masu azziqi, hatta da takalmin su yanzu mai tsada suke sakawa.
Ko kallon majalisar su 'yabbuga bata yi ba, ballantana ta ga yanda suka sanya mata ido su na gulmar ta.
Sallama ta yi da driver suka shige gida.
Can majalisar su Lamishi kuwa banda gulmar su ba abinda suka ke.
"Hummmm wagga ai ni zan baki labarin Hansatu ta sauya, bari dai, ai za su koma yar gidan jiya ne, ta na zuwa roqon abu zan mata kaca-kaca, yanzu ta koyi walaqanci,ko kallo bamu ishe ta ba,dan ta hwara daura suhwa, da holan, walle ta na barin shi"
"Ohhh ke kuwa me ya sa kin ka ce haka? Ai ba kin mata hwatan komawa gidan jiya ba, indai ta sha wahala yanda kun ka ce"
'Yabbuga ce ta kalli Asshibi a sheqe ta ce,
"Na hwadi, na ce na hwadi baki ganin wani kallon walaqanci da takai wa mutane?"
"Ai kuwa ko kallon wajen ga ma bata yi ba"
"Tauuu PA din Hansatu, ko zuwa zaki ki hwadi mata mi nicce?"
Lamishi da ta zabga tagumi ta na tunanin shin duniya ina Mubaraka ta shiga ne, ta ce,
"Dan Allah ku bar yi mana hayaniyar ga, wadda ku ka yi domin ita bata san ku na yi ba, ni abinda ya ishe ni ya dameni"
"In baki so ki ji mi muka hwadi tai garkar ki, nan garka ta ta wallah"
(in bakya so ki ji me muke cewa je ki gidan ki, nan gida na ne)
"Hajiya na amince ku aura min duk wadda kuka so, amma fa ba zan amince ku aura wa sultana mutunin da bata qauna ba"
"To Uban mu, mun jiya, in an tashi auren sai ka hana,...dalla fita ka ban waje, yau so kuke sai kun batan duk wani farin ciki da nake ciki na ga alama"
Daddy ne ya shiga dakin bakin nan kamar gonar audiga, cikin, farin ciki ya ce ma Sultan,
"Ku shirya kai da qaunar ka gobe akwai party, around 1am, kwana za a yi ana murnar samun nasara, diyoyin gwamnoni ne suka partyn a Abuja, na san za ku buqaci kudi sosai, dan kusan kowa a wajen ya na taqama da uba nai, ga wannan, ku dauki duk nawa ya muku"
Wani dan kati ya miqa masa,wanda yake a matsayin makullin ma'ajiyar kudin Gwamnan, kallo kawai Sultan ya bisu da shi,ya kasa cewa komai, da kyar ya bude baki ya ce,
"Yaushe ku ka zama haka? Yaushe kuka dena damuwa da abinda muke so sai wanda kuke so? Yaushe za ku saki duniya, ku kama qiyama?"
Daddy bai fahimci ina Sultan ya dosa ba, ita da ta san akan me yake magana, tuni ta miqe, ta na son kawar da zancen Sultan ya sa kai ya bar dakin.
"Kwantar da hankalin ka ka jiya diyan ga in ka ce kabi nasu to fa ruwa ma sai an tauna musu an hadiye musu tsabar gata"
"Amma mi an kai mai ? Ban taba ganin Sultan ya yi hushi haka ba,mi kin kai mai? Ki hwadi min gaskiya ko inna bincika na gano kin masa wani abu ran ki zai ɓaci, ban hada d'iya na da kowa ba"
"Ni kuma ni na haihe su , har da ka ke hwadi min baka hada d'iyan ka da kowa ba, maganar wannan yaron driver ne taqi qarewa gidan ga, ya zo ya na wani hwadin magana yanda ya ga dama, to shi kan shi na sanar masa magana diyar Minister , shi na yake hushi "
Shiru ya yi bai ce komai ba, ya fita ya bar dakin, bai tsaya a ko ina ba sai dakin Sultana, ta na bathroom, ta na alwala, sai da ta gama ta fito taga wayar ta a hannun shi, ya na duddubawa, har ta isa gaban shi bai aje wayar ba sai da ya gama abinda yake.
