Sashe 56
A Garin Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kwantawa ya yi ya na kallon sama, tunanin iyayen shi yake yi, a rayuwa shi dai ba shi da sa'a, wai ace ya na da iyaye a cikin garin Zamfara, amma kamar ba shi da kowa, ba wanda ya ke da kusanci da shi, da zuciyar shi, balle ya ji damuwar shi, ba wanda ya damu da rayuwar shi,tunawa ya yi da sanda ya kai musu maganar auren, kafin ya fita daga gidan ya na dakin shi, ya ji mata na ta shiga ana fita, ana yi wa Lamishi Barka, d'an ta zai auri diyar gwamna, wa ya je ya baza a unguwar sai Allah masani.
Gaba daya basu damu da wai bari a bincika a ga mene ne dalilin yin auren ba, farin cikin su kawai dan su zai auri yar gwamna, ba komai, Allah dai ya kai mu biki lafiya.
Tunani ya dinga yi, na me ya rage a bikin wanda yake haqqin shi ne bai ba? Domin hatta da lefe da ya yi wa Sultana maganar shi, cewa ta yi ba sai ya yi ba, Hajiya Ikee kuwa ta ce bata san zance ba, ba a ɗauke masa lefe ba, sai ya yi, duk abinda ake buqata, dan haka kudin kawai ya tura ta account din Hajiya Ikee, ya ce su sai duk abinda ya kamata, ganin mahaukatan kudin sun rudar da Hajiya Ikee, amma bata yi mamaki ba, duba da wa ya tsaya masa a garin, ba qananan kudi yake samu ba a wajen Gwamna, Hajiya ta dau alqawarin ita zata kula da lefe, to amma ya rasa dalilin da ya sa yake neman dalilin da zai kai shi gidan su Sultana, ya na so ya sanya ta a idanun shi, zuciyar shi na azalzalar shi ta na tunzira shi akan ya je ya gan ta, daya bangaren na zuciyar shi na kwabar shi, bai biye wa daya daga cikin su ba, ko da ya fita ya dauki hanya, bai tsaya a ko ina ba sai gidan su.
Ko gaishe su bai ba, ya tsaya a tsaye ya ciro kudi masu uban yawa daga aljifan jikin shi, ya ajiye wa Lamishi, ya ce gashi nan su samu inda za a musu ɗinkin gaggawa in sun sai tufafin da suke so su sa a bikin, ba ya so su je masa wajen biki a hargitse.
Godiya suka dinga yi kamar za su kwanta, makullin mota ya bawa Jameelu, ya ce ya dakko wasu manyan ledoji a bayan motar, a guje ya fita ya na tsalle, ledoji ne manya masu nauyi Jameelu ya shiga da su, Dan Talo na ta bata rai ba a bashi komai ba.
Lawwali murmushin takaici ya yi, dan duk ya fahimci komai, tura leda daya gaban Dan Talo ya yi, ya ce,
"Sai ka bar bata fuska, ka sanya ranar daurin aure, kuma ka yi wanka dan Allah, kaya duk kyawun su in ba wanka ba sa kyau, Jameelu ga naku nan,ga wannan ku tai ku sai takalma da hulla, bana so ku taho wajen nan kamar almajirrai,"
"Tau Yaya mun gode"
"Kaiii wanga yaro Allah shi qaro bud'i" in ji Dan Talo.
"Addu'ar ku kenan,bud'i dai bud'i dai, to Allah shi bud'a din, ba bu ruwan ku da ta ina bud'in zai taho"
Fatali ya yi da dan karamin kwanon man gyadan da Mai Buruji ta soya, ya bar gidan, cikin takaicin iyayen nashi.
Ko da ya koma unguwar da yake zama, har zai wuce gidan shi, kawai ya tsaya, ya kira Sultana, ta na dauka ya ce,
"Ki shirya ki hito, zamu daukan hoto, ina jiran ki, nan da awa guda"
"Daukan hoto kuma? Na ko aza bai dame ka ba irin wannan abubuwan"
"Za mu yi ne dan Hajiya, ke san wadda taka son ayi komai a bayyane, hoton zai faranta ran ta"
Ta ji dadin yanda ya duba lamarin Hajiyar ta, da gaskiyar shi, hoton zai faranta ranta matuqa.