"Sultana da dukkan alamu ki na son Lawwali, amma Sultana ki sani, ke baki san waye Lawwali ba, ni na san waye shi, ina mai baki shawara da ki hakura da shi, tun da wuri, tun lokaci bai qure miki ba"
"Daddy kenan, indai Hajiya ta ji ta gani, ta ke zaune da kai, banga dalilin da zai sa ni na kasa auren driver na ba"
Cikin rashin fahimta ya ce,
"Me ki ke nufi? Sultana yaushe kin ka hwara magana irin wannan? Me ki ke nufi da abinda kin ka hwadi yanzu?"
"Never mind Daddy, ina so nayi sallah, pls"
"Sultana ina son sanin damuwar ki, talk to ur Daddy Sulty Baby, ki sanar da ni mi ki ka so"
Cikin kuka ta ce,
"Daddy ka tambayi Hajiya, ta san komai, dan Allah ka barni na gana da Ubangiji na, shi ne kaɗai zai min maganin damuwa ta, Hajiya ta tabbatar min da ba zan samu me nake so wajen ku ba, yanzu ka tabbatar min da na hakura da farin ciki na, saboda bai muku ba, bai yi daidai da abinda kuke so ba, ni Auwal nike so, ba wani shugaban qasa ba,"
Daddyn su ne ya ja ta jikin shi ya na lallashi, a zuciyar shi kuwa ya na mamakin sanda ya yi sake Lawwali ya yi nasarar dasa soyayyar shi a zuciyar sultana haka, sai yanzu yake tunawa da alamomin da Hajiya ke sanar da shi, lallai ya yi sake, Lawwali na shirin yi masa babbar illa, indai har ta nan ya biyo.
"Ya isa kukan haka nan, zan yi tunani akan maganar, ki daina kuka"
Da sauri ta kalle shi, ta na son tabbtar da gaskiyar maganar shi, dan yanzu gaba daya ta cire yarda a tsakanin su, gani take komai nasu qarya ne.
Sai da ya ga ta daina kukan ya bar dakin, wajen Hajiya Ikee ya koma, ta na zaune ta zabga uban tagumi ta na tunanin yanda za ta raba tsakanin Lawwali da sultana.
"Ki na da gaskiya ashe da kin ka ce na kori yaron nan daga gidan nan naqi ji, ashe ya min babbar illa ina zaune ba tare da na sani ba?"
Kamar an sosa mata inda ke mata qaiqayi haka ta miqe, kallon lokaci ta yi, ta ga ya tafi sosai, ta gaji tilis, kuma maganar nan na buqatar dogon nazari, ko kadan ba ta son batawa Sultana, amma dole ne ta raba tsakanin su da Lawwali.
"Wannan magana ta riga ta wuce, yanzu mafita za ka nemo mana, dan kuwa ba zan taba yarda diyar ciki na ta auri driver ba, yau ko min muqamin da za ka damqa masa a gwamnati walle ba ya hanawa a kire shi da driver, ba zan zama abin dariya cikin abukkai ba,dole ka dau mataki"
"Ba zaki gane ba, yanzu raba tsakanin sultana da Lawwali babbar musiba ce wallah, duk yanda zan miki bayanin yaron nan ba zaki gane ba, ni na san wane ne Lawwali,"
"Driver din? Me ye ba zan gane ba? Yau muke tare, ka kore shi kawai, shi bar gidan"
Bai ce mata komai ba ya fada bathroom.
Mita ta dunga yi tare da fadin ya sa yaron shi din nan da ke masa aiki, a sace Lawwalin ya bar doron qasa baki daya, Indai ze zame musu fitina akan dukkan tsarin su.
*************************
Sai guje guje suke abin su a katafaren tsakar gidan kakannin nasu, cike da nishad'i da jin dadi, ita kan ta Hajiyar Hansatu rabon ta da fitowa farfajiyar gidan haka ta manta, Hansatu na ta tuna yarintar ta, zaune suke a saman kujeru na qarfe masu matuqar kyau, gaban su table ne an aje fruits da abin sha, su na ta hira a tsakanin su, wanda ya san Hansatu sati Uku da suka wuce ya gan ta yanzu ba zai gane ta ba, ta ciko ta murmure, ga wani haske da ta yi, in ta saka riga da skirt sai ta cike su famm, ban taba zaton hansatu na da shape haka ba sai yanzu.