A gaggauce ta shiga wanka,ta fara shirya wa, dan bata so ta bar shi ya zauna jiran ta.
Shima gida ya wuce, ya samu ya watsa ruwa, ya yi shirin shi tsaf cikin farar shadda mai golden din aiki, ya na daga cikin dinkunan da suka siyo ready made shi da Sultana, a qalla sun siya kaya masu kyau da tsada kusan kala goma goma, a gogon shi na gold ya daura, kuma kalar aikin kayan shi (maza ku sani haramun ne namiji ya sanya agogo gold ko zoben gold sai azurfa).
Takalmin shi ma kalar aikin rigar shi, sai hula fara mai ratsin golden, Masha Allah, ko shi kan shi sai da ya jima gaban madubi ya na kallon kan shi, a fili ya bayyana cewa,
"Lawwali kenan, dan gidan Lamishi da Dan Talo, Yayan Mubaraka, Angon Sultana"
(Aunty Asma'u😆)
Murmushi ya yi, ya dauki turarukan shi ya dinga fesawa a hankali, ta yanda qamshin su ba zai hau kai ba, ya na gamawa ya taje gemun shi da ke qarawa fuskar shi kyau da kwarjini, (Team Gemu🥰)
Sai da ya rufe gidan sannan ya shige motar shi da ya bari a waje.
Ya na zuwa qofar gidan su Sultana Kiran ta na shiga wayar shi, dauka ya yi, ya ce ta fito ya na waje.
Ya na nan zaune a mota ya ga securies guda uku sun bude mata qofar, kamar hadin baki ta fito sanye da doguwar riga golden color, ta na ta walkiya a cikin duhun daren, Lawwali sakin baki ya yi ya na kallon Sultana, anyaa ita ce kuwa?
Sultana ta ji dad'in yanda Lawwali ya shagala da kallon ta, sai yanzu ta ke godewa Hajiya da ta dage sai an kawo wadda zata shirya ta, dan kuwa in ita zata shirya ba zata fito a matsayin amarya ba, dunkunan da a ka kashe makudan kudi aka yi su, a banza za a sanya su ba su yi kyawun da ake so ba.
Da sauri ya fita ya bude mata qofa, ta shiga, ta na murmushi qasa qasa.
Bayan ya zauna kafin ya tada motar,suka kalli juna, a tare suka furta,
"Ka/kin yi kyau"
Dariya suka yi, sannan Lawwali ya tada mota, sai hadadden gidan Hoton da ke cikin garin na Gusau, tun da suka shiga wajen mutane ke kallon su, domin kusan duk amaren da angwayen da suka je wajen dan d'aukan hoto Lawwali da Sultana sun fi su yin shiga mai kyau, da tsari, da burgewa.
Sai da aka gama wa mutum uku, sannan aka zo kan su, a lokacin qarfe goma na dare ta gota.
Style kala kala aka dinga nuna musu su kuwa su na kyafewa ana daukan su hoto, style din da suka ga ya sabawa shari'a in ance su yi, sai Sultana ko Lawwali d'aya daga cikin su yaqi.
A haka dai aka gama daukan su hotunan, wasu matasa ne suka gane Sultana, habaa manaa nan da nan waje ya cika da surutai kala kala, wasu na yabon ta, su na ta so a dauke su hoto da ita, wasu kuma na tsangwamar ta saboda mahaifin ta.
Lawwali bai tsaya biye wa shiririta ba, ya ja ta suka tafi gida.
Hajiya ta rude ta rikice da ta ga hotuna, ga su an tura musu ga waya, ga wasu sun taho da su a envelope,kallon Lawwali ta dinga yi daga sama har qasa, ko ba shi da arziki ya na da kyauwun huce takaici.
A cikin daren ta dinga dora hotunan a social media, qawayen ta kawai take jira su ga wannan hotunan, ta ga reaction din su akan mijin Sultanan ta.
Sultana ma ta dora hotunan a social media, musamman Instagram ,ganin yanda suka rude da kallon hotuna kamar basu da lokacin shi ne ya sanya Lawwali yin sallama da Sultan ya tafi gida.
Kayan shi ya cire ya tafi daji, domin ya na da mahimmin abu da ya ke so ya gudanar a can.................