Hajiya ce ta kalle ta ta ce,
"Gaskiya ya kamata a sauya maki waya, yanzu da yar wayar nan ta zamani ake hira da miji, sai ku yi chatting din ku kamar ku na tare, haka naga Yayan ki na yi da waccan maras kunyar da ta qi dawowa, amma fa soyayya a waya kamar Juliet,"
"Hajiya wai mi an kai mata ne haka?"
"Wannan fa baki gane alqiblar ta, dan yanzu ko an ce mi yayi mata bata hwadi, ta na can qasar waje, da alama can taka so su koma da zama, tunda can ta yi rayuwar ta, ni kuwa ba me d'auke min yaro shi tai wata uwa duniya"
"Ohhh amma ko bata kyauta ba gaskiya, ai mace hankuri aka santa da shi a gidan miji, ba irin wanga hali ba"
"Haka ne, ita kam sam bata san wannan ba, komi so takai ayi yanda taka so, ba ko shi yiwa,"
"Allah to ya shirya ta, ya sa ta dawo su ci gaba da zaman su lahiya,"
"Ameen dai"
Su na tsaka da hira Hajiya ta dauki waya, ta kira Yayan Hansatu, tace ya aiko mata da waya mai kyau, kafin Hansatu ta wuce, amsawa ya yi, da toh, sanan suka yi sallama.
Hansatu bata koma gida ba kuwa sai da dalleliyar waya mai kyau, ba ta wani murna da wayar kawai dai ta nuna ta na murna ne, domin kuwa wanda ake mata kwadayin su yi hirar da shi, tunda ya tafi sai dai taji labari wajen Hajiya sun yi waya, amma baya kiran ta, balle ta samu No shi, kuma ita ba zata iya tambayar hajiyar ta No isah ba.
Ko a mota ajiye kwalin wayar kawai ta yi a cinyar ta ta na tunani, ga dai shi ya tafi, kuma ya fadawa Hajiya kasuwancin goro yayi albarka, amma ko sisi bai masu aike ba, bata san ranar dawowar shi ba.
A qofar gidan su motar ta tsaya, fitowa suka yi ita da yaran, kowa ya gan su ya ga jikokin masu azziqi, hatta da takalmin su yanzu mai tsada suke sakawa.
Ko kallon majalisar su 'yabbuga bata yi ba, ballantana ta ga yanda suka sanya mata ido su na gulmar ta.
Sallama ta yi da driver suka shige gida.
Can majalisar su Lamishi kuwa banda gulmar su ba abinda suka ke.
"Hummmm wagga ai ni zan baki labarin Hansatu ta sauya, bari dai, ai za su koma yar gidan jiya ne, ta na zuwa roqon abu zan mata kaca-kaca, yanzu ta koyi walaqanci,ko kallo bamu ishe ta ba,dan ta hwara daura suhwa, da holan, walle ta na barin shi"
"Ohhh ke kuwa me ya sa kin ka ce haka? Ai ba kin mata hwatan komawa gidan jiya ba, indai ta sha wahala yanda kun ka ce"
'Yabbuga ce ta kalli Asshibi a sheqe ta ce,
"Na hwadi, na ce na hwadi baki ganin wani kallon walaqanci da takai wa mutane?"
"Ai kuwa ko kallon wajen ga ma bata yi ba"
"Tauuu PA din Hansatu, ko zuwa zaki ki hwadi mata mi nicce?"
Lamishi da ta zabga tagumi ta na tunanin shin duniya ina Mubaraka ta shiga ne, ta ce,
"Dan Allah ku bar yi mana hayaniyar ga, wadda ku ka yi domin ita bata san ku na yi ba, ni abinda ya ishe ni ya dameni"
"In baki so ki ji mi muka hwadi tai garkar ki, nan garka ta ta wallah"
(in bakya so ki ji me muke cewa je ki gidan ki, nan gida na ne)