*Biki bidiri buredeee*
💅🏻 *A GARIN MU* 💅🏻
BY HAERMEEBRAERH
PAGE 42:
Tokare take jikin gini, kamar wadda aka jingine, ta na ta dariyar yaqe, hannun ta dauke da kwano, shinkafa ce a ciki, ta sha ganyen zogale da quli, tumatur da albasa, da soyayyan mai, abincin da Lamishi ke matuqar so kenan.
"Ko ni mutan gidan ga ba su amsa sallama ne? Sai buga sallama nake tun garka shiru ka ke ji"
Lamishi ce ta fito, sanye da kayan da ta ke gwada wa, in da kudin ka yanzu za ka samu abinda ka ke nema, har sun samu ɗinkin da suka kai, guda bibbiyu, manyan leshi guda biyu atampa manya biyu, kowa d'aid'ai, sun siyo takalma da jakunkuna, sarqoqi da abun hannu, sai sabbin mayafai .
Lamishi ce ta yatsina baki ta ce,
"To wa ya ji ki mu na can mu na harikar azziqi"
"Ai fa, na ga harikar azziqi, mutumi na zai yi aure shi na ko a fad'i min, duk abin da ya faru a baya ai ke san sabanin harshe da haqori ne, to Allah shi sanya alkhairi, ni zan koma, ga gwaben shinkahwa na kawo miki, na san ki na so"
Wangale baki Lamishi ta yi, ta amshe kwano, ta gauraya gaban ta ta afa a baki, dad'in abun ne ya soki kunnen ta sai da ta sosa.
'Yabbuga na ganin haka ta saki jiki ta na zuba, ta ce wannan ta ce wancan, nan dai Lamishi ta manta da komai, suka hau hira akai ta bawa 'Yabbuga labarin abun azziqin da ke ta gudana a gidan.
"To ni dai ba wannan ba, ke dai ga bikin ga da ya taho a qurarren lokaci, ko tuwahi sabo ban dunka ba, dama ya kai wata guda ne, da na sa Dan Jumma ya sai min Holan ko Suhwa, nima na daura ana bikin Babban d'a"
Dariya suka sanya sukai shewa, tare da tafawa,
"Kar ki damu, ina nan da wata da Hajiya Ikeelima tabban, ke san su irin wannan ba shi gaban su, sai su sa sutura su ɗebe su basuwa kyauta, anjima in sun gane ta ba su ganewa "
'Yabbuga guda ta kama hanci ta zabga, ji take kamar ta jawo goben a d'aura auren,
Gaba daya basu damu da wai bari a bincika a ga mene ne dalilin yin auren ba, farin cikin su kawai dan su zai auri yar gwamna, ba komai, Allah dai ya kai mu biki lafiya.
Tunani ya dinga yi, na me ya rage a bikin wanda yake haqqin shi ne bai ba? Domin hatta da lefe da ya yi wa Sultana maganar shi, cewa ta yi ba sai ya yi ba, Hajiya Ikee kuwa ta ce bata san zance ba, ba a ɗauke masa lefe ba, sai ya yi, duk abinda ake buqata, dan haka kudin kawai ya tura ta account din Hajiya Ikee, ya ce su sai duk abinda ya kamata, ganin mahaukatan kudin sun rudar da Hajiya Ikee, amma bata yi mamaki ba, duba da wa ya tsaya masa a garin, ba qananan kudi yake samu ba a wajen Gwamna, Hajiya ta dau alqawarin ita zata kula da lefe, to amma ya rasa dalilin da ya sa yake neman dalilin da zai kai shi gidan su Sultana, ya na so ya sanya ta a idanun shi, zuciyar shi na azalzalar shi ta na tunzira shi akan ya je ya gan ta, daya bangaren na zuciyar shi na kwabar shi, bai biye wa daya daga cikin su ba, ko da ya fita ya dauki hanya, bai tsaya a ko ina ba sai gidan su.
Ko gaishe su bai ba, ya tsaya a tsaye ya ciro kudi masu uban yawa daga aljifan jikin shi, ya ajiye wa Lamishi, ya ce gashi nan su samu inda za a musu ɗinkin gaggawa in sun sai tufafin da suke so su sa a bikin, ba ya so su je masa wajen biki a hargitse.
Godiya suka dinga yi kamar za su kwanta, makullin mota ya bawa Jameelu, ya ce ya dakko wasu manyan ledoji a bayan motar, a guje ya fita ya na tsalle, ledoji ne manya masu nauyi Jameelu ya shiga da su, Dan Talo na ta bata rai ba a bashi komai ba.
Lawwali murmushin takaici ya yi, dan duk ya fahimci komai, tura leda daya gaban Dan Talo ya yi, ya ce,
"Sai ka bar bata fuska, ka sanya ranar daurin aure, kuma ka yi wanka dan Allah, kaya duk kyawun su in ba wanka ba sa kyau, Jameelu ga naku nan,ga wannan ku tai ku sai takalma da hulla, bana so ku taho wajen nan kamar almajirrai,"
"Tau Yaya mun gode"
"Kaiii wanga yaro Allah shi qaro bud'i" in ji Dan Talo.
"Addu'ar ku kenan,bud'i dai bud'i dai, to Allah shi bud'a din, ba bu ruwan ku da ta ina bud'in zai taho"
Fatali ya yi da dan karamin kwanon man gyadan da Mai Buruji ta soya, ya bar gidan, cikin takaicin iyayen nashi.
Ko da ya koma unguwar da yake zama, har zai wuce gidan shi, kawai ya tsaya, ya kira Sultana, ta na dauka ya ce,
"Ki shirya ki hito, zamu daukan hoto, ina jiran ki, nan da awa guda"
"Daukan hoto kuma? Na ko aza bai dame ka ba irin wannan abubuwan"
"Za mu yi ne dan Hajiya, ke san wadda taka son ayi komai a bayyane, hoton zai faranta ran ta"
Ta ji dadin yanda ya duba lamarin Hajiyar ta, da gaskiyar shi, hoton zai faranta ranta matuqa.
A gaggauce ta shiga wanka,ta fara shirya wa, dan bata so ta bar shi ya zauna jiran ta.
Shima gida ya wuce, ya samu ya watsa ruwa, ya yi shirin shi tsaf cikin farar shadda mai golden din aiki, ya na daga cikin dinkunan da suka siyo ready made shi da Sultana, a qalla sun siya kaya masu kyau da tsada kusan kala goma goma, a gogon shi na gold ya daura, kuma kalar aikin kayan shi (maza ku sani haramun ne namiji ya sanya agogo gold ko zoben gold sai azurfa).
Takalmin shi ma kalar aikin rigar shi, sai hula fara mai ratsin golden, Masha Allah, ko shi kan shi sai da ya jima gaban madubi ya na kallon kan shi, a fili ya bayyana cewa,
"Lawwali kenan, dan gidan Lamishi da Dan Talo, Yayan Mubaraka, Angon Sultana"
(Aunty Asma'u😆)
Murmushi ya yi, ya dauki turarukan shi ya dinga fesawa a hankali, ta yanda qamshin su ba zai hau kai ba, ya na gamawa ya taje gemun shi da ke qarawa fuskar shi kyau da kwarjini, (Team Gemu🥰)
Sai da ya rufe gidan sannan ya shige motar shi da ya bari a waje.
Ya na zuwa qofar gidan su Sultana Kiran ta na shiga wayar shi, dauka ya yi, ya ce ta fito ya na waje.
Ya na nan zaune a mota ya ga securies guda uku sun bude mata qofar, kamar hadin baki ta fito sanye da doguwar riga golden color, ta na ta walkiya a cikin duhun daren, Lawwali sakin baki ya yi ya na kallon Sultana, anyaa ita ce kuwa?
Sultana ta ji dad'in yanda Lawwali ya shagala da kallon ta, sai yanzu ta ke godewa Hajiya da ta dage sai an kawo wadda zata shirya ta, dan kuwa in ita zata shirya ba zata fito a matsayin amarya ba, dunkunan da a ka kashe makudan kudi aka yi su, a banza za a sanya su ba su yi kyawun da ake so ba.
Da sauri ya fita ya bude mata qofa, ta shiga, ta na murmushi qasa qasa.
Bayan ya zauna kafin ya tada motar,suka kalli juna, a tare suka furta,
"Ka/kin yi kyau"
Dariya suka yi, sannan Lawwali ya tada mota, sai hadadden gidan Hoton da ke cikin garin na Gusau, tun da suka shiga wajen mutane ke kallon su, domin kusan duk amaren da angwayen da suka je wajen dan d'aukan hoto Lawwali da Sultana sun fi su yin shiga mai kyau, da tsari, da burgewa.
Sai da aka gama wa mutum uku, sannan aka zo kan su, a lokacin qarfe goma na dare ta gota.
Style kala kala aka dinga nuna musu su kuwa su na kyafewa ana daukan su hoto, style din da suka ga ya sabawa shari'a in ance su yi, sai Sultana ko Lawwali d'aya daga cikin su yaqi.
A haka dai aka gama daukan su hotunan, wasu matasa ne suka gane Sultana, habaa manaa nan da nan waje ya cika da surutai kala kala, wasu na yabon ta, su na ta so a dauke su hoto da ita, wasu kuma na tsangwamar ta saboda mahaifin ta.
Lawwali bai tsaya biye wa shiririta ba, ya ja ta suka tafi gida.
Hajiya ta rude ta rikice da ta ga hotuna, ga su an tura musu ga waya, ga wasu sun taho da su a envelope,kallon Lawwali ta dinga yi daga sama har qasa, ko ba shi da arziki ya na da kyauwun huce takaici.
A cikin daren ta dinga dora hotunan a social media, qawayen ta kawai take jira su ga wannan hotunan, ta ga reaction din su akan mijin Sultanan ta.
Sultana ma ta dora hotunan a social media, musamman Instagram ,ganin yanda suka rude da kallon hotuna kamar basu da lokacin shi ne ya sanya Lawwali yin sallama da Sultan ya tafi gida.
Kayan shi ya cire ya tafi daji, domin ya na da mahimmin abu da ya ke so ya gudanar a can.................
*Biki bidiri buredeee*
💅🏻 *A GARIN MU* 💅🏻
BY HAERMEEBRAERH
PAGE 42:
Tokare take jikin gini, kamar wadda aka jingine, ta na ta dariyar yaqe, hannun ta dauke da kwano, shinkafa ce a ciki, ta sha ganyen zogale da quli, tumatur da albasa, da soyayyan mai, abincin da Lamishi ke matuqar so kenan.
"Ko ni mutan gidan ga ba su amsa sallama ne? Sai buga sallama nake tun garka shiru ka ke ji"
Lamishi ce ta fito, sanye da kayan da ta ke gwada wa, in da kudin ka yanzu za ka samu abinda ka ke nema, har sun samu ɗinkin da suka kai, guda bibbiyu, manyan leshi guda biyu atampa manya biyu, kowa d'aid'ai, sun siyo takalma da jakunkuna, sarqoqi da abun hannu, sai sabbin mayafai .
Lamishi ce ta yatsina baki ta ce,
"To wa ya ji ki mu na can mu na harikar azziqi"
"Ai fa, na ga harikar azziqi, mutumi na zai yi aure shi na ko a fad'i min, duk abin da ya faru a baya ai ke san sabanin harshe da haqori ne, to Allah shi sanya alkhairi, ni zan koma, ga gwaben shinkahwa na kawo miki, na san ki na so"
Wangale baki Lamishi ta yi, ta amshe kwano, ta gauraya gaban ta ta afa a baki, dad'in abun ne ya soki kunnen ta sai da ta sosa.
'Yabbuga na ganin haka ta saki jiki ta na zuba, ta ce wannan ta ce wancan, nan dai Lamishi ta manta da komai, suka hau hira akai ta bawa 'Yabbuga labarin abun azziqin da ke ta gudana a gidan.
"To ni dai ba wannan ba, ke dai ga bikin ga da ya taho a qurarren lokaci, ko tuwahi sabo ban dunka ba, dama ya kai wata guda ne, da na sa Dan Jumma ya sai min Holan ko Suhwa, nima na daura ana bikin Babban d'a"
Dariya suka sanya sukai shewa, tare da tafawa,
"Kar ki damu, ina nan da wata da Hajiya Ikeelima tabban, ke san su irin wannan ba shi gaban su, sai su sa sutura su ɗebe su basuwa kyauta, anjima in sun gane ta ba su ganewa "
'Yabbuga guda ta kama hanci ta zabga, ji take kamar ta jawo goben a d'aura auren,